• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’an NDLEA Sun Yi Artabu Da Miyagu A Jihar Edo

Jami’ai Uku sun samu rauni, an cire wa daya harsashi a kwakwalwa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Jami’an NDLEA Sun Yi Artabu Da Miyagu A Jihar Edo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) sun yi artabu da miyagu wadanda suka zagaye su tare da dakile dukkan hanyoyin fita a kauyen Opuje da ke Karamar Hukumar Owan ta Yamma a Jihar Edo yayin da jami’an suka kai sumame kan gidajen ajiya da aka cika makil da tan-tan na miyagun kwayoyi. 

Miyagun bayan bude wuta, sun raunata mutane uku, inda daya daga ciki harsashi ta same shi a kwakwalwa.

  • Iwobi Ya Jefa Kwallo 2 Yayin Da Fulham Ta Lallasa Forest Da Ci 5-0
  • Kotu Ta Yi Wa Dan Fashi Daurin Rai Da Rai A Zamfara

Wannan yana zuwa ne watanni 11 bayan da gungun matasa dauke da muggan makamai da ke yi wa masu safarar miyagun kwayoyi aiki suka far wa jami’an hukumar da suka kawo sumame kauyen don lalata tantunan ajiya wadanda aka boye sama da kiligiram 317,417 na wiwi.

Zuwa yanzu dai an samu kama mutane uku: Omoruan Theophilus mai shekaru 37; Aigberuan Jacob mai shekaru 42 da kuma Ekeinde Anthony Zaza mai shekaru 53.

Kauyen na Opuje yayi kaurin suna wajen noman ganyen wiwi, inda masu safarar miyagun kwayoyi suka dade suna zuba hannun jari a ciki tare da lalata bishiyoyi don samun manyan gonakin wiwi na kadadodi daruruwa.

Labarai Masu Nasaba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

Bayan girbe haramtaccen ganyen, sukan gina manyan gidajen ajiya a cikin dajin sannan su dauki matasa su ba su muggan makamai don tsaron gidan ba kakkautawa.

Biyo bayan bayanan sirri cewa masu safarar miyagun kwayoyin sun cika gidajen ajiyan su a dajin saboda dillanci a bukukuwan karshen shekara, hukumar NDLEA ta shirya zaratan jami’ai saboda kai sumame dajin don dakile dillancin da kuma lalata gidajen ajiyan miyagun kwayoyin.

A yayin hakan ne aka lalata gidan ajiya da ke dauke da kilogiram 6,000 na wiwi a Ujiogba dake Karamar Hukumar Esan ta yamma a makon da ta gabata.

To amma a yayin wannan aikin, zaratan jami’an na hukumar sun tsinci kansu cikin matsanancin musayar wuta da miyagu a safiyar Litinin 4 ga watan Disamba a yayin da suka nufi dajin Opuje inda suka dakile dukkan hanyoyi don hana jami’an NDLEA fita.

Amma jami’an bayan sun dauki awanni biyu suna ba ta kashi, sun samu nasarar fita daga dajin.

Sai dai kafin jami’an su fita, ‘yan bindigan sun raunata jami’ai uku, inda daya daga ciki harasashi ta same shi har cikin kwakwalwa, inda motocin jami’an suka samu illa matuka daga harasasai.

Jami’an da suka samu raunin an garzaya da su nan take zuwa asibiti, inda shi kuma wanda ya samu rauni a kwakwalwa aka yi masa tiyata aka cire harsashin daga cikin kwakwalwarsa a jiya Laraba 6 ga watan Satumba.

A yayin da yake martani dangane da harin da aka kai wa jami’an, shugaban hukumar NDLEA, Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya) ya yi gargadin cewa wadanda suke daukar nauyin kai hari kan jami’ai a bakin aiki ba za su taba samun aminci ba, kuma komai dadewa za su girbi abin da suka shuka kamar yanda doka ta tanadar.

Kazalika, Marwa ya jinjina wa jami’an da suka kai sumamen, inda ya ce ko kadan, hare-haren miyagu ba zai sa kasa a guiwar hukumar ko ya hana ta dakile dillalan miyagun kwayoyi daga lalata al’umma a kasar nan ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Iwobi Ya Jefa Kwallo 2 Yayin Da Fulham Ta Lallasa Forest Da Ci 5-0

Next Post

Gwamnan Sakkwato Zai Saya Wa Kansa Motocin Biliyan Daya

Related

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

12 hours ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

12 hours ago
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa
Labarai

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

14 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

15 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

16 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

17 hours ago
Next Post
Gwamnan Sakkwato Zai Saya Wa Kansa Motocin Biliyan Daya

Gwamnan Sakkwato Zai Saya Wa Kansa Motocin Biliyan Daya

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.