ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

by Ibrahim Bala
1 year ago
Mata

Assalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.

Jama’a barkanku da kasancewa tare da wannan fili mai albarka na MARURUN ZUCIYA, shafin dake zakulo muku matsaloli da kuma hanyar da za a magance matsalar.

  • Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato
  • KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

A wannan lokacin zan dan yi tsokaci wato jan hankali, ko na ce dan fadakarwa, har ma da tunatarwa, musamman a kan matan da suke da aure, wadanda ba su jima ba.

ADVERTISEMENT

Wani abun mamaki a kasar hausa ko na ce a Arewacin Najeriya wai bazawara ce take yawon yin tallan maganin mallakar miji to, saboda Allah mene ya sa ita ba ta mallake nata mijin ta zauna ba?

Mu kula, mu lura, mu kiyaye, su ma mazaje su rika jan kunnen  matansu a kan irin wadannan matan. Ko kuma za a yi miki kishiya wata ta dauko kafa ta zo wai tana da maganin da za ki mallake kishiya ko miji sai abin da ki ka ce, karshenta kuma bazawara ce.

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi

A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

Mafi akasarin matan da suke irin wannan tallace-tallacen magungunan zawarawa ne, shin ita ba ta yi amfani da maganin bane ta mallake mijinta ta kasa fita daga gidan miji?.

Mu kiyaye, kuma mu ji taoron Allah, ke da aka kawo wa tallan maganin ki sani babu wani magani da zai sa ki mallake mijinki, tamkar ladabi da biyayya, da bin umarnin Allah subhanahu wa ta’ala. Ki bi mijinki sau da kafa ki yi masa biyayya da ladabi, in ki ka bi Allah ki ka bi manzon Allah (s.a.w), ki ka kyautatawa mijinki ai kin mallake miji, me miji yake da bukata?, kar ki yarda wani ko wata ya kawo miki wani magani ya ce ki yi amfani da shi na mallake miji, ai kyakkyawan maganin mallakar miji ga ‘ya’ya mata shi ne; ni-na-yi-bari -na-bari, ayi biyayyar aure, kuma babu wata biyayya da Manzon Allah (s.a.w) bai fade ta a hadisi da za a bi ba a zauna da maza lafiya.

Kuma masu yaho suna sayar da magungunan kuna cewa maganin mallake miji ko a hana kishiya shigowa a ji tsoron Allah, ku sani idan mata ne ku kun girma kun haifa ‘ya’yanku za su yi aure a wani gidan, idan ma baku haifa ba to, ku sani kannenku ko ‘yan’uwanku za su yi aure a wani gidan, abin da ka je ka yi wa ‘yar wani ka hana ta zaman gidan miji to, kai ma tana nan kamar sako ne ka bayar.

Idan wata matsala ki ke ciki tsakaninki da mijinki ina mai baki shawara addu’a ita ce maganin komai, domin garkuwa ce kuma takobi ce ga mumini, ba wani abu da addu’a ba za ta yanka shi ba, babu wani abu da addu’a ba za ta kare ka da shi ba. 

Ki yi addu’a ki gayawa Allah (s.w), ki samu mijinki ke da shi ku yi magana da shi, ko shaidan ne mijinki idan ki ka kwantar da kai, ki ka yarda shi uba ne a gare ki, ki ka yi masa biyayya, ki ka yi masa ladabi, ki ka bi ta sanyin murya ki ka yi masa magana, in wani abu ne za ku sasanta tsakaninku, ba sai an tayaki da maganin mallakar miji ba.

Maganin mallakar miji har sai an baki labari?, ubangiji Allah ya zaunar da matan mu lafiya, da kannenmu da yayyenmu dukkaninsu Allah ya kara musu lafiya, wadanda ba su da miji ubangiji Allah ya mallaka musu, zawarawan ma da suke yaho suke irin wadanan barnace-barnacen son kai, da son zuciya da neman kudi, ubangiji Allah ya basu miji nagari kuma Allah ya shirye su.

Mata
Ibrahim Bala
+ postsBio
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Matsalar Ƙwacen Waya: Ina Mafita?
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

MASU ALAKA

Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi
Ado Da Kwalliya

Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi

June 14, 2026
A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa
Ado Da Kwalliya

A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

June 6, 2026
Ko Kin San… Cututtukan Da Man Ridi Ke Warkarwa?
Ado Da Kwalliya

Ko Kin San… Cututtukan Da Man Ridi Ke Warkarwa?

May 17, 2026
Next Post
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

LABARAI MASU NASABA

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

July 12, 2026
Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

July 12, 2026
Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

July 12, 2026
FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

July 12, 2026
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

July 12, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

July 12, 2026
Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

July 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.