• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matakai Bakwai Da Kasashe Ke Dauka Don Rage Matsalar Makamashi

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Matakai Bakwai Da Kasashe Ke Dauka Don Rage Matsalar Makamashi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasar Jamus ta sanar da matakan da take dauka domin rage makamashin da ake amfani da shi bayan fari da tsananin zafi da annobar Korona da kuma fadan Ukraine sun haifar da matsalar makamashi a duniya.

Sai dai karuwar matsalar makamashi ta taba ko’ina a duniya, inda Jamus ba ita ce kasa kadai da ta bullo da matakai domin tinkarar hakan.

  • Muna Zargin Masallatai Da Coci-coci Da Hannu A Satar Mai –Kyari
  • Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Keta Ka’idojin Fitar Da Kayayyaki

 Ga wasu hanyoyi bakwai da gwamnatoci suke dauka domin dakile matsalar ta makamashi. Nahiyar Turai na fuskantar matsalar makamashi da ba ta taba gani ba, bayan da Rasha da rage yawan gas din da take fitarwa ta bututun Nord Stream 1.

Hakan ne ya sa dakile matsalar matsalar makamashi ta zamo babban abu da gwamnatoci a Turai din suka sa gaba.

Rage abubuwa masu zafi da kuma na’urar bayar da sanyi

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

Tarayyar Turai ta dauki matakin rage amfani da gas da kashi 15 lokacin hunturu da kuma tabbatar da cewa cibiyoyin adana albarkatun gas sun cika zuwa kashi 80 kafin nan da 1 ga watan Nuwamba.

Kasashen Jamus da Faransa da Sifaniya na bullo da matakai da suka takaita amfani da abubuwa masu zafi a wuraren jama’a zuwa Celsius 19 lokacin hunturu.

Su ma Faransa da Sifaniya sun saka irin wannan mataki ga nau’rorin bayar sanyi a gine-gine lokacin bazara zuwa Celsius 26 da 27C. Haka nan ma, shaguna masu nau’rorin bayar da sanyi a Faransa za su rika rufe kofofinsu ko kuma a ci tararsu ta Yuro 750.

“Matakai masu sauki kamar rage abubuwan zafi zuwa ma’auni kadan a Turai za su rage yawan albarkatun gas da bututun Nord Stream 1 ke samar da shi a lokacin hunturu,’’ a cewar kungiyar makamashi ta kasa da kasa.

Rufe fitilun wuta

Jamus ta ce ba za a kunna wuta da daddare ba daga yanzu a gine[1]ginen jama’a ko wuraren tarihi, yayin a Sifaniya kuma za a rika kashe wuta a shaguna da misalin 10 na dare. Faransa na da yakinin cewa matakai da ta bijiro da su za su taimaka wajen rage makamashi da ake amfani da shi da kashi 10.

Kasar bata dogara da gas din da Rasha ke samar wa ba kamar makwabciyarta Jamus saboda kashi 42 na wutar lantarkinta na zuwa ne daga tashar Nukiliya.

Sai dai tsananin zafi da fari ya shafi nau’rorin bayar da sanyi a cibiyoyin nukiliya da dama wanda ya tilasta su rage yawan hasken da suke bayar wa.

Samun ruwan sama

China na fuskantar irin wannan matsalar ta makamashi. Yayin da mai da gas din da take samu daga Rasha ya gamu da cikas bayan afkuwatr fada da Ukraine, fari da kuma tsananin zafi sun yi matukar shafar su.

Wannan ya sanya koguna bushewa wadda kuma ya shafi bangaren bayar da hasken lantarki.

A lardin Sichuan, da ke samun kashi 80 na wutan lantarki daga madatsar ruwa, hukumomi sun tilastawa masana’antu rufewa na tsawon kwanaki shida domin rage wutar da ake amfani da ita, inda aka bai wa ofisoshi da kuma shaguna umarnin rufe wuta da kuma nau’rorin bayar da sanyi. Jihohi makwabta kamar Chongking su ma sun dauki irin wannan mataki.

Ministan aikin gona na kasar ya sanar da matakan ‘samar da gajimare’, inda ake sake sinadarai zuwa cikin gajimare domin samun ruwan sama, sai dai ba a sanar da wajen da za a yi hakan ba.

Rage lokutan aiki

Ita ma Pakistan, ta bullo da hanyoyin zamani domin rage makamashin da ake amfani da ita.

A watan Yunin wannan shekara, kasar ta sanar da cewa za ta rage kwanakin aiki a ofisoshin gwamnati daga shida zuwa biyar – wanda kuma ya juyawa matakin baya da aka sanar makon farko a baya, lokacin da sabuwar gwamnati ta karbi mulki a Islamabad da yin alkawarin kara inganta aikin gwamnati.

Makonni kadan daga baya, yanayi ya kai maki 50 na ma’aunin Celsius a Pakistan, wadda hakan ya kawo matsi ga babban layin samar da wutan lantarki a kasar.

Matsalar tsadar makamashi da ake kara fuskanta a duniya, ya sanya abubuwa tabarbarewa, inda a yanzu gwamnatoci ke duba matakan ganin ma’aikatanta sun yi aiki daga gida a ranakun Juma’a.

Rufe makarantu

Kasar Bangladesh ma na daukar irin wannan mataki, inda za a rufe makarantu na karin kwana daya a cikin mako, inda yanzu ranakun Asabar da Juma’a za su kasance na hutu.

An kuma rage sa’a daya ta aiki na ma’aikatan gwamnati a kwana guda daya.

Bangladesh ta dogara da shigo mata da iskar gas, wadda kuma na daya daga cikin nau’ukan mai mafi tsada.

Wannan kuma na nufin za ta yi gogayya da kasashe masu karfin tattalin arziki a Turai kafin samun gas dinta.

Makamin nukiliya

A wasu wurare, karuwar matsalar makamashi ta janyo koma baya na burbushin halittu.

Yawan gawayi da Indiya ke shigo da shi ya matakin sama a watan Yuni, duk da cewa gwamnati ta dauki matakai a baya na rage gawayi da take shigo da shi kasar. Amma kasashe na duba wasu hanyoyi na daban.

Bayan shekara 11 da aka samu bala’in cibiyar nukiliyar Japan ta Fukushima, kasar na duba yiwuwar samar da wata sabuwar cibiyar nukiliya.

Hasken rana

Matsalar ta makamashi za ta iya zama abu da za a iya sabuntawa. Faransa na shirin kara karfi wajen samar da makamashi.

Kasashe kamar Afirka ta Kudu da China na karfafawa ‘yan kasuwa da kuma daidaikun mutane zuba jari a bangaren nau’rorin samar da hasken rana, da bullo da matakai da kuma farashi da zai bar mutane sayar da makamashin wuta zuwa ga babbar layin samar da wutan lantarki a kasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hasken RanaJamusMatakaiRage Matsala
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasuwar Mile 12 Ta Na Jagorantar Hadin Kan ‘Yan Kasuwar Jihar Legas

Next Post

Ana Wata-ga-wata: Gwamnati Ta Sake Bankado Kadarorin Abba Kyari

Related

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

21 minutes ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

3 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

5 hours ago
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

9 hours ago
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

10 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

1 day ago
Next Post
Ana Wata-ga-wata: Gwamnati Ta Sake Bankado Kadarorin Abba Kyari

Ana Wata-ga-wata: Gwamnati Ta Sake Bankado Kadarorin Abba Kyari

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.