• English
  • Business News
Wednesday, September 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

by Ibrahim Bala
2 months ago
in Ado Da Kwalliya
0
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Assalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.

Jama’a barkanku da kasancewa tare da wannan fili mai albarka na MARURUN ZUCIYA, shafin dake zakulo muku matsaloli da kuma hanyar da za a magance matsalar.

  • Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato
  • KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan ÆŠaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

A wannan lokacin zan dan yi tsokaci wato jan hankali, ko na ce dan fadakarwa, har ma da tunatarwa, musamman a kan matan da suke da aure, wadanda ba su jima ba.

Wani abun mamaki a kasar hausa ko na ce a Arewacin Najeriya wai bazawara ce take yawon yin tallan maganin mallakar miji to, saboda Allah mene ya sa ita ba ta mallake nata mijin ta zauna ba?

Mu kula, mu lura, mu kiyaye, su ma mazaje su rika jan kunnen  matansu a kan irin wadannan matan. Ko kuma za a yi miki kishiya wata ta dauko kafa ta zo wai tana da maganin da za ki mallake kishiya ko miji sai abin da ki ka ce, karshenta kuma bazawara ce.

Labarai Masu Nasaba

Gyaran Fuska Da Laushin Fata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Mafi akasarin matan da suke irin wannan tallace-tallacen magungunan zawarawa ne, shin ita ba ta yi amfani da maganin bane ta mallake mijinta ta kasa fita daga gidan miji?.

Mu kiyaye, kuma mu ji taoron Allah, ke da aka kawo wa tallan maganin ki sani babu wani magani da zai sa ki mallake mijinki, tamkar ladabi da biyayya, da bin umarnin Allah subhanahu wa ta’ala. Ki bi mijinki sau da kafa ki yi masa biyayya da ladabi, in ki ka bi Allah ki ka bi manzon Allah (s.a.w), ki ka kyautatawa mijinki ai kin mallake miji, me miji yake da bukata?, kar ki yarda wani ko wata ya kawo miki wani magani ya ce ki yi amfani da shi na mallake miji, ai kyakkyawan maganin mallakar miji ga ‘ya’ya mata shi ne; ni-na-yi-bari -na-bari, ayi biyayyar aure, kuma babu wata biyayya da Manzon Allah (s.a.w) bai fade ta a hadisi da za a bi ba a zauna da maza lafiya.

Kuma masu yaho suna sayar da magungunan kuna cewa maganin mallake miji ko a hana kishiya shigowa a ji tsoron Allah, ku sani idan mata ne ku kun girma kun haifa ‘ya’yanku za su yi aure a wani gidan, idan ma baku haifa ba to, ku sani kannenku ko ‘yan’uwanku za su yi aure a wani gidan, abin da ka je ka yi wa ‘yar wani ka hana ta zaman gidan miji to, kai ma tana nan kamar sako ne ka bayar.

Idan wata matsala ki ke ciki tsakaninki da mijinki ina mai baki shawara addu’a ita ce maganin komai, domin garkuwa ce kuma takobi ce ga mumini, ba wani abu da addu’a ba za ta yanka shi ba, babu wani abu da addu’a ba za ta kare ka da shi ba. 

Ki yi addu’a ki gayawa Allah (s.w), ki samu mijinki ke da shi ku yi magana da shi, ko shaidan ne mijinki idan ki ka kwantar da kai, ki ka yarda shi uba ne a gare ki, ki ka yi masa biyayya, ki ka yi masa ladabi, ki ka bi ta sanyin murya ki ka yi masa magana, in wani abu ne za ku sasanta tsakaninku, ba sai an tayaki da maganin mallakar miji ba.

Maganin mallakar miji har sai an baki labari?, ubangiji Allah ya zaunar da matan mu lafiya, da kannenmu da yayyenmu dukkaninsu Allah ya kara musu lafiya, wadanda ba su da miji ubangiji Allah ya mallaka musu, zawarawan ma da suke yaho suke irin wadanan barnace-barnacen son kai, da son zuciya da neman kudi, ubangiji Allah ya basu miji nagari kuma Allah ya shirye su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MaganiMata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rasuwar ÆŠantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Next Post

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Related

Gyaran fuska
Ado Da Kwalliya

Gyaran Fuska Da Laushin Fata

3 days ago
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata
Ado Da Kwalliya

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

1 week ago
Yadda Za A Magance Ciwon Sanyi (Infection) Da Tafarnuwa
Ado Da Kwalliya

Yadda Za A Magance Ciwon Sanyi (Infection) Da Tafarnuwa

2 weeks ago
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Ado Da Kwalliya

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

1 month ago
Hanyoyin Gyaran Gashi
Ado Da Kwalliya

Hanyoyin Gyaran Gashi

1 month ago
Amfanin Kabewa A Jikin Mace
Ado Da Kwalliya

Amfanin Kabewa A Jikin Mace

1 month ago
Next Post
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

LABARAI MASU NASABA

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

September 2, 2025
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

September 2, 2025
Gwamna Dauda Lawal A Shekara 60: Inda Akwai Fata, Akwai Mafita

Gwamna Dauda Lawal A Shekara 60: Inda Akwai Fata, Akwai Mafita

September 2, 2025
Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

September 2, 2025
Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka

Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka

September 2, 2025
Gwamna Yusuf

Gwamna Yusuf Zai Kaddamar Da Majalisar Shurah Ta Jihar Kano

September 2, 2025
Xi: Alakar Sin Da Rasha Ta Zama Misali Na Kyakkyawar Dangantakar Manyan Kasashe

Xi: Alakar Sin Da Rasha Ta Zama Misali Na Kyakkyawar Dangantakar Manyan Kasashe

September 2, 2025
Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

September 2, 2025
Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

September 2, 2025
Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya

Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya

September 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.