ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Mayar Wa Da Kotu Motocin Da Aka Dauka A Gidan Matawalle – ‘Yansanda

Jami'in hulda da jama'a na rundunar 'yan sandan jihar, Yazid Abubakar, ya ce an mayar da motocin ne bisa bin umarnin babbar kotun tarayya da ke Gusau.

by Muhammad
3 years ago
Matawalle

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta ce ta mayar da dukkanin motocin da ta kama daga hannun tsohon gwamnan jihar, Bello Matawalle zuwa kotu.

Wata tattaunawa ta wayar tarho da gidan Telebijin na Channels ya yi ranar Asabar da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Yazid Abubakar, ya ce an mayar da motocin ne bisa bin umarnin babbar kotun tarayya da ke Gusau.

  • ‘Yansanda Sun Kai Samame Gidan Matawalle, Sun Kwace Motoci 40
  • Sakarci Da Talauci Ne Yasa Gwamnatin Zamfara Shiga Gidana Sata- Bello Matawalle

“Eh, rundunar ‘yan sanda ta bi umarnin kotu dangane da mayar da dukkan motocin tsohon gwamna Bello Matawalle,” Cewar Kakakin ‘Yansandan.

ADVERTISEMENT

“Mun mayar da dukkan motocin zuwa harabar babbar kotun tarayya da ke Gusau, kamar yadda nake magana da ku yanzu, babu wata mota guda da ke hannun ‘yan sanda.”

A ranar 15 ga watan Yuni, mai shari’a Aliyu Bappa na babbar kotun tarayya Gusau ya umurci dukkanin jami’an tsaro da ke da ruwa da tsaki wajen kwashe motocin daga gidajen Matawalle na Gusau da Maradun da su dawo da su cikin sa’o’i 48.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Kotun ta kuma bayar da umarnin dakatar da wadanda ake kara a karar da Matawalle ya shigar a gaban kotu daga daukar wani mataki na gaba dangane da lamarin.

Wadanda suka amsa karar sun hada da Sufeto-Janar na ‘yan sandan Nijeriya da hukumar ‘yan sandan Nijeriya da kwamishinan ‘yan sandan jihar Zamfara da hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) da kuma hukumar tsaro ta farin kaya (NSCDC).

Gidan Talabijin na Channels ya ziyarci babbar kotun tarayya da safiyar Lahadi domin tabbatar da wannan umarnin inda ya rawaito cewa motoci 29 ne kawai ke harabar kotun har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto.

Sai dai majiyoyi sun ce har yanzu wasu motocin na nan a sansanin ‘yan sanda ana sa ran za su isa Gusau a yau Lahadi ko kuma safiyar Litinin.

Sai dai har yanzu tsohon gwamnan bai tabbatar da ko an dawo da motocin ba, har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto.

A baya dai gwamnatin jihar Zamfara ta ce an kwato fiye da motoci 40 da suka hada da motocin hana shigar harsashi guda uku da kuma SUV guda takwas daga gidajen tsohon gwamnan biyu.

Matawalle
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    ‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo
Labarai

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Next Post
Mata Sun Cancanci Samun Karin Mukamai A Gwamnati — Remi Tinubu

Mata Sun Cancanci Samun Karin Mukamai A Gwamnati — Remi Tinubu

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.