• English
  • Business News
Tuesday, July 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matar Da Ta Fi Amfanar Da Al’umma A Shekarar 2024: Olori Atuwatse III

by Leadership Hausa
8 months ago
in Labarai
0
Olori Atuwatse III
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Olori Atuwatse III, ita ce ta kafa gidauniyar Elevate Africa, ta samu wannan karramawar ne saboda gudummawar da take bayarwa ga al’umma ta fuskar amfanar da su a fannonin ilimi da jagoranci nagari da tallafawa jama’a musamman mabuƙata.

Wasu daga cikin ɓangarorin da ta yi fice wanda suka kai ga samun wannan karramawar sun haɗa da tallafawa al’umma ta hannun gidauniyar “Royal Iwere Foundation (RIF)”, Olori, ta samar da shirye-shirye masu tasiri ga jama’a kamar horar da malamai da shirin ƙarfafa gwuiwa a fannin ƙirƙire-ƙirƙire da fannoni da dama wajen mayar da hankali a fannin inganta ilimi da kiwon lafiya da inganta tattalin arziƙi ga matasa, musamman ‘ya’ya mata da  sauran al’umma.

  • Katafaren Aikin Karkatar Da Ruwa Na Sin Ya Karkata Kyubik Mita Biliyan 76.5 Zuwa Arewacin Kasar
  • Bankin Zenith Ya Tallafa Wa Matasa Da Naira Miliyan 77 A Jihar Legas

Ta kasance mamba a babban kwamitin bayar da shawarwari kan inganta harkokin mata a Nijeriya (HLAC), don bai wa mata damar dogaro a kai. Olori, ta haɗa kai da gwamnati a fafutukar da take na magance matsalolin da suka shafi mata da kawar da fifiko wajen samar da damarmaki.

Olori Atuwatse III, tana matuƙar ƙoƙari wajen ganin ci gaban matasa ta yadda take taka muhimmiyar rawa don  samar wa matasan kayan aiki da ba su horo kan fasahar sana’o’i ta yadda za su dogara da kansu, wannan yunƙuri ya taimaka wajen kawar da zaman kashe wando a ƙasarnan, tare da bai wa matasa damar yin nasara wajen cimma burikansu na rayuwa.

Olori, mace ce mai matuƙar tasiri a duniya, kasancewarta ɗaya daga cikin Matan Afirka 100 masu tasiri a shekarar 2023, ta kuma taɓa yin alƙalanci a shirin gasar lambar yabo ta Diana a 2024, bugu da ƙari tana taka muhimmiyar rawa a matsayin mai bayar da shawara don samar da  ingantaccen canji a duniya.

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Baya da cewa ta yi karatu a fannin shari’a daga Makarantar Tattalin Arziki ta London, Olori, ta kafa manyan wuraren harkokin kasuwanci da yin nasara a ɓangarori daban-daban da suka haɗa da fannin dinke-dinke da sauransu, ta kuma kasance ɗaya daga cikin masu jagorantar masana’antu da dama, inda ta bayar da bayar da gagarumar gudummawa wajen  ɓunƙasa su.

Olori Atuwatse III, ta yi gadon mulki da tasiri a wajen al’umma, kasancewarta Sarauniyar Warri, kuma uwa ce mai kishin ƙasa wadda ta himmatu wajen barin gadon ilimi da ƙarfafa wa al’umma da samar musu da ci gaba mai ɗorewa a masarautar Warri da duniya baki ɗaya.

Olori Atuwatse III, mata ce ga Sarkin Warri Ogiame Atuwatse III, wanda suke da ‘ya’ya uku, rashin nasara ba ya daƙile mutum wajene cinma burinsa, sai dai ta haska masa ba ya kan turbar da zai kai ga nasarar da inda ya kamata ya bi. saboda haka akwai buƙatar ya sauya alkibla tare da ƙara ƙaimi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: #GwarzonShekara2024 #Award2024 #Leadership #LeadershipAward #LabaraiOlori Atuwatse III
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Banki A Shekarar 2024: Dame (Dr.) Adaora Umeoji

Next Post

Gwarzon Shugaban Kamfani Mallakar Gwamnati Na 2024: Bamanga Usman Jada

Related

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

3 hours ago
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China
Labarai

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

4 hours ago
Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba
Ra'ayi Riga

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

5 hours ago
Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta
Labarai

Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta

5 hours ago
Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura
Manyan Labarai

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

6 hours ago
Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari

8 hours ago
Next Post
Bamanga Usman Jada

Gwarzon Shugaban Kamfani Mallakar Gwamnati Na 2024: Bamanga Usman Jada

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

July 15, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

July 15, 2025
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

July 15, 2025
Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

July 15, 2025
Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta

Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta

July 15, 2025
Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.