• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matar Da Ta Fi Amfanar Da Al’umma A Shekarar 2024: Olori Atuwatse III

by Leadership Hausa
10 months ago
in Labarai
0
Olori Atuwatse III
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Olori Atuwatse III, ita ce ta kafa gidauniyar Elevate Africa, ta samu wannan karramawar ne saboda gudummawar da take bayarwa ga al’umma ta fuskar amfanar da su a fannonin ilimi da jagoranci nagari da tallafawa jama’a musamman mabuƙata.

Wasu daga cikin ɓangarorin da ta yi fice wanda suka kai ga samun wannan karramawar sun haɗa da tallafawa al’umma ta hannun gidauniyar “Royal Iwere Foundation (RIF)”, Olori, ta samar da shirye-shirye masu tasiri ga jama’a kamar horar da malamai da shirin ƙarfafa gwuiwa a fannin ƙirƙire-ƙirƙire da fannoni da dama wajen mayar da hankali a fannin inganta ilimi da kiwon lafiya da inganta tattalin arziƙi ga matasa, musamman ‘ya’ya mata da  sauran al’umma.

  • Katafaren Aikin Karkatar Da Ruwa Na Sin Ya Karkata Kyubik Mita Biliyan 76.5 Zuwa Arewacin Kasar
  • Bankin Zenith Ya Tallafa Wa Matasa Da Naira Miliyan 77 A Jihar Legas

Ta kasance mamba a babban kwamitin bayar da shawarwari kan inganta harkokin mata a Nijeriya (HLAC), don bai wa mata damar dogaro a kai. Olori, ta haɗa kai da gwamnati a fafutukar da take na magance matsalolin da suka shafi mata da kawar da fifiko wajen samar da damarmaki.

Olori Atuwatse III, tana matuƙar ƙoƙari wajen ganin ci gaban matasa ta yadda take taka muhimmiyar rawa don  samar wa matasan kayan aiki da ba su horo kan fasahar sana’o’i ta yadda za su dogara da kansu, wannan yunƙuri ya taimaka wajen kawar da zaman kashe wando a ƙasarnan, tare da bai wa matasa damar yin nasara wajen cimma burikansu na rayuwa.

Olori, mace ce mai matuƙar tasiri a duniya, kasancewarta ɗaya daga cikin Matan Afirka 100 masu tasiri a shekarar 2023, ta kuma taɓa yin alƙalanci a shirin gasar lambar yabo ta Diana a 2024, bugu da ƙari tana taka muhimmiyar rawa a matsayin mai bayar da shawara don samar da  ingantaccen canji a duniya.

Labarai Masu Nasaba

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

Baya da cewa ta yi karatu a fannin shari’a daga Makarantar Tattalin Arziki ta London, Olori, ta kafa manyan wuraren harkokin kasuwanci da yin nasara a ɓangarori daban-daban da suka haɗa da fannin dinke-dinke da sauransu, ta kuma kasance ɗaya daga cikin masu jagorantar masana’antu da dama, inda ta bayar da bayar da gagarumar gudummawa wajen  ɓunƙasa su.

Olori Atuwatse III, ta yi gadon mulki da tasiri a wajen al’umma, kasancewarta Sarauniyar Warri, kuma uwa ce mai kishin ƙasa wadda ta himmatu wajen barin gadon ilimi da ƙarfafa wa al’umma da samar musu da ci gaba mai ɗorewa a masarautar Warri da duniya baki ɗaya.

Olori Atuwatse III, mata ce ga Sarkin Warri Ogiame Atuwatse III, wanda suke da ‘ya’ya uku, rashin nasara ba ya daƙile mutum wajene cinma burinsa, sai dai ta haska masa ba ya kan turbar da zai kai ga nasarar da inda ya kamata ya bi. saboda haka akwai buƙatar ya sauya alkibla tare da ƙara ƙaimi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: #GwarzonShekara2024 #Award2024 #Leadership #LeadershipAward #LabaraiOlori Atuwatse III
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Banki A Shekarar 2024: Dame (Dr.) Adaora Umeoji

Next Post

Gwarzon Shugaban Kamfani Mallakar Gwamnati Na 2024: Bamanga Usman Jada

Related

Tinubu
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

27 minutes ago
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa
Labarai

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

1 hour ago
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
Labarai

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

2 hours ago
Neja
Labarai

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

3 hours ago
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
Labarai

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

4 hours ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

6 hours ago
Next Post
Bamanga Usman Jada

Gwarzon Shugaban Kamfani Mallakar Gwamnati Na 2024: Bamanga Usman Jada

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

September 15, 2025
Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

September 15, 2025
Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.