Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Masu Garkuwa Biyu Sun Shiga Komar Mafarauta A Jihar Kogi

by Muhammad
November 30, 2020
in LABARAI
2 min read
Mafarauta
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Ahmed Muhammed Danasabe

 

samndaads

Kungiyar Mafarauta ta Najeriya reshen Jihar Kogi (KGHGN) ta kama wasu wadanda a ke zargi da satar jama’a tare da yin garkuwa da su guda biyu, wadanda su ke tare jama’a a kan babban hanyar Lokoja zuwa Okene a safiyar Alhamis da ta gabata.

Kwamandan kungiyar Mafarautan na jihar, Bature Inusa, ne ya jagoranci mafarautan zuwa maboyar masu garkuwa da mutanen biyo bayan samun bayanan sirri da kungiyar ta yi.

Bayan sun yi ma sa tambayoyi ne sai ya amsa da bakinsa cewa shi ke bai wa masu garkuwa da mutanen bayanan yadda za su gudanar da ta’asarsu ta garkuwa da mutane.

Bayan samun bayanan sirri ne, sai Kwamanda Inusa ya jagoranci mafarautan har maboyar masu garkuwa da mutanen, inda su ka samu nasarar kama wani mai suna Suleiman Naru.

Kwamandan ya ce, “a yayin da mu ka yi wa wanda mu ke zargin tambayoyi, ya shaida ma na cewa, dukkansu na zaune ne a Kabba Junction kuma sun yi garkuwa da wata mata, inda su ka karbi kudin fansa Naira miliyan biyar daga ’yan uwanta kafin su sake ta.”

Ya kuma shaida ma na cewa, “shugabansu ya ba shi Naira 120,000, inda ya ce zai yi amfani da sauran kudaden wajen sayo makamai a Kaduna.”

Kwamanda Inusa har ila yau ya ce, masu garkuwa da mutanen su tara ne kuma sun yi garkuwa da mutane uku, ciki har da mai dakin tsohon shugaban karamar hukumar Okene. Kazalika, ya tabbatar da kama mutun guda cikin masu garkuwa da mutanen da kuma mai taimaka musu da bayanai.

Kwamandan kungiyar mafarautan wanda yace nan bada dadewa ba za a mika su ga yan sanda,ya kuma ce mafarautan suna nan suna bin sawun sauran masu garkuwa da jama’ar don damke su, inda yace da yardan Allah sai sun kama su.

Daga nan Inusa ya roki gwamnatin jihar Kogi data samar wa kungiyar mafarautan kayayakin aiki irinsu motocin hawa da ofis ofis da na’urorin sadarwa da kuma dan abin kashewa ga mambobin kungiyar domin kara musu kwarin gwiwar gudanar da ayyukansu.

Cikin abubuwan da aka gano daga masu garkuwa da jama’ar sun hada da bindiga  kirar AK 47 kirar cikin gida guda daya da kananan bindigogi kirar pistol guda uku da albarusai da kuma kullin ganye da ake zargin tabar wiwi ne.

A yayin hada wannan rehotu, wakilimmu bai kai ga jin ta bakin mai magana da yawun rundunar yan sandar jihar Kogi, DSP Williams Ayah, a hukumance ba.

SendShareTweetShare
Previous Post

Kowa Na Jin Zafin Kisan Manoman Zabarmari – Buhari

Next Post

Yadda Boko Haram Ta Yi Wa Manoma Da Masunta 110 Kisan Gilla A Zabarmari

RelatedPosts

Man Fetur

Kudirin Dokar Man Fetur Zai Bai Wa Nijeriya Damar Cin Gajiyar Albarkatunsa – Majalisar Dattawa

by Muhammad
3 hours ago
0

Daga Muhammad Maitela, Shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmad Ibrahim Lawan...

Jobe

Ma’aikata Da ’Yan Fansho Ke Wawashe Rabin Kudin Katsina, Cewar Kwamishina Jobe

by Muhammad
3 hours ago
0

Daga Sagir Abubukar, Kwamishinan Kasafin Kudi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki...

Rasuwar

Ana Cigaba Da Jimamin Rasuwar Mai Shari’ a Rabiu Danlami A Kano

by Muhammad
3 hours ago
0

Daga Haruna Akarada, Ana cigaba da gudanar da ta’aziyya ta...

Next Post
Alhakin

Yadda Boko Haram Ta Yi Wa Manoma Da Masunta 110 Kisan Gilla A Zabarmari

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version