ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

by Yusuf Shuaibu and Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
Ganduje

A daidai lokacin da wa’adin mulkin gwamnan Jihar Kano mai barin gado, Abdullahi Ganduje ke karewa, ya roki gafarar wadanda ya saba musu a yayin gudanar da mulkinsa na tsawon shekaru takwas a Jihar Kano.

Sai dai kuma a wani martani da ya mayar kan yafiyar Gwamna Ganduje mai barin gado, tsohon kwamishinan ayyuka da ababen more rayuwa, Muaz Magaji ya ce “Eh na yafe maka, amma ba zan taba mantawa da yadda kuka kulla makarkashiyar kawar da ni daga doron kasa ba a lokuta da dama.”

  • Kwaliyyar Da Samari Da ‘Yanmata Suka Tsara Don Burgewa A Wannan Sallar
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kwaso Daliban Nijeriya Bayan Barkewar Rikici A Sudan

Ana sa ran Gwamna Ganduje zai kammala wa’adinsa na biyu na shekaru takwas nan da watan gobe tare da mika ragamar mulkin Jihar Kano ga zababben gwamna, Abba Kabir Yusuf.

ADVERTISEMENT

Da yake karin haske daga kalamansa, Ganduje ya ce “Na yafe wa duk wanda yayi min laifi ko ya wulakanta ni, domin haka, ina neman gafara ga duk wanda na yi wa ba daidai ba”.

A cewarsa, ya yi hakan ne bisa karantarwar addinin Musulunci, inda ya kara da cewa afuwa na da matukar muhimmanci a cikin koyarwar addinin Musulunci.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

“Aikina na gwamnan Jihar Kano ya zo karshe, kuma wannan gaisuwa ce ta bankwana. Ina muku fatan alheri. Ga wadanda muka bata wa rai, ina rakonsu su gafarta mana, a nawa bangaren na yafe wa wadanda suka zalunce ni komai girman laifin. “

Bayan ya kammala jawabi, “Tsohon kwamishinan ayyuka da ababen more rayuwa na Ganduje, Mu’az Magaji, wanda ya halarci taron ya tashi ya ce, “Eh, na yafe maka, amma ba zan manta da yadda kuka kulla makircin kawar da ni daga doron kasa ba a lokuta da dama”.

Sai dai Magaji a cikin shafinsa na Facebook ya ambaci wurare uku da ya tsallake rijiya da baya da ake zargin tsohon ubangidansa ne ya shirya masa gadar zare.

Ra’ayoyin Kanawa Kan Neman Gafarar Gwamna Ganduje

Ganduje Bai Cika Sharadan Tuba Ba, Saboda Haka Ba Da Gaske Yake Yi Ba – Musa Falaki

Sheikh Musa Falaki yana daga cikin masu yawan kallon yadda abubuwan gwamnati ke tafiya ta fuskar shari’a. Kan bautun neman gafarar Ganduje, Falaki ya bayyana cewa Ganduje bai cika sharadan tuba ba, domin kuwa cikin sharadan tuba na farko ma shi ne, yin nadama kan abubuwan da suka wakana, saboda haka rashin wannan nadama ya sa Kanawa ke kallon wannan neman gafara a matsayin wasa da hankali, musamman kasancewar neman gafara abu biyu ne, ko dai neman gafara kan abin da ka aikata wa Allah tsakaninka da shi, sannan akwai kuma abin da mutum ya yi wa ‘yan’uwansa mutane, wannan hakki sai dai a biya masu hakkinsu kafin a nemi gafararsu, idan sun ga dama su yafe maka.

Tuban Gwamna Ganduje Ya Zo A Lokacin Da Ba Za A Karbar Ba – Ata

Tsohon shugaban Kasuwar Kantin Kwari Sanusi Umar Ata, da yake tsokaci kan neman gafarar da Gwamna Ganduje ya nema daga Kanawa, ya bayyana cewa gaskiya magana idan aka dubi ayar Alkur’ani da ke cewa, “Babu tuba ga wanda ya zo gargarar mutuwa,” wannan tuba da Ganduje ke nema bai wuce ganin damar da Allah ya ba shi ta zo karshe ba, don haka dole ya nemi wannan gafara.

Ya ci gaba da cewa duk cikin wadanda Allah ya bai wa damar mulkar Jihar Kano babu wanda ya fi Ganduje samun dama, amma bai amfani da damar wajen tausasa wa jama’a ba. Misali, ya yi taro da ‘yan a caba yake fada masu cewar tsiyar Nasara sai za shi gida, yanzun ya kama hanyar tafiya gidan kenan? Haka kuma an ji shi a wani taro yana cewa zai hau dutsen Goron Dutse ya tsinke birki ya gangaro da gudu, kenan zai murkushe kowa?  Haka kuma ya ce zai dau manjagara ya sosa bayansa da shi, kenan akwai tanadin keta a zuciyarsa.

“Saboda haka mu aganinmu, wannan kawai bai wuce gargarar kubucewar mulki ba, muna ganin batun neman gafarar talakawan Kano lokaci ya kure masa,” in ji Ata.

Neman Gafarar Ganduje Rufo Kura Da Bargon Akuya Ne Kawai – Kwamared Ishak

Wani mai fashin bakin a kan harkokin siyasar Jihar Kano, Kwamared Ishak Gandun Albasa ya bayyana neman gafarar da Ganduje ya yi da cewa wayon rufo kura da bargon akuya ne kawai.

A cewarsa, ba zai yiwu shugaban da ya riki jagorancin al’umma na tsawon shekaru takwas ya fito ya ce yana neman jama’ar jihar su yafe masa abin da ya yi masu ba. idan a matsayinsa na Dan’adam ne yake neman wannan gafara kan abin da ya aikata da kuskure, wannan wata magana ce daban, amma idan ya san yana neman gafara ne kan ta’asar da ya yi wa jama’ar Kano, wannan kuma hakki ne da ya kama ya dawo masu da kayansu, sai a wuce wurin.

“Kasancewar Dan’adam mai kuskure ne, hakan ba yana nufin ka ci dukiyar al’umma ko ka yi wasarai-rai da dukiyarsu ka buda baki su ka ce su yafe maka. Abin da ya kamata shi ne, idan hakkinsu ka cinye ko ka bayar da dama aka ciniye, sai da dawo masu da wannan hakkin, idan kuma wani kuskure ne ya yi wanda kowani Dan’adam na iya yin irin wannan kuskuren, wannan ba laifi idan ya nemi gafara, amma ban da abin da aka yi wa jama’a da ganganci,” in ji Kwamared Ishak.

Neman Gafarar Ganduje Ya Nuna Cikar Dattijantakarsa – Amb. Dandago

Amb. Mansur Haruna Dandago, dan Kasuwa kuma dan siyasa ya bayyana cewa neman gafarar da Gwamna Ganduje ya yi shi ne abin da ya kamata ga duk wani dattijon arziki, kuma wannan ke tabbatar da sunansa na Khadimul Islam, ganin yadda Allah ya ba shi damar jagorantar Kanawa tsawon shekara takwas, ya gode wa Allah bisa wannan bai wa, sannan kuma ya nemi gafarar wadanda ya sabawa, shi kuma a kashin kansa ya tabbatar da yafe wa kowa.

“Babu shakka mun yafe masa, kuma Allah ya yafe mana baki daya.

“Gwamna Ganduje shi ne mutun na farko daga cikin wadanda suka jagoranci Kanawa a matsayin gwamna wanda ya nuna wannan dattijantaka na neman gafarar wadanda ya mulka. Shi ma Marigayi Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Ado Bayero shi ma a lokacin da ya cika shekara 50 a kan karagar mulki ya nemi gafarar al’ummar Jihar Kano, don haka wannan kyakkyawna misali ne ga duk mai neman haduwa da Allah lami lafiya,” in ji Amb. Dandago.

Ganduje
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
Ganduje
Abdullahi Muh'd Sheka
+ posts Bio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Bayan Biyan Kudin Fansa, Kasurgumin Dan Bindiga Ya Saki Daliba 4 Na Kwalejin Yauri

Bayan Biyan Kudin Fansa, Kasurgumin Dan Bindiga Ya Saki Daliba 4 Na Kwalejin Yauri

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.