ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bude Kofa Da Hadin Gwiwa Da Juna Kalmomi Ne Mafi Dadi

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Kofa

A watanni uku na farkon bana, yadda kasar Sin ta fitar da Deepseek, samfurin kirkirarriyar basira ta AI, da ma fim din da aka yi shi da kagaggun hotuna mai suna “Ne Zha 2”, ya yi matukar jawo hankalin kasashen duniya, wadanda kuma suka shaida yadda kasar Sin ke tabbatar da bunkasa mai inganci, da ma yadda kasar ke kara kwarewarta ta fannin kirkire-kirkire. 

Sai dai ba Deepseek da Ne Zha 2 su kadai ba ne, kasar Sin na tabbatar da ci gaba da kirkire-kirkire a fannoni daban daban, kuma hakan ya faru ne sakamakon yadda kasar ta shafe shekaru gommai tana ta bude kofarta ga kasashen ketare.

  • Mastalar Tsaro: Jihohi Sun Kashe Naira Biliyan 214 Wajen Sayen Makamai
  • Koch Usman Abdullahi Zai Jagoranci Kano Pillars A Karon Farko Bayan Dakatarwa

A ganin kasar Sin, ya zama dole a bude kofa ga kasashen ketare don samun tabbatuwar ci gaban kasa. Haka kuma saboda yadda kasar Sin ke ta hadin gwiwa da kasashen duniya da kuma koyi daga wajensu, kasar ta tabbatar da ci gaban tattalin arzikinta da kuma kirkire-kirkire. A sa’i daya kuma, kasar Sin ta yi ta raba damammaki da ma nasarorinta da kasashen duniya. Akasin haka, wasu kasashe sun yi ta katse huldar tattalin arziki tare da kafa shingaye ga sauran kasashe, a yunkurin kiyaye fifikon da suke da shi a wasu fannoni,wadanda kuma suka yi ta kakaba wa sauran kasashe karin harajin kwastam, don neman farfado da tattalin arzikinsu.

ADVERTISEMENT

Sai dai ko kwalliya za ta biya kudin sabulu?

Mu dauki harajin fito a matsayin misali, wanda shugaba Donald Trump na Amurka ke kallonsa a matsayin kalma mafi dadi a cikin kamus, wanda hakan ya sa sabuwar gwamnatin Amurka ta yi ta daukar kwararan matakan haraji, har ma a kwanakin baya, ta sanar da sanya haraji na ramuwar gayya a kan kasashen da ke cinikayya da ita. A ganin gwamnatin Amurka, hakan zai taimaka wajen kare masana’antu na cikin kasar tare da samar da karin guraben aikin yi. Sai dai ko za ta cimma burinta? A hakika, sanya haraji a kan kayayyakin da take shigowa da su daga sauran kasashe, zai haifar da karuwar kudaden da kamfanonin cikin gidan kasar suke kashewa, sakamakon haka, wasu kamfanoni ba yadda za su yi sai dai su sallami wasu ma’aikatansu. Ban da haka, ta la’akari da tsadar kudin da ake biyan ma’aikatan cikin kasar da ma rashin cikakken tsarin masana’antun samar da kayayyaki a kasar, da wuya Amurka ta cimma burinta na tilasta wa kamfanonin kasashen waje su kafa masana’antu a kasar. Kwanan nan, jami’an kungiyar tarayyar Turai sun yi gargadin cewa, matakin kakaba haraji na ramuwar gayya da Amurka ta dauka ka iya haddasa raguwar ma’aunin tattalin arziki na GDP da kaso 7% a fadin duniya. Sai kuma a hasashen da cibiyar nazari ta jami’ar Yale ta kasar Amurka ta yi, idan kasashen duniya sun dauki matakan ramuwar gayya, biyowa bayan harajin da Amurka ta sanya musu, lallai ma’aunin GDP din kasar Amurka zai ragu da kaso 1%. A zahiri dai, a zamanin da muke ciki na samun dunkulewar tattalin arzikin duniya, kariyar cinikayya ba za ta haifar da da mai ido ba, maimakon hakan, hasarori ne kawai za ta haddasa ga kowa, ciki har da wanda ya dauki matakin.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Har ila yau a kan batun haraji, a karshen bara, kasar Sin ta cire harajin kwastan a kan dukkanin kayayyakin da take shigowa da su daga kasashen da suka fi fama da koma bayan tattalin arziki, wadanda suka kulla huldar diplomasiyya da ita, ciki har da wasu kasashe 33 dake nahiyar Afirka, matakin da a hannu guda ya saukaka hanyoyin shigowar amfanin gona na kasashen Afirka cikin kasuwar kasar Sin don biyan bukatun gidanta, a dayan hannu kuma, ya taimaka ga saukaka fatara da ma bunkasuwar sana’o’i a kasashen Afirka. Wato ke nan, Sin da kasashen Afirka sun tabbatar da cin moriyar juna da samun nasara tare ta hanyar bude kofa da ma hada gwiwa da juna.

Lallai kashe fitilun wasu ba zai taimaka ga samar da haske ga wasu ba. A zamanin dunkeluwar tattalin arzikin duniya, tuni kasa da kasa sun zamanto masu matukar alaka da juna a tattalin arzikinsu, kuma ko kadan ba zai yiwu ba su katse huldar tattalin arziki da juna.

Ba shakka, bude kofa da hadin gwiwa da juna kalmomi ne mafi dadi, wanda a baya an shaida hakan, kuma zai ci gaba da tabbata a gaba. (Lubabatu Lei)

 

 

 

 

Kofa
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Kofa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Kofin Duniya: Kocin Nijeriya Na Fatan Matashin Ɗan Wasan Arsenal Nwaneri Ya Wakilci Ƙasar

Kofin Duniya: Kocin Nijeriya Na Fatan Matashin Ɗan Wasan Arsenal Nwaneri Ya Wakilci Ƙasar

LABARAI MASU NASABA

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

June 5, 2026
Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 5, 2026
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.