Tsohon Gwamnan Jihar Zamfara, Bello Matawale, ya bada tallafin kudi naira miliyan 200 don sayo Shanu da Ragunan Layya da rabon tsabar kudi ga mutane daban-daban a jihar don saukaka musu da basu damar samun yin Layya.
Sakataren yada labaran Jam’iyyar APC a jihar, Yusuf Idrisa Gusau, ne ya sanar da hakan a wata sanarwar menema labarai da ya fitar a Gusau a karshen mako.
- ‘Yansanda Sun Mayar Wa Da Kotu Motocin Da Aka Dauka A Gidan Matawalle – ‘Yansanda
- ‘Yansanda Sun Kai Samame Gidan Matawalle, Sun Kwace Motoci 40
Matawalle, wanda yake daya daga cikin Jagororin jam’iyyar APC a jihar, ya umarci shugabannin jam’iyyar APC na jihar karkashin shugabanta, Hon. Tukur Umar Danfulani, da ya jagoranci rabon Shanun da Ragunan layyar.
Wadanda za su ci gajiyar rabon sun hada da ‘Yan Jam’iyyar APC, marayu da marasa galihu da malaman addinin Musulunci da dai sauransu.
Shugaban jam’iyyar ya mika godiyarsa ga tsohon Gwamna, Bello Matawallen, kan wannan karamcin da ya yi wa al’umar Jihar Zamfara.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp