ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kai Samame Gidan Matawalle, Sun Kwace Motoci 40

by Sadiq
3 years ago
Matawalle

Gwamnatin Jihar Zamfara ta bada umarnin kai samame gidan tsohon gwamnan jihar, Muhammad Bello Matawalle tare da kwace wasu motoci da ake kyautata zaton na gwamnatin jihar ne.

A ranar Juma’a ne aka kwace wasu motocin a gidan Matawalle da ke Gusau.

  • Motocin Fasinja Kirar Sin Da Aka Sayar Sun Karu Da Kashi 37.6 A Mayu
  • Sabon Shugaban Kamfanin Jiragen Saman Nijeriya Ya Yi Tonon Silili

Idan za a iya tunawa, da yake magana a wani gidan rediyon yankin, Gwamna mai ci Dauda Lawal ya ce, “Tsohon Gwamna Bello Matawalle ya tafi da motoci 17 daga ofishinsa da kuma wadanda ke ofishin mataimakin gwamna yana mai cewa motocinsa ne, asali ma kayan ofis ma ba su tsira ba.”

ADVERTISEMENT

A cewar wani rahoto, an kwashe motoci kirar jeeps masu sulke guda hudu.

An ce ‘yansanda sun kai farmaki gidan tsohon gwamnan, wanda ba shi da nisa da gidan gwamnati a Gusau, babban birnin jihar.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

LEADERSHIP ta rawaito cewa Gwamna Lawal ya zargi Matawalle da yin awon gaba da motocin gwamnati tare da wawashe kadarori da suka hada da talabijin da kayan dafa abinci a gidan gwamnatin jihar da ofishin hulda da jama’a na jihar da ke Abuja.

A ranar Asabar din da ta gabata ne, Lawal ya bai wa Matawalle wa’adin kwanaki biyar ya mayar da motocin da ake zargin jami’an gwamnatinsa sun tafi da su.

Lawal wanda ya bada wa’adin ta wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sulaiman Idris ya fitar, ya sha alwashin kwato kudade da kadarorin gwamnatin jihar da aka sace.

“Muna da hujjoji da bayanan da ke nuna rashin dacewar Matawalle. Ina karyar ta ke? Tsohon gwamnan ya bayar da kwangilar sayen motocin da za a raba wa manyan ma’aikatu kan kudi Naira biliyan 1,149,800,000.

“An bayar da kwangilar siyan motocin ga kamfanin Hafkhad Properties and Facilities Management Nig. Ltd.

“An yi amfani da kudin ne don siyan mota kirar Toyota Lexus VIP mai kare harsashi.

“Mun sanar da tsohon Gwamna Bello Matawalle da Mataimakinsa a hukumance cewa su dawo da dukkan motocin da suka bace cikin kwanaki biyar,” in ji shi.

A lokacin da LEADERSHIP ta tuntubi gwamnatin Jihar Zamfara kan lamarin, mai magana da yawun Gwamna Lawal, Sulaiman Bala Idris, ya shaida wa wakilinmu cewa bai da masaniyar cewa shugaban nasa ne ya bayar da umarnin kai samamen, inda ya ce ‘yansanda na yin aikinsu ne kawai.

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Alfanu Da Rashin Alfanun Rusau A Kano Daga Bakin Kanawa

Alfanu Da Rashin Alfanun Rusau A Kano Daga Bakin Kanawa

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.