ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kai Samame Gidan Matawalle, Sun Kwace Motoci 40

by Sadiq
3 years ago
Matawalle

Gwamnatin Jihar Zamfara ta bada umarnin kai samame gidan tsohon gwamnan jihar, Muhammad Bello Matawalle tare da kwace wasu motoci da ake kyautata zaton na gwamnatin jihar ne.

A ranar Juma’a ne aka kwace wasu motocin a gidan Matawalle da ke Gusau.

  • Motocin Fasinja Kirar Sin Da Aka Sayar Sun Karu Da Kashi 37.6 A Mayu
  • Sabon Shugaban Kamfanin Jiragen Saman Nijeriya Ya Yi Tonon Silili

Idan za a iya tunawa, da yake magana a wani gidan rediyon yankin, Gwamna mai ci Dauda Lawal ya ce, “Tsohon Gwamna Bello Matawalle ya tafi da motoci 17 daga ofishinsa da kuma wadanda ke ofishin mataimakin gwamna yana mai cewa motocinsa ne, asali ma kayan ofis ma ba su tsira ba.”

ADVERTISEMENT

A cewar wani rahoto, an kwashe motoci kirar jeeps masu sulke guda hudu.

An ce ‘yansanda sun kai farmaki gidan tsohon gwamnan, wanda ba shi da nisa da gidan gwamnati a Gusau, babban birnin jihar.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

LEADERSHIP ta rawaito cewa Gwamna Lawal ya zargi Matawalle da yin awon gaba da motocin gwamnati tare da wawashe kadarori da suka hada da talabijin da kayan dafa abinci a gidan gwamnatin jihar da ofishin hulda da jama’a na jihar da ke Abuja.

A ranar Asabar din da ta gabata ne, Lawal ya bai wa Matawalle wa’adin kwanaki biyar ya mayar da motocin da ake zargin jami’an gwamnatinsa sun tafi da su.

Lawal wanda ya bada wa’adin ta wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sulaiman Idris ya fitar, ya sha alwashin kwato kudade da kadarorin gwamnatin jihar da aka sace.

“Muna da hujjoji da bayanan da ke nuna rashin dacewar Matawalle. Ina karyar ta ke? Tsohon gwamnan ya bayar da kwangilar sayen motocin da za a raba wa manyan ma’aikatu kan kudi Naira biliyan 1,149,800,000.

“An bayar da kwangilar siyan motocin ga kamfanin Hafkhad Properties and Facilities Management Nig. Ltd.

“An yi amfani da kudin ne don siyan mota kirar Toyota Lexus VIP mai kare harsashi.

“Mun sanar da tsohon Gwamna Bello Matawalle da Mataimakinsa a hukumance cewa su dawo da dukkan motocin da suka bace cikin kwanaki biyar,” in ji shi.

A lokacin da LEADERSHIP ta tuntubi gwamnatin Jihar Zamfara kan lamarin, mai magana da yawun Gwamna Lawal, Sulaiman Bala Idris, ya shaida wa wakilinmu cewa bai da masaniyar cewa shugaban nasa ne ya bayar da umarnin kai samamen, inda ya ce ‘yansanda na yin aikinsu ne kawai.

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
Next Post
Alfanu Da Rashin Alfanun Rusau A Kano Daga Bakin Kanawa

Alfanu Da Rashin Alfanun Rusau A Kano Daga Bakin Kanawa

LABARAI MASU NASABA

Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.