• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Da Ta Haddasa Harin Bom Na Kaduna

by Bello Hamza, Yusuf Shuaibu and Salim Sani Shehu
1 year ago
in Manyan Labarai
0
kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mummunan harin da ake kai wa fararen hula da sunan ‘kuskure’ a Nijeriya na dada daukar hankali, inda al’amura ke kara kamari a ‘yan shekarun nan. Tun a shekarar 2017 da aka rika samun aukuwar hakan a yankin arewa maso gabas, har yanzu ba a magnace ba inda ko a baya-bayan nan, akalla fararen hula 40 aka kashe a garin Mutumji da ke karamar hukumar Maru a Jihar Zamfara.

A wannan makon Nijeriya ta tsunduma cikin alhini yayin da akalla fararen hula 85 suka rasu bayan wani jirgin yakin sojoji mara matuki ya jefa bom a kauyen Tudun Biri da ke yankin Rigasa a Jihar Kaduna, yayin da al’ummar Musulmi suke gudanar da taron Maulidin Annabi Muhammad (SAW).

  • An Kaddamar Da Cibiyar Buga Muhimman Takardu Ta AU Da Sin Ta Ba Da Taimakon Ginawa
  • Jami’an NDLEA Sun Yi Artabu Da Miyagu A Jihar Edo

Baya ga wadanda suka rasu, akwai kimanin mutum 66 da suka jikkata a harin, kamar yadda hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa ta fitar a cikin wata sanarwa. Ya zuwa lokacin hada wannan rahoto an binne gawarwaki 85 da suka hada da yara da mata da tsoffi, yayin da ake ci gaba da neman karin wadanda abin ya shafa, in ji hukumar.
Domin neman ba’asin musabbabin wannan lamari, LEADERSHIP Hausa ta tattauna da wani kwararre kan harkokin tsaro a Nijeriya, Aliko Ibrahim El-Rasheed, wanda ya taba aiki a ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, kuma tsohon jami’in tsaro na sirri kana hafsan sojan sama.
A cikin shirin D Space (twitter), da LEADERSHIP Hausa ta gudanar ranar 5 ga Disamba, El-Rasheed ya bayyana rashin kyakkyawan tsari na tattara bayanai da aiki da su a sassan rundunonin tsaro daban-daban da suka hada da sojojin sama, da na kasa, da na ruwa, da ‘yansanda, da jami’an tsaron DSS, a matsayin babbar matsalar da ke haifar da ire-iren wadannan hare-hare a kan fararen hula.
Ya kawo misalign abin da ya faru a sansanin ‘yan gudun hijira na Rann a shekarar 2017, da ke iyaka da Nijeriya da Kamaru, inda aka yi asarar rayuka sama da 100, El-Rasheed ya sake bayyana irin wannan lamarin da ya faru Zamfara a watan Disambar 2022, da irin asarar rayukan da aka rasa sakamakon hare-haren bisa kuskure.
Kamar yadda El-Rasheed ya bayyana, matsalar ta ta’allaka ce da gazawar jami’an tsaron Nijeriya wajen samar da hadin gwiwa a tsakaninsu. Ya kuma jaddada bukatar sojoji da ‘yansanda da hukumomin leken asiri su rika musayar bayanai ta ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan tsaron kasa.
El-Rasheed ya kuma gano akwai wani babban gibi da ake samu a tsakanin jami’an tsaro da gwamnatocin jihohi wanda ya yi kiran magancewa, domin a cewarsa rashin hadin kai yana haifar da babban kalubale ga aiwatar da ingantattun shirye-shirye ko atisayen da aka tsara don hana irin wadannan abubuwan faruwa.
Yayin da yake kawo mafita kuwa, El-Rasheed ya zayyana muhimman abubuwa guda uku wanda ya kamata a kalla. Da farko, ya jaddada mahimmancin tabbatar da ingancin bayanai daga jami’an tsaro kafin a ba da izinin duk wani aiki ko atisaye.
Na biyu, ya jaddada bukatar inganta hanyoyin musayar bayanai a tsakanin dukkanin jami’an tsaron Nijeriya, da samar hadin gwiwa sosai da sosai a tsakaninsu.
A karshe El-Rasheed ya bukaci jama’a da su sanar da jami’an tsaro na kusa da su a lokacin gudanar da manyan tarukan al’umma, inda ya jaddada muhimmancin gudanar da taruka da rana kasancewar ana cikin yaki ne da ‘yan ta’adda, domin dakile sake faruwar lamarin.

…Muna Tattaunawa Da Gwamnatin Tarayya Kan Lamarin – Gwamna Uba Sani

Gwamna Jihar Kaduna, Malam Uba Sani ya bayyana cewa, a lokacin da abin ya faru a cikin dare ya nemi shugaban rundunar tsaron Nijeriya Janar Christoper Musa, wanda dan asalin Jihar Kaduna ne ya nuna masa bacin ransa ganin irin ibtila’in da aka samu na rasa rayuka masu yawa haka.

Labarai Masu Nasaba

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

Ya kuma bayyana cewa ya yi magana da Shugaban Kasa Bola Tinubu, “Muna nan muna daukar matakai, wadanda suke a asibiti, gwamnati za ta dauki nauyin yi musu magani, na kuma yi kiran cewa, lallai a yi bincike don sanin abin da ya kawo matsalar kuma duk wanda aka samu da laifi na kusukure a duba a gani in ganganci ne domin a dauki matakai saboda kar a sami irin wannan abin a nan gaba”.

Ya kuma ce, Sojoji ba a karkashin gamnatin jihar suke ba, mallakin gwamnatin tarayya ne, “Za mu jagorancin ganin an tabbatar da yin abin da ya kamata, amma wannan abu ne da ni kadai ba zan iya yanke hukunci ba dole sai mun zauna da shugaban kasar Nijeriya don sanin yadda za a fito wa batun biyan diyya, kuma na riga na yi masa bayani mun tattauna da shi, wajibi ne mu tsaya tsayin daka don kare rayuwar al’umma da dukiyoyinsu, za kuma mu tabbatar da ba jami’an tsarto dukkan hadin kan da suke bukata don samun nasarar yakar ‘yan ta’adda.
“Tuni muka fara taimakawa wadanda suka jikkata a asibiti da kuma iyalan wadanda suka rasu, ba mu jira agaji daga gwamnatin tarayya ba.” In ji shi.

…Ansariddeen Attajjaniyya Ta Gabatar Da Bukatu 5

Kungiyar Jam’iyyatu Ansariddeen Attijjaniyya ta lissafa wasu abubuwa guda biyar da take neman gwamnatin tarayya ta aiwatar bisa kisan kiyashi da jirgin sojojin Nijeriya ya yi wa masu bikin maulidi a kauyen Tudun Biri da ke Jihar Kaduna.

Kungiyar ta bayyana abubuwan ne a wani taron ‘yan jarida da ta kira a shalkwatarta da ke Abuja.
Cikina abubuwan da kungiyar ta nemi gwamnatin tarayya ta yi sun hada da gudanar da cikakken bincike cikin gaggawa kan tare da sabunta bayanai ga al’umma, saboda tabbatar da adalci.
Haka kuma kungiyar ta ce dole ne a karfafa ka’idojin aiki a tsakanin sojojin Nijeriya, musamman ma na tura jiragen marasa matuKi.

Har ila yau, kungiyar ta bukaci a horar da sojoji sanin ‘yancin Dan’adam da kuma kare rayukan fararen hula tare da jaddada tausayawa da mutunta bambance-bambance da kuma fahimtar al’adu, wanda hakan na iya taimakawa wajen hana sake afkuwan wannan lamari.
Ta kuma yi kira da a samar da hadin kan a tsakanin sojoji da kuma al’umma.
Daga karshe, kungiyar ta nemi gwamnatin tartayya ta biya diyyar rayukan da aka salwantar ga iyalan wadanda lamarin ya shafa. Ta ce dole ne a tallafa wa rayuwar iyalan da suka rasa ‘yan’uwansu da kudade, domin sake rayuwarsu.

Da yake karin bayani, Babban Sakataren Kungiyar na Kasa, Alhaji Alkasim Yahaya ya bayyana cewa, “Muna mika ta’aziyyarmu ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu a wannan mummunan lamari. Babu wata magana da za ta iya rage radadin da suke ciki, amma za mu ci gaba da yin addu’o’i a gare ku.

“Muna bakin cikin yadda wannan musiba ta faru a daidai lokacin da al’umma ke bikin murnar zagayowar haihuwar Annabi Muhammadu (SAW) cikin lumana. Muna kira da rundunar sojin Nijeriya ta gudanar da sahihin bincike kan lamari tare da daukan mataki ga duk wadanda aka samu da hannnu a ciki.
“A matsayinmu na kungiya, muna bukata a nuna gaskiya da rikon amana wajen hukunta wadanda suka aikata wannan kisan kiyashi. Mun san cewa babu wanda ya fi karfin doka, dole ne a hukunta wadanda suka aikata wannan ta’asa ga mabiyanmu ba tare da la’akari da matsayinsu ba,” in ji shi.

Kungiyar ta ce aikata wannan mummunan lamari ba karamin laifi ba ne na take hakkin Dan’adam, musamman a lokacin bikin zagayowar haihuwar Annabi (SAW) da masoya ‘yan Tijjaniyya ke yi duk shekara. Sannan kuma ta yi kira da rundunar sojin Nijeriya da gwamnatin tarayya da su gaggauta daukar mataki cikin gaggawa tare yin amfani da wadannan sharudda.

Ta ce a shirye take ta ba da goyon baya da hadin kai ga masu ruwa da tsaki domin kawo sauyi mai ma’ana da kwanciyar hankali a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin Kadunajirgin yakin NAFTudun Biri
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Yaɗa Labarai Ya Kafa Kwamitin Tsara Cusa Ɗa’a Da Kishin Ƙasa

Next Post

Hajjin 2024: NAHCON Za Ta Sabunta Ka’idojin Ciyar Da Alhazai Da Masaukansu

Related

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

51 minutes ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

2 hours ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

10 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

16 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

21 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

1 day ago
Next Post
NAHCON

Hajjin 2024: NAHCON Za Ta Sabunta Ka'idojin Ciyar Da Alhazai Da Masaukansu

LABARAI MASU NASABA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.