• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Da Ta Haddasa Harin Bom Na Kaduna

by Bello Hamza, Yusuf Shuaibu and Salim Sani Shehu
2 years ago
in Manyan Labarai
0
kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mummunan harin da ake kai wa fararen hula da sunan ‘kuskure’ a Nijeriya na dada daukar hankali, inda al’amura ke kara kamari a ‘yan shekarun nan. Tun a shekarar 2017 da aka rika samun aukuwar hakan a yankin arewa maso gabas, har yanzu ba a magnace ba inda ko a baya-bayan nan, akalla fararen hula 40 aka kashe a garin Mutumji da ke karamar hukumar Maru a Jihar Zamfara.

A wannan makon Nijeriya ta tsunduma cikin alhini yayin da akalla fararen hula 85 suka rasu bayan wani jirgin yakin sojoji mara matuki ya jefa bom a kauyen Tudun Biri da ke yankin Rigasa a Jihar Kaduna, yayin da al’ummar Musulmi suke gudanar da taron Maulidin Annabi Muhammad (SAW).

  • An Kaddamar Da Cibiyar Buga Muhimman Takardu Ta AU Da Sin Ta Ba Da Taimakon Ginawa
  • Jami’an NDLEA Sun Yi Artabu Da Miyagu A Jihar Edo

Baya ga wadanda suka rasu, akwai kimanin mutum 66 da suka jikkata a harin, kamar yadda hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa ta fitar a cikin wata sanarwa. Ya zuwa lokacin hada wannan rahoto an binne gawarwaki 85 da suka hada da yara da mata da tsoffi, yayin da ake ci gaba da neman karin wadanda abin ya shafa, in ji hukumar.
Domin neman ba’asin musabbabin wannan lamari, LEADERSHIP Hausa ta tattauna da wani kwararre kan harkokin tsaro a Nijeriya, Aliko Ibrahim El-Rasheed, wanda ya taba aiki a ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, kuma tsohon jami’in tsaro na sirri kana hafsan sojan sama.
A cikin shirin D Space (twitter), da LEADERSHIP Hausa ta gudanar ranar 5 ga Disamba, El-Rasheed ya bayyana rashin kyakkyawan tsari na tattara bayanai da aiki da su a sassan rundunonin tsaro daban-daban da suka hada da sojojin sama, da na kasa, da na ruwa, da ‘yansanda, da jami’an tsaron DSS, a matsayin babbar matsalar da ke haifar da ire-iren wadannan hare-hare a kan fararen hula.
Ya kawo misalign abin da ya faru a sansanin ‘yan gudun hijira na Rann a shekarar 2017, da ke iyaka da Nijeriya da Kamaru, inda aka yi asarar rayuka sama da 100, El-Rasheed ya sake bayyana irin wannan lamarin da ya faru Zamfara a watan Disambar 2022, da irin asarar rayukan da aka rasa sakamakon hare-haren bisa kuskure.
Kamar yadda El-Rasheed ya bayyana, matsalar ta ta’allaka ce da gazawar jami’an tsaron Nijeriya wajen samar da hadin gwiwa a tsakaninsu. Ya kuma jaddada bukatar sojoji da ‘yansanda da hukumomin leken asiri su rika musayar bayanai ta ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan tsaron kasa.
El-Rasheed ya kuma gano akwai wani babban gibi da ake samu a tsakanin jami’an tsaro da gwamnatocin jihohi wanda ya yi kiran magancewa, domin a cewarsa rashin hadin kai yana haifar da babban kalubale ga aiwatar da ingantattun shirye-shirye ko atisayen da aka tsara don hana irin wadannan abubuwan faruwa.
Yayin da yake kawo mafita kuwa, El-Rasheed ya zayyana muhimman abubuwa guda uku wanda ya kamata a kalla. Da farko, ya jaddada mahimmancin tabbatar da ingancin bayanai daga jami’an tsaro kafin a ba da izinin duk wani aiki ko atisaye.
Na biyu, ya jaddada bukatar inganta hanyoyin musayar bayanai a tsakanin dukkanin jami’an tsaron Nijeriya, da samar hadin gwiwa sosai da sosai a tsakaninsu.
A karshe El-Rasheed ya bukaci jama’a da su sanar da jami’an tsaro na kusa da su a lokacin gudanar da manyan tarukan al’umma, inda ya jaddada muhimmancin gudanar da taruka da rana kasancewar ana cikin yaki ne da ‘yan ta’adda, domin dakile sake faruwar lamarin.

…Muna Tattaunawa Da Gwamnatin Tarayya Kan Lamarin – Gwamna Uba Sani

Gwamna Jihar Kaduna, Malam Uba Sani ya bayyana cewa, a lokacin da abin ya faru a cikin dare ya nemi shugaban rundunar tsaron Nijeriya Janar Christoper Musa, wanda dan asalin Jihar Kaduna ne ya nuna masa bacin ransa ganin irin ibtila’in da aka samu na rasa rayuka masu yawa haka.

Labarai Masu Nasaba

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Ya kuma bayyana cewa ya yi magana da Shugaban Kasa Bola Tinubu, “Muna nan muna daukar matakai, wadanda suke a asibiti, gwamnati za ta dauki nauyin yi musu magani, na kuma yi kiran cewa, lallai a yi bincike don sanin abin da ya kawo matsalar kuma duk wanda aka samu da laifi na kusukure a duba a gani in ganganci ne domin a dauki matakai saboda kar a sami irin wannan abin a nan gaba”.

Ya kuma ce, Sojoji ba a karkashin gamnatin jihar suke ba, mallakin gwamnatin tarayya ne, “Za mu jagorancin ganin an tabbatar da yin abin da ya kamata, amma wannan abu ne da ni kadai ba zan iya yanke hukunci ba dole sai mun zauna da shugaban kasar Nijeriya don sanin yadda za a fito wa batun biyan diyya, kuma na riga na yi masa bayani mun tattauna da shi, wajibi ne mu tsaya tsayin daka don kare rayuwar al’umma da dukiyoyinsu, za kuma mu tabbatar da ba jami’an tsarto dukkan hadin kan da suke bukata don samun nasarar yakar ‘yan ta’adda.
“Tuni muka fara taimakawa wadanda suka jikkata a asibiti da kuma iyalan wadanda suka rasu, ba mu jira agaji daga gwamnatin tarayya ba.” In ji shi.

…Ansariddeen Attajjaniyya Ta Gabatar Da Bukatu 5

Kungiyar Jam’iyyatu Ansariddeen Attijjaniyya ta lissafa wasu abubuwa guda biyar da take neman gwamnatin tarayya ta aiwatar bisa kisan kiyashi da jirgin sojojin Nijeriya ya yi wa masu bikin maulidi a kauyen Tudun Biri da ke Jihar Kaduna.

Kungiyar ta bayyana abubuwan ne a wani taron ‘yan jarida da ta kira a shalkwatarta da ke Abuja.
Cikina abubuwan da kungiyar ta nemi gwamnatin tarayya ta yi sun hada da gudanar da cikakken bincike cikin gaggawa kan tare da sabunta bayanai ga al’umma, saboda tabbatar da adalci.
Haka kuma kungiyar ta ce dole ne a karfafa ka’idojin aiki a tsakanin sojojin Nijeriya, musamman ma na tura jiragen marasa matuKi.

Har ila yau, kungiyar ta bukaci a horar da sojoji sanin ‘yancin Dan’adam da kuma kare rayukan fararen hula tare da jaddada tausayawa da mutunta bambance-bambance da kuma fahimtar al’adu, wanda hakan na iya taimakawa wajen hana sake afkuwan wannan lamari.
Ta kuma yi kira da a samar da hadin kan a tsakanin sojoji da kuma al’umma.
Daga karshe, kungiyar ta nemi gwamnatin tartayya ta biya diyyar rayukan da aka salwantar ga iyalan wadanda lamarin ya shafa. Ta ce dole ne a tallafa wa rayuwar iyalan da suka rasa ‘yan’uwansu da kudade, domin sake rayuwarsu.

Da yake karin bayani, Babban Sakataren Kungiyar na Kasa, Alhaji Alkasim Yahaya ya bayyana cewa, “Muna mika ta’aziyyarmu ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu a wannan mummunan lamari. Babu wata magana da za ta iya rage radadin da suke ciki, amma za mu ci gaba da yin addu’o’i a gare ku.

“Muna bakin cikin yadda wannan musiba ta faru a daidai lokacin da al’umma ke bikin murnar zagayowar haihuwar Annabi Muhammadu (SAW) cikin lumana. Muna kira da rundunar sojin Nijeriya ta gudanar da sahihin bincike kan lamari tare da daukan mataki ga duk wadanda aka samu da hannnu a ciki.
“A matsayinmu na kungiya, muna bukata a nuna gaskiya da rikon amana wajen hukunta wadanda suka aikata wannan kisan kiyashi. Mun san cewa babu wanda ya fi karfin doka, dole ne a hukunta wadanda suka aikata wannan ta’asa ga mabiyanmu ba tare da la’akari da matsayinsu ba,” in ji shi.

Kungiyar ta ce aikata wannan mummunan lamari ba karamin laifi ba ne na take hakkin Dan’adam, musamman a lokacin bikin zagayowar haihuwar Annabi (SAW) da masoya ‘yan Tijjaniyya ke yi duk shekara. Sannan kuma ta yi kira da rundunar sojin Nijeriya da gwamnatin tarayya da su gaggauta daukar mataki cikin gaggawa tare yin amfani da wadannan sharudda.

Ta ce a shirye take ta ba da goyon baya da hadin kai ga masu ruwa da tsaki domin kawo sauyi mai ma’ana da kwanciyar hankali a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin Kadunajirgin yakin NAFTudun Biri
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Yaɗa Labarai Ya Kafa Kwamitin Tsara Cusa Ɗa’a Da Kishin Ƙasa

Next Post

Hajjin 2024: NAHCON Za Ta Sabunta Ka’idojin Ciyar Da Alhazai Da Masaukansu

Related

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

32 minutes ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

17 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

22 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

23 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

1 day ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

2 days ago
Next Post
NAHCON

Hajjin 2024: NAHCON Za Ta Sabunta Ka'idojin Ciyar Da Alhazai Da Masaukansu

LABARAI MASU NASABA

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.