• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matakan Fara Sana’ar Hakar Ma’adanai Bisa Doka A Nijeriya

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
Ma'adanai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hakar ma’adanai na da matukar muhimmanci ga tattalin arzikin Nijeriya da ma Afirka gaba daya. Ta nan ne ake samar wa masana’antunmu na ciki da wajen kasa kayan sarrafawa, wanda kuma hakan ke samar da aikin yi ga dimbin matasa a ciki da wajen kasar nan.

A Nijeriya, tarihi ya nuna irin tasirin ma’adanai ga tattalin arzikin kasa inda ake samun fiye da kashi 0.3 na arzikin kasa daga bangaren ma’adanai (kamar yadda bayani ya nuna a kasafin kudin shekarar 2022). Bincike ya kuma nuna cewa, a yankin Afirka ake samun kashi 30 na dukkan ma’adanai na duniya, lamarin da ya sa Afirka a sahun gaba a harkar ma’adanai na duniya.

  • Matsalar Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Haramta Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Kotun Sauraren Karar Zaben Gwamna A Legas Za Ta Yanke Hukunci Ranar Litinin

Duk da kasancewar harkar hakar ma’adanai na da muhimmanci ga tattalin arzikin Nijeriya amma har zuwa yanzu ba a kai ga bunkasa sashin ba yadda ya kamata, saboda rashin cikakken kayan aiki na zama da rashin masu zuba jari da kuma yadda har yanzu ake ci gaba da amfani kayan aikin hakar ma’adanai ba na zamani, uwa uba kuma yadda masu hakar ma’adanai ba tare da izini ba suka mamaye bangaren. Wannan kuma yana samun bunkasa ne saboda yadda aka yi sakaci har ‘yan kasashe waje suka shigo suka mamaye bangaren suma suna hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba. Masana sun bayyana yadda hakar ma’adanai ba tare da cikakken izini ba ke cutar da muhalli da al’umma gaba daya.

A ‘yan shekarun nan gwamnati ta dauki matakai na ganin an farfado da bangaren hakar ma’adanai, musamman ganin ana ganin lokaci ya yi da za a duba wasu bangarori don nema wa Nijeriya kudaden shiga saboda ganin yadda kasuwar albarkatun man fetur yake komawa baya.

Gwamnati ta dauki matakai masu muhimmanci don jawo hankalin ‘yan kasuwa da masu zuba jari na ciki da wajen kasa don su shigo a dama da su a harkar hakar ma’adanai a Nijeriya, kuma daga dukkan alamu wannan matakai sun fara haifar da da mai ido.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

Ga wanda yake son fadawa harkar hakar ma’adanai a Nijeriya ga wasu matakai masu muhimmanci da za su iya taimaka masa don gudanar da harkar kamar yadda doka ta tanada.

1). Samun Lasisi Daga Hukuma: kafin fara hakar ma’adanai yana da kyau mutum ya nemi izinin gwamnati ta hanyar samun lasisi na irin harka ma’adanan da zai yi. Laisisin da ake bayarwa sun hada da na masu dan karamin karfi da kuma na manya-manyan kamfanoni. Lasisin kuma zai iya kasancewa na mai haka kai staye ko mai sarrafawa, ko kuma na masu tsotso ruwa suna sayarwa, wato kamar masu ‘Fiya wata’ duk sai sun samu lasisi, ana kuma samun lasisin ne a karkashin ofishin gwmanati mai suna ‘Nigerian Cadastre’ wanda sune ke da alhakin sa ido a kan dukkan harkokin hakar ma’adanai a Nijeriya. A kwai kuma bukatar mutum ya nemi cikakken bayani na yadda ofishinsu ke aiki don ya samu saukin yin rajistar. Haka kuma cikin sharuddan dole mutum ya yi rajistar kamfaninsa tare da hukumar yi wa kamfanoni rajista a Nijeriya wato “Cooperate Affairs Commission” don sunan kamfanin mutum ya shiga cikin jerin kamfanoni da ke harkokinsu a Nijeriya, wannan na da matukar muhimmanci.
2). Bayanin Yadda Za A Gudanar Da Kasuwancin Ma’adanan ‘Business Plan’:
Akwai bukatar a samu cikakken bayani na irin ma’adanan da ake son fara haka da inda ake samunsu, yana kuma da muhimmanci a gudanar da bincike na kimiyya don sanin yawan ma’adanan a yankin, saboda ganin irin jarin da za a zuba.
3). Binciken Wurin Da Ake Son Gudanar Da Hakar Ma’adanan
Wannan kuma bincike ne na musamman da kwararru ke gudanarwa a wurin da ake son fara hakar ma’adanan don a gano hakikanin yawan ma’adanan da ke a cikin kasa, ta haka za a iya fahimtar yawa da ingancin ma’adanan don kada masu zuba jari su yi asara.
4). Binciken Kimiyya:
Binciken kimiyya a wurin da ake sa ran hakar ma’adanai yana bayar da bayanai don gane ainihin yawan ma’adanain da ake da shi a kasa da kuma yawan da za a iya hakowa a kullum. Wannan yana bayar da daman tsara yadda za a fuskanci aikin da yawan ma’akatan da ake bukata don samun cikakkiyar nasara.
5). Samar Da Kayyakin Aiki Na Zamani:
Yana da matukar muhimmanci samar da kayan aiki na zamani da za a gudanar da aiki a cikin sauki, wannan kuma ya hada da motoci na daukar ma’adanai da aka hako da muka ma’aikata.
6). Samar Da Wutar Lantarki Da Gidajen Ma’aikata
Yana da muhimmanci a samar da wurin kwana ga ma’aikata, yana kuma da kyau a gina gidan nesa da wurin da ake hakar ma’adanan saboda kariya daga cutar da ma’aikatan daga turirin ma’adanan da ake hakowa. Haka kuma samar da wutar lantarki na NEPA ko janaretab zai taimaka.
7). Fara Hakar Ma’adanan Gadan-gadan:
Daga nan kuma sai a fara aiki don ci gajiyar ma’adanan da aka shirya haka, ana taftacesu tare da wucewa da su kasuwa a ciki ko wajen kasa.

Yana kuma da muhimmanci a shigar da Sarakuna gargajiya da shugabanin matasa na yankin da ake hakar ma’adanan don kasancewa cikin jerin ma’aikata ko ‘yan kwangon da za su samar da wasu kayyakin aiki a ma’aikatar, wannan yana da matukar muhimmanci don rage kishi na ganin ana kwashe masu albarkatun kasa su kuma basu ci gajiyar abin ba. In har aka shigar da su, su da kansu za su ba harkar kariya daga duk wani abin da zai cutar da tafiyar saboda suma suna amfana. A na gaba za mu kawo muku irin ma’adanan da Allah ya shimfida a sassan Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchiMa’adanaiYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Cunkoso A Gidan Yari: Yadda Mutum 1400 Ke Zaman Jiran Shari’a A Nasarawa

Next Post

Ta Ina Talakawa Za Su Mori Rage Farashin Simintin BUA?

Related

Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

3 hours ago
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa
Labarai

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

5 hours ago
Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano
Labarai

Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano

6 hours ago
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno
Labarai

Bam Ya Hallaka Ma’aikatan Hukumar Ilimi 2 A Hanyar Damboa-Maiduguri

8 hours ago
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027
Siyasa

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

9 hours ago
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19
Manyan Labarai

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

10 hours ago
Next Post
BUA

Ta Ina Talakawa Za Su Mori Rage Farashin Simintin BUA?

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

May 13, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

May 13, 2025
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

May 13, 2025
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

May 13, 2025
Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano

Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano

May 13, 2025
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

May 13, 2025
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Bam Ya Hallaka Ma’aikatan Hukumar Ilimi 2 A Hanyar Damboa-Maiduguri

May 13, 2025
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

May 13, 2025
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

May 13, 2025
Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.