ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’an NDLEA Sun Yi Artabu Da Miyagu A Jihar Edo

Jami’ai Uku sun samu rauni, an cire wa daya harsashi a kwakwalwa

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
NDLEA

Jami’an hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) sun yi artabu da miyagu wadanda suka zagaye su tare da dakile dukkan hanyoyin fita a kauyen Opuje da ke Karamar Hukumar Owan ta Yamma a Jihar Edo yayin da jami’an suka kai sumame kan gidajen ajiya da aka cika makil da tan-tan na miyagun kwayoyi. 

Miyagun bayan bude wuta, sun raunata mutane uku, inda daya daga ciki harsashi ta same shi a kwakwalwa.

  • Iwobi Ya Jefa Kwallo 2 Yayin Da Fulham Ta Lallasa Forest Da Ci 5-0
  • Kotu Ta Yi Wa Dan Fashi Daurin Rai Da Rai A Zamfara

Wannan yana zuwa ne watanni 11 bayan da gungun matasa dauke da muggan makamai da ke yi wa masu safarar miyagun kwayoyi aiki suka far wa jami’an hukumar da suka kawo sumame kauyen don lalata tantunan ajiya wadanda aka boye sama da kiligiram 317,417 na wiwi.

ADVERTISEMENT

Zuwa yanzu dai an samu kama mutane uku: Omoruan Theophilus mai shekaru 37; Aigberuan Jacob mai shekaru 42 da kuma Ekeinde Anthony Zaza mai shekaru 53.

Kauyen na Opuje yayi kaurin suna wajen noman ganyen wiwi, inda masu safarar miyagun kwayoyi suka dade suna zuba hannun jari a ciki tare da lalata bishiyoyi don samun manyan gonakin wiwi na kadadodi daruruwa.

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Bayan girbe haramtaccen ganyen, sukan gina manyan gidajen ajiya a cikin dajin sannan su dauki matasa su ba su muggan makamai don tsaron gidan ba kakkautawa.

Biyo bayan bayanan sirri cewa masu safarar miyagun kwayoyin sun cika gidajen ajiyan su a dajin saboda dillanci a bukukuwan karshen shekara, hukumar NDLEA ta shirya zaratan jami’ai saboda kai sumame dajin don dakile dillancin da kuma lalata gidajen ajiyan miyagun kwayoyin.

A yayin hakan ne aka lalata gidan ajiya da ke dauke da kilogiram 6,000 na wiwi a Ujiogba dake Karamar Hukumar Esan ta yamma a makon da ta gabata.

To amma a yayin wannan aikin, zaratan jami’an na hukumar sun tsinci kansu cikin matsanancin musayar wuta da miyagu a safiyar Litinin 4 ga watan Disamba a yayin da suka nufi dajin Opuje inda suka dakile dukkan hanyoyi don hana jami’an NDLEA fita.

Amma jami’an bayan sun dauki awanni biyu suna ba ta kashi, sun samu nasarar fita daga dajin.

Sai dai kafin jami’an su fita, ‘yan bindigan sun raunata jami’ai uku, inda daya daga ciki harasashi ta same shi har cikin kwakwalwa, inda motocin jami’an suka samu illa matuka daga harasasai.

Jami’an da suka samu raunin an garzaya da su nan take zuwa asibiti, inda shi kuma wanda ya samu rauni a kwakwalwa aka yi masa tiyata aka cire harsashin daga cikin kwakwalwarsa a jiya Laraba 6 ga watan Satumba.

A yayin da yake martani dangane da harin da aka kai wa jami’an, shugaban hukumar NDLEA, Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya) ya yi gargadin cewa wadanda suke daukar nauyin kai hari kan jami’ai a bakin aiki ba za su taba samun aminci ba, kuma komai dadewa za su girbi abin da suka shuka kamar yanda doka ta tanadar.

Kazalika, Marwa ya jinjina wa jami’an da suka kai sumamen, inda ya ce ko kadan, hare-haren miyagu ba zai sa kasa a guiwar hukumar ko ya hana ta dakile dillalan miyagun kwayoyi daga lalata al’umma a kasar nan ba.

NDLEA
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Next Post
Gwamnan Sakkwato Zai Saya Wa Kansa Motocin Biliyan Daya

Gwamnan Sakkwato Zai Saya Wa Kansa Motocin Biliyan Daya

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.