ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’an NDLEA Sun Yi Artabu Da Miyagu A Jihar Edo

Jami’ai Uku sun samu rauni, an cire wa daya harsashi a kwakwalwa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
NDLEA

Jami’an hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) sun yi artabu da miyagu wadanda suka zagaye su tare da dakile dukkan hanyoyin fita a kauyen Opuje da ke Karamar Hukumar Owan ta Yamma a Jihar Edo yayin da jami’an suka kai sumame kan gidajen ajiya da aka cika makil da tan-tan na miyagun kwayoyi. 

Miyagun bayan bude wuta, sun raunata mutane uku, inda daya daga ciki harsashi ta same shi a kwakwalwa.

  • Iwobi Ya Jefa Kwallo 2 Yayin Da Fulham Ta Lallasa Forest Da Ci 5-0
  • Kotu Ta Yi Wa Dan Fashi Daurin Rai Da Rai A Zamfara

Wannan yana zuwa ne watanni 11 bayan da gungun matasa dauke da muggan makamai da ke yi wa masu safarar miyagun kwayoyi aiki suka far wa jami’an hukumar da suka kawo sumame kauyen don lalata tantunan ajiya wadanda aka boye sama da kiligiram 317,417 na wiwi.

ADVERTISEMENT

Zuwa yanzu dai an samu kama mutane uku: Omoruan Theophilus mai shekaru 37; Aigberuan Jacob mai shekaru 42 da kuma Ekeinde Anthony Zaza mai shekaru 53.

Kauyen na Opuje yayi kaurin suna wajen noman ganyen wiwi, inda masu safarar miyagun kwayoyi suka dade suna zuba hannun jari a ciki tare da lalata bishiyoyi don samun manyan gonakin wiwi na kadadodi daruruwa.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Bayan girbe haramtaccen ganyen, sukan gina manyan gidajen ajiya a cikin dajin sannan su dauki matasa su ba su muggan makamai don tsaron gidan ba kakkautawa.

Biyo bayan bayanan sirri cewa masu safarar miyagun kwayoyin sun cika gidajen ajiyan su a dajin saboda dillanci a bukukuwan karshen shekara, hukumar NDLEA ta shirya zaratan jami’ai saboda kai sumame dajin don dakile dillancin da kuma lalata gidajen ajiyan miyagun kwayoyin.

A yayin hakan ne aka lalata gidan ajiya da ke dauke da kilogiram 6,000 na wiwi a Ujiogba dake Karamar Hukumar Esan ta yamma a makon da ta gabata.

To amma a yayin wannan aikin, zaratan jami’an na hukumar sun tsinci kansu cikin matsanancin musayar wuta da miyagu a safiyar Litinin 4 ga watan Disamba a yayin da suka nufi dajin Opuje inda suka dakile dukkan hanyoyi don hana jami’an NDLEA fita.

Amma jami’an bayan sun dauki awanni biyu suna ba ta kashi, sun samu nasarar fita daga dajin.

Sai dai kafin jami’an su fita, ‘yan bindigan sun raunata jami’ai uku, inda daya daga ciki harasashi ta same shi har cikin kwakwalwa, inda motocin jami’an suka samu illa matuka daga harasasai.

Jami’an da suka samu raunin an garzaya da su nan take zuwa asibiti, inda shi kuma wanda ya samu rauni a kwakwalwa aka yi masa tiyata aka cire harsashin daga cikin kwakwalwarsa a jiya Laraba 6 ga watan Satumba.

A yayin da yake martani dangane da harin da aka kai wa jami’an, shugaban hukumar NDLEA, Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya) ya yi gargadin cewa wadanda suke daukar nauyin kai hari kan jami’ai a bakin aiki ba za su taba samun aminci ba, kuma komai dadewa za su girbi abin da suka shuka kamar yanda doka ta tanadar.

Kazalika, Marwa ya jinjina wa jami’an da suka kai sumamen, inda ya ce ko kadan, hare-haren miyagu ba zai sa kasa a guiwar hukumar ko ya hana ta dakile dillalan miyagun kwayoyi daga lalata al’umma a kasar nan ba.

NDLEA
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Gwamnan Sakkwato Zai Saya Wa Kansa Motocin Biliyan Daya

Gwamnan Sakkwato Zai Saya Wa Kansa Motocin Biliyan Daya

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.