ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

by Yusuf Shuaibu and Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
Ganduje

A daidai lokacin da wa’adin mulkin gwamnan Jihar Kano mai barin gado, Abdullahi Ganduje ke karewa, ya roki gafarar wadanda ya saba musu a yayin gudanar da mulkinsa na tsawon shekaru takwas a Jihar Kano.

Sai dai kuma a wani martani da ya mayar kan yafiyar Gwamna Ganduje mai barin gado, tsohon kwamishinan ayyuka da ababen more rayuwa, Muaz Magaji ya ce “Eh na yafe maka, amma ba zan taba mantawa da yadda kuka kulla makarkashiyar kawar da ni daga doron kasa ba a lokuta da dama.”

  • Kwaliyyar Da Samari Da ‘Yanmata Suka Tsara Don Burgewa A Wannan Sallar
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kwaso Daliban Nijeriya Bayan Barkewar Rikici A Sudan

Ana sa ran Gwamna Ganduje zai kammala wa’adinsa na biyu na shekaru takwas nan da watan gobe tare da mika ragamar mulkin Jihar Kano ga zababben gwamna, Abba Kabir Yusuf.

ADVERTISEMENT

Da yake karin haske daga kalamansa, Ganduje ya ce “Na yafe wa duk wanda yayi min laifi ko ya wulakanta ni, domin haka, ina neman gafara ga duk wanda na yi wa ba daidai ba”.

A cewarsa, ya yi hakan ne bisa karantarwar addinin Musulunci, inda ya kara da cewa afuwa na da matukar muhimmanci a cikin koyarwar addinin Musulunci.

LABARAI MASU NASABA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

“Aikina na gwamnan Jihar Kano ya zo karshe, kuma wannan gaisuwa ce ta bankwana. Ina muku fatan alheri. Ga wadanda muka bata wa rai, ina rakonsu su gafarta mana, a nawa bangaren na yafe wa wadanda suka zalunce ni komai girman laifin. “

Bayan ya kammala jawabi, “Tsohon kwamishinan ayyuka da ababen more rayuwa na Ganduje, Mu’az Magaji, wanda ya halarci taron ya tashi ya ce, “Eh, na yafe maka, amma ba zan manta da yadda kuka kulla makircin kawar da ni daga doron kasa ba a lokuta da dama”.

Sai dai Magaji a cikin shafinsa na Facebook ya ambaci wurare uku da ya tsallake rijiya da baya da ake zargin tsohon ubangidansa ne ya shirya masa gadar zare.

Ra’ayoyin Kanawa Kan Neman Gafarar Gwamna Ganduje

Ganduje Bai Cika Sharadan Tuba Ba, Saboda Haka Ba Da Gaske Yake Yi Ba – Musa Falaki

Sheikh Musa Falaki yana daga cikin masu yawan kallon yadda abubuwan gwamnati ke tafiya ta fuskar shari’a. Kan bautun neman gafarar Ganduje, Falaki ya bayyana cewa Ganduje bai cika sharadan tuba ba, domin kuwa cikin sharadan tuba na farko ma shi ne, yin nadama kan abubuwan da suka wakana, saboda haka rashin wannan nadama ya sa Kanawa ke kallon wannan neman gafara a matsayin wasa da hankali, musamman kasancewar neman gafara abu biyu ne, ko dai neman gafara kan abin da ka aikata wa Allah tsakaninka da shi, sannan akwai kuma abin da mutum ya yi wa ‘yan’uwansa mutane, wannan hakki sai dai a biya masu hakkinsu kafin a nemi gafararsu, idan sun ga dama su yafe maka.

Tuban Gwamna Ganduje Ya Zo A Lokacin Da Ba Za A Karbar Ba – Ata

Tsohon shugaban Kasuwar Kantin Kwari Sanusi Umar Ata, da yake tsokaci kan neman gafarar da Gwamna Ganduje ya nema daga Kanawa, ya bayyana cewa gaskiya magana idan aka dubi ayar Alkur’ani da ke cewa, “Babu tuba ga wanda ya zo gargarar mutuwa,” wannan tuba da Ganduje ke nema bai wuce ganin damar da Allah ya ba shi ta zo karshe ba, don haka dole ya nemi wannan gafara.

Ya ci gaba da cewa duk cikin wadanda Allah ya bai wa damar mulkar Jihar Kano babu wanda ya fi Ganduje samun dama, amma bai amfani da damar wajen tausasa wa jama’a ba. Misali, ya yi taro da ‘yan a caba yake fada masu cewar tsiyar Nasara sai za shi gida, yanzun ya kama hanyar tafiya gidan kenan? Haka kuma an ji shi a wani taro yana cewa zai hau dutsen Goron Dutse ya tsinke birki ya gangaro da gudu, kenan zai murkushe kowa?  Haka kuma ya ce zai dau manjagara ya sosa bayansa da shi, kenan akwai tanadin keta a zuciyarsa.

“Saboda haka mu aganinmu, wannan kawai bai wuce gargarar kubucewar mulki ba, muna ganin batun neman gafarar talakawan Kano lokaci ya kure masa,” in ji Ata.

Neman Gafarar Ganduje Rufo Kura Da Bargon Akuya Ne Kawai – Kwamared Ishak

Wani mai fashin bakin a kan harkokin siyasar Jihar Kano, Kwamared Ishak Gandun Albasa ya bayyana neman gafarar da Ganduje ya yi da cewa wayon rufo kura da bargon akuya ne kawai.

A cewarsa, ba zai yiwu shugaban da ya riki jagorancin al’umma na tsawon shekaru takwas ya fito ya ce yana neman jama’ar jihar su yafe masa abin da ya yi masu ba. idan a matsayinsa na Dan’adam ne yake neman wannan gafara kan abin da ya aikata da kuskure, wannan wata magana ce daban, amma idan ya san yana neman gafara ne kan ta’asar da ya yi wa jama’ar Kano, wannan kuma hakki ne da ya kama ya dawo masu da kayansu, sai a wuce wurin.

“Kasancewar Dan’adam mai kuskure ne, hakan ba yana nufin ka ci dukiyar al’umma ko ka yi wasarai-rai da dukiyarsu ka buda baki su ka ce su yafe maka. Abin da ya kamata shi ne, idan hakkinsu ka cinye ko ka bayar da dama aka ciniye, sai da dawo masu da wannan hakkin, idan kuma wani kuskure ne ya yi wanda kowani Dan’adam na iya yin irin wannan kuskuren, wannan ba laifi idan ya nemi gafara, amma ban da abin da aka yi wa jama’a da ganganci,” in ji Kwamared Ishak.

Neman Gafarar Ganduje Ya Nuna Cikar Dattijantakarsa – Amb. Dandago

Amb. Mansur Haruna Dandago, dan Kasuwa kuma dan siyasa ya bayyana cewa neman gafarar da Gwamna Ganduje ya yi shi ne abin da ya kamata ga duk wani dattijon arziki, kuma wannan ke tabbatar da sunansa na Khadimul Islam, ganin yadda Allah ya ba shi damar jagorantar Kanawa tsawon shekara takwas, ya gode wa Allah bisa wannan bai wa, sannan kuma ya nemi gafarar wadanda ya sabawa, shi kuma a kashin kansa ya tabbatar da yafe wa kowa.

“Babu shakka mun yafe masa, kuma Allah ya yafe mana baki daya.

“Gwamna Ganduje shi ne mutun na farko daga cikin wadanda suka jagoranci Kanawa a matsayin gwamna wanda ya nuna wannan dattijantaka na neman gafarar wadanda ya mulka. Shi ma Marigayi Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Ado Bayero shi ma a lokacin da ya cika shekara 50 a kan karagar mulki ya nemi gafarar al’ummar Jihar Kano, don haka wannan kyakkyawna misali ne ga duk mai neman haduwa da Allah lami lafiya,” in ji Amb. Dandago.

Ganduje
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa
Ganduje
Abdullahi Muh'd Sheka
+ posts Bio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato
Manyan Labarai

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Labarai

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Labarai

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Next Post
Bayan Biyan Kudin Fansa, Kasurgumin Dan Bindiga Ya Saki Daliba 4 Na Kwalejin Yauri

Bayan Biyan Kudin Fansa, Kasurgumin Dan Bindiga Ya Saki Daliba 4 Na Kwalejin Yauri

LABARAI MASU NASABA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.