ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kai Samame Gidan Matawalle, Sun Kwace Motoci 40

by Sadiq
3 years ago
Matawalle

Gwamnatin Jihar Zamfara ta bada umarnin kai samame gidan tsohon gwamnan jihar, Muhammad Bello Matawalle tare da kwace wasu motoci da ake kyautata zaton na gwamnatin jihar ne.

A ranar Juma’a ne aka kwace wasu motocin a gidan Matawalle da ke Gusau.

  • Motocin Fasinja Kirar Sin Da Aka Sayar Sun Karu Da Kashi 37.6 A Mayu
  • Sabon Shugaban Kamfanin Jiragen Saman Nijeriya Ya Yi Tonon Silili

Idan za a iya tunawa, da yake magana a wani gidan rediyon yankin, Gwamna mai ci Dauda Lawal ya ce, “Tsohon Gwamna Bello Matawalle ya tafi da motoci 17 daga ofishinsa da kuma wadanda ke ofishin mataimakin gwamna yana mai cewa motocinsa ne, asali ma kayan ofis ma ba su tsira ba.”

ADVERTISEMENT

A cewar wani rahoto, an kwashe motoci kirar jeeps masu sulke guda hudu.

An ce ‘yansanda sun kai farmaki gidan tsohon gwamnan, wanda ba shi da nisa da gidan gwamnati a Gusau, babban birnin jihar.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

LEADERSHIP ta rawaito cewa Gwamna Lawal ya zargi Matawalle da yin awon gaba da motocin gwamnati tare da wawashe kadarori da suka hada da talabijin da kayan dafa abinci a gidan gwamnatin jihar da ofishin hulda da jama’a na jihar da ke Abuja.

A ranar Asabar din da ta gabata ne, Lawal ya bai wa Matawalle wa’adin kwanaki biyar ya mayar da motocin da ake zargin jami’an gwamnatinsa sun tafi da su.

Lawal wanda ya bada wa’adin ta wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sulaiman Idris ya fitar, ya sha alwashin kwato kudade da kadarorin gwamnatin jihar da aka sace.

“Muna da hujjoji da bayanan da ke nuna rashin dacewar Matawalle. Ina karyar ta ke? Tsohon gwamnan ya bayar da kwangilar sayen motocin da za a raba wa manyan ma’aikatu kan kudi Naira biliyan 1,149,800,000.

“An bayar da kwangilar siyan motocin ga kamfanin Hafkhad Properties and Facilities Management Nig. Ltd.

“An yi amfani da kudin ne don siyan mota kirar Toyota Lexus VIP mai kare harsashi.

“Mun sanar da tsohon Gwamna Bello Matawalle da Mataimakinsa a hukumance cewa su dawo da dukkan motocin da suka bace cikin kwanaki biyar,” in ji shi.

A lokacin da LEADERSHIP ta tuntubi gwamnatin Jihar Zamfara kan lamarin, mai magana da yawun Gwamna Lawal, Sulaiman Bala Idris, ya shaida wa wakilinmu cewa bai da masaniyar cewa shugaban nasa ne ya bayar da umarnin kai samamen, inda ya ce ‘yansanda na yin aikinsu ne kawai.

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
Alfanu Da Rashin Alfanun Rusau A Kano Daga Bakin Kanawa

Alfanu Da Rashin Alfanun Rusau A Kano Daga Bakin Kanawa

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.