ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kai Samame Gidan Matawalle, Sun Kwace Motoci 40

by Sadiq
3 years ago
Matawalle

Gwamnatin Jihar Zamfara ta bada umarnin kai samame gidan tsohon gwamnan jihar, Muhammad Bello Matawalle tare da kwace wasu motoci da ake kyautata zaton na gwamnatin jihar ne.

A ranar Juma’a ne aka kwace wasu motocin a gidan Matawalle da ke Gusau.

  • Motocin Fasinja Kirar Sin Da Aka Sayar Sun Karu Da Kashi 37.6 A Mayu
  • Sabon Shugaban Kamfanin Jiragen Saman Nijeriya Ya Yi Tonon Silili

Idan za a iya tunawa, da yake magana a wani gidan rediyon yankin, Gwamna mai ci Dauda Lawal ya ce, “Tsohon Gwamna Bello Matawalle ya tafi da motoci 17 daga ofishinsa da kuma wadanda ke ofishin mataimakin gwamna yana mai cewa motocinsa ne, asali ma kayan ofis ma ba su tsira ba.”

ADVERTISEMENT

A cewar wani rahoto, an kwashe motoci kirar jeeps masu sulke guda hudu.

An ce ‘yansanda sun kai farmaki gidan tsohon gwamnan, wanda ba shi da nisa da gidan gwamnati a Gusau, babban birnin jihar.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

LEADERSHIP ta rawaito cewa Gwamna Lawal ya zargi Matawalle da yin awon gaba da motocin gwamnati tare da wawashe kadarori da suka hada da talabijin da kayan dafa abinci a gidan gwamnatin jihar da ofishin hulda da jama’a na jihar da ke Abuja.

A ranar Asabar din da ta gabata ne, Lawal ya bai wa Matawalle wa’adin kwanaki biyar ya mayar da motocin da ake zargin jami’an gwamnatinsa sun tafi da su.

Lawal wanda ya bada wa’adin ta wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sulaiman Idris ya fitar, ya sha alwashin kwato kudade da kadarorin gwamnatin jihar da aka sace.

“Muna da hujjoji da bayanan da ke nuna rashin dacewar Matawalle. Ina karyar ta ke? Tsohon gwamnan ya bayar da kwangilar sayen motocin da za a raba wa manyan ma’aikatu kan kudi Naira biliyan 1,149,800,000.

“An bayar da kwangilar siyan motocin ga kamfanin Hafkhad Properties and Facilities Management Nig. Ltd.

“An yi amfani da kudin ne don siyan mota kirar Toyota Lexus VIP mai kare harsashi.

“Mun sanar da tsohon Gwamna Bello Matawalle da Mataimakinsa a hukumance cewa su dawo da dukkan motocin da suka bace cikin kwanaki biyar,” in ji shi.

A lokacin da LEADERSHIP ta tuntubi gwamnatin Jihar Zamfara kan lamarin, mai magana da yawun Gwamna Lawal, Sulaiman Bala Idris, ya shaida wa wakilinmu cewa bai da masaniyar cewa shugaban nasa ne ya bayar da umarnin kai samamen, inda ya ce ‘yansanda na yin aikinsu ne kawai.

MASU ALAKA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Next Post
Alfanu Da Rashin Alfanun Rusau A Kano Daga Bakin Kanawa

Alfanu Da Rashin Alfanun Rusau A Kano Daga Bakin Kanawa

LABARAI MASU NASABA

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.