ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’an NDLEA Sun Yi Artabu Da Miyagu A Jihar Edo

Jami’ai Uku sun samu rauni, an cire wa daya harsashi a kwakwalwa

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
NDLEA

Jami’an hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) sun yi artabu da miyagu wadanda suka zagaye su tare da dakile dukkan hanyoyin fita a kauyen Opuje da ke Karamar Hukumar Owan ta Yamma a Jihar Edo yayin da jami’an suka kai sumame kan gidajen ajiya da aka cika makil da tan-tan na miyagun kwayoyi. 

Miyagun bayan bude wuta, sun raunata mutane uku, inda daya daga ciki harsashi ta same shi a kwakwalwa.

  • Iwobi Ya Jefa Kwallo 2 Yayin Da Fulham Ta Lallasa Forest Da Ci 5-0
  • Kotu Ta Yi Wa Dan Fashi Daurin Rai Da Rai A Zamfara

Wannan yana zuwa ne watanni 11 bayan da gungun matasa dauke da muggan makamai da ke yi wa masu safarar miyagun kwayoyi aiki suka far wa jami’an hukumar da suka kawo sumame kauyen don lalata tantunan ajiya wadanda aka boye sama da kiligiram 317,417 na wiwi.

ADVERTISEMENT

Zuwa yanzu dai an samu kama mutane uku: Omoruan Theophilus mai shekaru 37; Aigberuan Jacob mai shekaru 42 da kuma Ekeinde Anthony Zaza mai shekaru 53.

Kauyen na Opuje yayi kaurin suna wajen noman ganyen wiwi, inda masu safarar miyagun kwayoyi suka dade suna zuba hannun jari a ciki tare da lalata bishiyoyi don samun manyan gonakin wiwi na kadadodi daruruwa.

LABARAI MASU NASABA

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Bayan girbe haramtaccen ganyen, sukan gina manyan gidajen ajiya a cikin dajin sannan su dauki matasa su ba su muggan makamai don tsaron gidan ba kakkautawa.

Biyo bayan bayanan sirri cewa masu safarar miyagun kwayoyin sun cika gidajen ajiyan su a dajin saboda dillanci a bukukuwan karshen shekara, hukumar NDLEA ta shirya zaratan jami’ai saboda kai sumame dajin don dakile dillancin da kuma lalata gidajen ajiyan miyagun kwayoyin.

A yayin hakan ne aka lalata gidan ajiya da ke dauke da kilogiram 6,000 na wiwi a Ujiogba dake Karamar Hukumar Esan ta yamma a makon da ta gabata.

To amma a yayin wannan aikin, zaratan jami’an na hukumar sun tsinci kansu cikin matsanancin musayar wuta da miyagu a safiyar Litinin 4 ga watan Disamba a yayin da suka nufi dajin Opuje inda suka dakile dukkan hanyoyi don hana jami’an NDLEA fita.

Amma jami’an bayan sun dauki awanni biyu suna ba ta kashi, sun samu nasarar fita daga dajin.

Sai dai kafin jami’an su fita, ‘yan bindigan sun raunata jami’ai uku, inda daya daga ciki harasashi ta same shi har cikin kwakwalwa, inda motocin jami’an suka samu illa matuka daga harasasai.

Jami’an da suka samu raunin an garzaya da su nan take zuwa asibiti, inda shi kuma wanda ya samu rauni a kwakwalwa aka yi masa tiyata aka cire harsashin daga cikin kwakwalwarsa a jiya Laraba 6 ga watan Satumba.

A yayin da yake martani dangane da harin da aka kai wa jami’an, shugaban hukumar NDLEA, Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya) ya yi gargadin cewa wadanda suke daukar nauyin kai hari kan jami’ai a bakin aiki ba za su taba samun aminci ba, kuma komai dadewa za su girbi abin da suka shuka kamar yanda doka ta tanadar.

Kazalika, Marwa ya jinjina wa jami’an da suka kai sumamen, inda ya ce ko kadan, hare-haren miyagu ba zai sa kasa a guiwar hukumar ko ya hana ta dakile dillalan miyagun kwayoyi daga lalata al’umma a kasar nan ba.

NDLEA
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Gwamnan Sakkwato Zai Saya Wa Kansa Motocin Biliyan Daya

Gwamnan Sakkwato Zai Saya Wa Kansa Motocin Biliyan Daya

LABARAI MASU NASABA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.