• English
  • Business News
Thursday, May 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matakai Bakwai Da Kasashe Ke Dauka Don Rage Matsalar Makamashi

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Matakai Bakwai Da Kasashe Ke Dauka Don Rage Matsalar Makamashi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasar Jamus ta sanar da matakan da take dauka domin rage makamashin da ake amfani da shi bayan fari da tsananin zafi da annobar Korona da kuma fadan Ukraine sun haifar da matsalar makamashi a duniya.

Sai dai karuwar matsalar makamashi ta taba ko’ina a duniya, inda Jamus ba ita ce kasa kadai da ta bullo da matakai domin tinkarar hakan.

  • Muna Zargin Masallatai Da Coci-coci Da Hannu A Satar Mai –Kyari
  • Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Keta Ka’idojin Fitar Da Kayayyaki

 Ga wasu hanyoyi bakwai da gwamnatoci suke dauka domin dakile matsalar ta makamashi. Nahiyar Turai na fuskantar matsalar makamashi da ba ta taba gani ba, bayan da Rasha da rage yawan gas din da take fitarwa ta bututun Nord Stream 1.

Hakan ne ya sa dakile matsalar matsalar makamashi ta zamo babban abu da gwamnatoci a Turai din suka sa gaba.

Rage abubuwa masu zafi da kuma na’urar bayar da sanyi

Labarai Masu Nasaba

Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

Hajji: NAHCON Ta Kammala Jigilar Kashi 77 Na Mahajjatan Nijeriya Zuwa Saudiyya 

Tarayyar Turai ta dauki matakin rage amfani da gas da kashi 15 lokacin hunturu da kuma tabbatar da cewa cibiyoyin adana albarkatun gas sun cika zuwa kashi 80 kafin nan da 1 ga watan Nuwamba.

Kasashen Jamus da Faransa da Sifaniya na bullo da matakai da suka takaita amfani da abubuwa masu zafi a wuraren jama’a zuwa Celsius 19 lokacin hunturu.

Su ma Faransa da Sifaniya sun saka irin wannan mataki ga nau’rorin bayar sanyi a gine-gine lokacin bazara zuwa Celsius 26 da 27C. Haka nan ma, shaguna masu nau’rorin bayar da sanyi a Faransa za su rika rufe kofofinsu ko kuma a ci tararsu ta Yuro 750.

“Matakai masu sauki kamar rage abubuwan zafi zuwa ma’auni kadan a Turai za su rage yawan albarkatun gas da bututun Nord Stream 1 ke samar da shi a lokacin hunturu,’’ a cewar kungiyar makamashi ta kasa da kasa.

Rufe fitilun wuta

Jamus ta ce ba za a kunna wuta da daddare ba daga yanzu a gine[1]ginen jama’a ko wuraren tarihi, yayin a Sifaniya kuma za a rika kashe wuta a shaguna da misalin 10 na dare. Faransa na da yakinin cewa matakai da ta bijiro da su za su taimaka wajen rage makamashi da ake amfani da shi da kashi 10.

Kasar bata dogara da gas din da Rasha ke samar wa ba kamar makwabciyarta Jamus saboda kashi 42 na wutar lantarkinta na zuwa ne daga tashar Nukiliya.

Sai dai tsananin zafi da fari ya shafi nau’rorin bayar da sanyi a cibiyoyin nukiliya da dama wanda ya tilasta su rage yawan hasken da suke bayar wa.

Samun ruwan sama

China na fuskantar irin wannan matsalar ta makamashi. Yayin da mai da gas din da take samu daga Rasha ya gamu da cikas bayan afkuwatr fada da Ukraine, fari da kuma tsananin zafi sun yi matukar shafar su.

Wannan ya sanya koguna bushewa wadda kuma ya shafi bangaren bayar da hasken lantarki.

A lardin Sichuan, da ke samun kashi 80 na wutan lantarki daga madatsar ruwa, hukumomi sun tilastawa masana’antu rufewa na tsawon kwanaki shida domin rage wutar da ake amfani da ita, inda aka bai wa ofisoshi da kuma shaguna umarnin rufe wuta da kuma nau’rorin bayar da sanyi. Jihohi makwabta kamar Chongking su ma sun dauki irin wannan mataki.

Ministan aikin gona na kasar ya sanar da matakan ‘samar da gajimare’, inda ake sake sinadarai zuwa cikin gajimare domin samun ruwan sama, sai dai ba a sanar da wajen da za a yi hakan ba.

Rage lokutan aiki

Ita ma Pakistan, ta bullo da hanyoyin zamani domin rage makamashin da ake amfani da ita.

A watan Yunin wannan shekara, kasar ta sanar da cewa za ta rage kwanakin aiki a ofisoshin gwamnati daga shida zuwa biyar – wanda kuma ya juyawa matakin baya da aka sanar makon farko a baya, lokacin da sabuwar gwamnati ta karbi mulki a Islamabad da yin alkawarin kara inganta aikin gwamnati.

Makonni kadan daga baya, yanayi ya kai maki 50 na ma’aunin Celsius a Pakistan, wadda hakan ya kawo matsi ga babban layin samar da wutan lantarki a kasar.

Matsalar tsadar makamashi da ake kara fuskanta a duniya, ya sanya abubuwa tabarbarewa, inda a yanzu gwamnatoci ke duba matakan ganin ma’aikatanta sun yi aiki daga gida a ranakun Juma’a.

Rufe makarantu

Kasar Bangladesh ma na daukar irin wannan mataki, inda za a rufe makarantu na karin kwana daya a cikin mako, inda yanzu ranakun Asabar da Juma’a za su kasance na hutu.

An kuma rage sa’a daya ta aiki na ma’aikatan gwamnati a kwana guda daya.

Bangladesh ta dogara da shigo mata da iskar gas, wadda kuma na daya daga cikin nau’ukan mai mafi tsada.

Wannan kuma na nufin za ta yi gogayya da kasashe masu karfin tattalin arziki a Turai kafin samun gas dinta.

Makamin nukiliya

A wasu wurare, karuwar matsalar makamashi ta janyo koma baya na burbushin halittu.

Yawan gawayi da Indiya ke shigo da shi ya matakin sama a watan Yuni, duk da cewa gwamnati ta dauki matakai a baya na rage gawayi da take shigo da shi kasar. Amma kasashe na duba wasu hanyoyi na daban.

Bayan shekara 11 da aka samu bala’in cibiyar nukiliyar Japan ta Fukushima, kasar na duba yiwuwar samar da wata sabuwar cibiyar nukiliya.

Hasken rana

Matsalar ta makamashi za ta iya zama abu da za a iya sabuntawa. Faransa na shirin kara karfi wajen samar da makamashi.

Kasashe kamar Afirka ta Kudu da China na karfafawa ‘yan kasuwa da kuma daidaikun mutane zuba jari a bangaren nau’rorin samar da hasken rana, da bullo da matakai da kuma farashi da zai bar mutane sayar da makamashin wuta zuwa ga babbar layin samar da wutan lantarki a kasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hasken RanaJamusMatakaiRage Matsala
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasuwar Mile 12 Ta Na Jagorantar Hadin Kan ‘Yan Kasuwar Jihar Legas

Next Post

Ana Wata-ga-wata: Gwamnati Ta Sake Bankado Kadarorin Abba Kyari

Related

Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum
Manyan Labarai

Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

57 minutes ago
Hajjin Bana: Jihar Filato Ta Ba Da Kyautar Kujera 500 Da Tallafin Miliyan 2 Ga Duk Maniyyaci
Manyan Labarai

Hajji: NAHCON Ta Kammala Jigilar Kashi 77 Na Mahajjatan Nijeriya Zuwa Saudiyya 

18 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Na Ƙara Farfaɗowa – Gwamnan CBN
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Na Ƙara Farfaɗowa – Gwamnan CBN

21 hours ago
Na Kwana A Marte Ne Don Ƙarfafa Gwiwar Jama’a Bayan Harin Boko Haram – Zulum
Manyan Labarai

Na Kwana A Marte Ne Don Ƙarfafa Gwiwar Jama’a Bayan Harin Boko Haram – Zulum

1 day ago
Gwamnatin Kano Ta Hana Tallace-tallacen Magungunan Gargajiya A Fina-finai Da Kan Tituna
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Hana Tallace-tallacen Magungunan Gargajiya A Fina-finai Da Kan Tituna

1 day ago
Yanzu-yanzu: Tukunyar Gas Ta Fashe A Harabar Filin Wasannin Na Kasa Da Ke Gudana A Ogun
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Tukunyar Gas Ta Fashe A Harabar Filin Wasannin Na Kasa Da Ke Gudana A Ogun

2 days ago
Next Post
Ana Wata-ga-wata: Gwamnati Ta Sake Bankado Kadarorin Abba Kyari

Ana Wata-ga-wata: Gwamnati Ta Sake Bankado Kadarorin Abba Kyari

LABARAI MASU NASABA

Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

May 22, 2025
‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

May 21, 2025
Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

May 21, 2025
Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

May 21, 2025
Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

May 21, 2025
Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

May 21, 2025
Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

May 21, 2025
Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

May 21, 2025
Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban

Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban

May 21, 2025
Sabbin Ministoci

Boko Haram: Majalisar Dattijai Ta Amince Da Kafa Sansanin Sojoji A Hong Ta Jihar Adamawa

May 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.