• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Jiran A Zartar Musu Da Hukuncin Kisa Na Karuwa A Nijeriya

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
Masu Jiran A Zartar Musu Da Hukuncin Kisa Na Karuwa A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daurarru fiye da 3200 ne a gidajen yarin Nijeriya ke jiran a zartar musu hukuncin kisa, kamar yadda hukumar kula da gidajen gyaran hali ta Nijeriya ta bayyana.

Kamfanin dillancin labarai na Nijeriya NAN ya ambato mai magana da yawun hukumar Abubakar Umar yana cewa ba ko yaushe, ake zartar da hukuncin kisa nan take da zarar kotu ta yanke hukunci ba.

  • Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
  • Nijeriya Ta Sanya Hannu A Yarjejeniyar Amfani Da Fasahar Shuka Itatuwa Da Kasar Netherlands

Ya ce sau da yawa, fursunonin da aka yanke wa hukuncin kisa kan shafe tsawon lokaci a halin rashin tabbas, daidai lokacin da ake daukaka kararraki.

A watan Yulin bara, jaridar Punch ta ambato hukumar kula da gidajen yarin Nijeriya na cewa adadin wadanda ke zaman jiran a zartar musu da hukuncin kisa ya kai 3,145.

Hakan dai na nufin a cikin wata tara kawai, mutum 153 kotuna suka sake yanke wa hukuncin kisa a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Wani rahoton Amnesty International na 2021, ya sanya Nijeriya a matsayin ta uku a duniya cikin jerin kasashen masu yawan daurarru da ke jiran a kashe su.

Mai magana da yawun hukumar gidajen yarin Nijeriya ya ce “Daurarrun da ke zaman jiran kisa na rayuwa ne a bangarensu daban, yayin da wasu kan kwashe fiye da shekara 15 suna jiran a zartar musu da hukunci, bayan kotu ta yanke shari’a.

A cewarsa mutum 3,298 ne suke jiran hauni ya aiwatar da hukuncin da aka yanke musu bayan kotuna sun same su da laifi.

Ya kuma ce adadin masu jiran a zartar musu da hukuncin kisan ya kai kashi 4.5 na illahirin daurarrun da ke tsare a kasar.

Abubakar Umar ya kara da cewa ana daure da wasu masu zaman jiran a zartar musu hukuncin kisa tun lokacin da aka kama su, har zuwa lokacin da ake yi musu shari’a, kafin a yanke musu hukunci.

Ya ce da yawan mutanen sun aikata laifuka ne kamar kisan kai da fashi da ta’addanci da sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hukuncin KisaKaruwaNijeriyta
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ra’ayoyinku A Kan Dambarwar Siyasar Jihar Adamawa

Next Post

Manchester City Za Ta Fadada Filin Wasanta

Related

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

38 minutes ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

1 hour ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

5 hours ago
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai
Labarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

5 hours ago
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89
Labarai

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

5 hours ago
Next Post
Manchester City Za Ta Fadada Filin Wasanta

Manchester City Za Ta Fadada Filin Wasanta

LABARAI MASU NASABA

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.