ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matar Da Ta Fi Amfanar Da Al’umma A Shekarar 2024: Olori Atuwatse III

by Leadership Hausa
2 years ago
Olori Atuwatse III

Olori Atuwatse III, ita ce ta kafa gidauniyar Elevate Africa, ta samu wannan karramawar ne saboda gudummawar da take bayarwa ga al’umma ta fuskar amfanar da su a fannonin ilimi da jagoranci nagari da tallafawa jama’a musamman mabuƙata.

Wasu daga cikin ɓangarorin da ta yi fice wanda suka kai ga samun wannan karramawar sun haɗa da tallafawa al’umma ta hannun gidauniyar “Royal Iwere Foundation (RIF)”, Olori, ta samar da shirye-shirye masu tasiri ga jama’a kamar horar da malamai da shirin ƙarfafa gwuiwa a fannin ƙirƙire-ƙirƙire da fannoni da dama wajen mayar da hankali a fannin inganta ilimi da kiwon lafiya da inganta tattalin arziƙi ga matasa, musamman ‘ya’ya mata da  sauran al’umma.

  • Katafaren Aikin Karkatar Da Ruwa Na Sin Ya Karkata Kyubik Mita Biliyan 76.5 Zuwa Arewacin Kasar
  • Bankin Zenith Ya Tallafa Wa Matasa Da Naira Miliyan 77 A Jihar Legas

Ta kasance mamba a babban kwamitin bayar da shawarwari kan inganta harkokin mata a Nijeriya (HLAC), don bai wa mata damar dogaro a kai. Olori, ta haɗa kai da gwamnati a fafutukar da take na magance matsalolin da suka shafi mata da kawar da fifiko wajen samar da damarmaki.

ADVERTISEMENT

Olori Atuwatse III, tana matuƙar ƙoƙari wajen ganin ci gaban matasa ta yadda take taka muhimmiyar rawa don  samar wa matasan kayan aiki da ba su horo kan fasahar sana’o’i ta yadda za su dogara da kansu, wannan yunƙuri ya taimaka wajen kawar da zaman kashe wando a ƙasarnan, tare da bai wa matasa damar yin nasara wajen cimma burikansu na rayuwa.

Olori, mace ce mai matuƙar tasiri a duniya, kasancewarta ɗaya daga cikin Matan Afirka 100 masu tasiri a shekarar 2023, ta kuma taɓa yin alƙalanci a shirin gasar lambar yabo ta Diana a 2024, bugu da ƙari tana taka muhimmiyar rawa a matsayin mai bayar da shawara don samar da  ingantaccen canji a duniya.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Baya da cewa ta yi karatu a fannin shari’a daga Makarantar Tattalin Arziki ta London, Olori, ta kafa manyan wuraren harkokin kasuwanci da yin nasara a ɓangarori daban-daban da suka haɗa da fannin dinke-dinke da sauransu, ta kuma kasance ɗaya daga cikin masu jagorantar masana’antu da dama, inda ta bayar da bayar da gagarumar gudummawa wajen  ɓunƙasa su.

Olori Atuwatse III, ta yi gadon mulki da tasiri a wajen al’umma, kasancewarta Sarauniyar Warri, kuma uwa ce mai kishin ƙasa wadda ta himmatu wajen barin gadon ilimi da ƙarfafa wa al’umma da samar musu da ci gaba mai ɗorewa a masarautar Warri da duniya baki ɗaya.

Olori Atuwatse III, mata ce ga Sarkin Warri Ogiame Atuwatse III, wanda suke da ‘ya’ya uku, rashin nasara ba ya daƙile mutum wajene cinma burinsa, sai dai ta haska masa ba ya kan turbar da zai kai ga nasarar da inda ya kamata ya bi. saboda haka akwai buƙatar ya sauya alkibla tare da ƙara ƙaimi.

Olori Atuwatse III
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Bamanga Usman Jada

Gwarzon Shugaban Kamfani Mallakar Gwamnati Na 2024: Bamanga Usman Jada

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.