• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mataimakin Shugaban Jami’ar Kwara, Akanbi, Ya Rasu Yana Da Shekaru 51

by Muhammad
3 years ago
Mataimakin

Mataimakin shugaban jami’ar jihar Kwara (KWASU), Farfesa Muhammed Mustapha Akanbi (SAN), ya rasu.

Akanbi mai shekaru 51, ya rasu ne a ranar Lahadin da ta gabata a wani asibiti da ke jihar Legas.

  • ‘Yan Bindigar Da Suka Yi Garkuwa Da Malami Da Dansa A Kwara, Sun Bukaci Fansar Miliyan 100
  • EFCC Ta Kama ‘Yan Damfara 18 A Jihar Kwara 

Hukumar jami’ar ta tabbatar da mutuwar Akanbi a wata sanarwa da magatakardar jami’ar, Dokta Kikelomo Sally, ya sanyawa hannu.

Kafin a nada shi a matsayin mataimakin shugaban KWASU shekaru biyu da suka wuce, Akanbi malamin shari’a ne a Jami’ar Ilorin (UNILORIN).

“Cikin alhini muna mika wuya ga Allah, Hukumar Gudanarwar Jami’ar Jihar Kwara ta sanar da rasuwar Mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa Muhammed Mustapha Akanbi (SAN).

LABARAI MASU NASABA

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bayyana rashin Akanbi a matsayin babban rashi mai raɗaɗi da kaduwa da mutuwar tasa.

“Mun mika wuya ga hukuncin Allah wanda yake bayarwa kuma yake karba. A kan wannan muke jimamin rasuwar mataimakin shugaban jami’ar da ya amsa kiran Allah a daren yau. Bawan Allah ne na gaskiya kuma mai kaskantar da kai, muna rokon Allah Madaukakin Sarki da Ya ba shi Aljannar Firdausi.

“Farfesa a fannin shari’a kwararre ne wanda ya taka rawa wajen bude wani sabon babi na daukaka KWASU. Muna mika ta’aziyyarmu ga iyalansa, kai tsaye zuwa ga KWASU da sauran malamai, da ’yan jihar Kwara da ma fadin kasar nan,” in ji gwamnan a wata sanarwa da babban mai yada labaransa ya sanya wa hannu, Rafiu Ajakaye.

A cikin sakon ta’aziyyar Sarkin Ilorin, Alh Ibrahim Sulu-Gambari, ya bayyana alhininsa game da rasuwar Akanbi.

Sulu-Gambari ya bayyana lamarin a matsayin abin ban tsoro, abin bantsoro da damuwa, yana mai jaddada cewa mutuwar Akanbi babban rashi ne ga al’ummar Masarautar Ilorin, Kwara da kuma Jama’a baki daya.

Sakon ta’aziyyar Sarkin na dauke da sa hannun mai magana da yawunsa, Malam Abdulazeez Arowona, ya ce: “Shi (Akanbi) ya kasance kwafin mahaifinsa kuma tsohon shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa mai zaman kanta (ICPC), Marigayi Mai shari’a Mustapha Akanbi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Kwamitin Shura Na Kano Ya Dakatar Da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamitin Shura Na Kano Ya Dakatar Da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

October 1, 2025
Next Post
Wike Ya Karbi Bakoncin Kwankwaso Don Kaddamar Da Bude Wasu Aiyuka A Jihar Ribas

Wike Ya Karbi Bakoncin Kwankwaso Don Kaddamar Da Bude Wasu Aiyuka A Jihar Ribas

LABARAI MASU NASABA

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

October 21, 2025
An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

October 21, 2025
Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

October 21, 2025
NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

October 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Ɗan Fashi Sanye Da Kayan NYSC A Enugu

October 21, 2025
Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.