Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Mata Sama Da Dubu Ke Aikin Ciyar Da Ɗalibai A Bauchi –Soro

by Tayo Adelaja
October 24, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muazu Hardawa, Bauchi

A ci gaba da gudanar da shirin gwamnatin tarayya na ciyar da ɗaliban makarantun firamare a Jihohi 14 na Nigeria, sama da mata dubu ɗaya ke gudanar da wannan aikin a Jihar Bauchi inda suke ciyar da ɗalibai sama da rabin milyan a makarantun firamaren cikin garin Bauchi da yankunan karkarar Jihar.

Me tallafawa gwamna kan wannan shiri, Alhaji Mansur Manu Soro shi ne ya ya bayyana haka cikin hirar sa da wakilinmu a Bauchi inda ya ƙara da cewa shirin ya samu nasara a tsawon kwanaki goma da aka gudanar da shi kafin hutun da ya gabata, a saboda haka yanzu aka sake ɗaukar Jihar bauchi aka bayar da kuɗin kwanaki 20 don wannan aiki, alhali wasu Jihohin na kwanaki goma aka basu, amma saboda yadda aka samu nasarar wannan aiki a baya da kuma kyawawan bayanai na yadda matan suka gudanar da wannan aiki, ya sa gwamnatin tarayya ta ƙara kima da yawan kwanakin da aka bayar da kuɗi don wannan aiki.

Mansur Manu Soro ya ƙara da cewa tun kafin a fara shirin gwamna ya bashi amanar tsara yadda shirin zai gudana a Bauchi kuma ya tsara ta yadda aka samu nasara, illa yan ƙorafe-ƙorafe da ba za a rasa ba wanda al’adace ta ɗan adam. Amma wannan shiri ya temaka sosai wajen ba yara abinci kyauta musamman ga ɗaliban ƙananan azuzuwa, kuma yanzu suna ƙoƙarin yadda za a faɗaɗa wannan shiri har zuwa kan sauran ɗalibai a kowace makaranta. Don haka ya buƙaci masu gudanar da wannan shiri su ci gaba da riƙe gaskiya don a samu nasara wajen faɗaɗa shirin.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Za mu Kamo Manchester City Da United

Next Post

Rikicin Gine Masallacin Idi A Kano: Ali Baba Ya Warware Zare Da Abawa

RelatedPosts

Abduljabbar

Abduljabbar Bai Kai Darajar A Yi Masa Gangami Ba –Sheikh Khalil

by Muhammad
20 hours ago
0

Ya Ce, Dalilin Da Ya Sa Sarkin Musulmi Ya Hana...

Tuhumar Malam Abduljabbar Za A Yi, Ba Mukabala Da Shi Ba– Sheikh Khalil

by Sulaiman Ibrahim
3 days ago
0

Daga Nasir S. Gwangwazo, Abuja Shugaban Majalisar Malamai na Shiyyar...

ISWAP

Boko Haram Ta Yi Garkuwa Da Ma’aikatan Jinkai Bakwai A Dikwa

by Sulaiman Ibrahim
3 days ago
0

Daga Muhammad Maitela, Maiduguri A harin bayan nan da mayakan...

Next Post

Rikicin Gine Masallacin Idi A Kano: Ali Baba Ya Warware Zare Da Abawa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version