• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Nijeriya Ba Daga APC Ba Ce – Gwamna Uzodimma

bySulaiman and Yusuf Shuaibu
1 year ago
APC

Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma ya bayyana cewa jam’iyya mai mulki ta APC ta yi iya bakin kokarinta wajen ciyar da kasar nan. Ya ce kalubalen tattalin arzikin da ake fuskanta a kasar nan duka a duniya ne.

Uzodimma, wanda shi ne shugaban kungiyar gwamnonin APC (PGF), ya bayyana haka a Abuja lokacin da ya jagoranci zababbun gwamnonin jam’iyyar APC a ziyarar da suka kai wa shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Ganduje, wanda yake jagorantar kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyya mai mulki.

  • 2027: A Kasar Da Babu Manufa Kadai Kwankwaso Zai Iya Zama Shugaban Kasa – APC
  • Jamus Ta Sanar Da Shirin Ficewar Dakarunta Daga Nijar

Gwamnan ya ce, “Gaskiyar magana ita ce, jam’iyyar APC ta yi kokari sosai a Nijeriya. Abin da ke faruwa a halin yanzu matsalar ce na tattalin arzikin duniya baki daya.

“Mu a Nijeriya karkashin jagorancinmu na Shugaban kasa, Bola Tinubu mun fitar da tsare-tsare don magance matsin tattalin arziki, idan aka yi la’akari da irin tattalin arzikin da yake ciki duba da irin yanayin da ya samu kansa. Ina da yakinin cewa nan ba da dadewa ba ‘yan Nijeriya za su dara.”

Dangane da damar da jam’iyyar take da shi na samun nasara a zaben gwamnonin Edo da Ondo duba da halin kuncin da kasar nan ke ciki, Uzodimma ya ce jam’iyyar APC ce ke rike da jihohi 20 cikin 30 na kasar nan, tare da shugabancin kasa, kuma idan har zabe abu ne wanda yake tattare da wayan jama’a, lallai masu rinjaye ne za su samu shugabanci.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

A nasa bangaren, Ganduje ya ce shugabannin jam’iyyar za su yi kokarin kulla kyakkyawar alaka da gwamnoni a karkashin tutar jam’iyyar APC.

Ya ce, “Babu shakka mun yi matukar farin ciki a yau da na samu labarin kuna zuwa. Don haka, ina ganin wannan wata ni’ima ce mai girma a gare mu. Saboda haka, mun yi farin ciki da wannan ziyara kuma muna da kwarin gwiwa a kanku.

“Za mu yi duk mai yiwuwa don ganin mun ci gaba da wanzar da kyautata alaka da gwamnoninmu a fadin kasar nan, kuma za mu taimaka wajen kare muradunsu wanda ko shakka babu su ma suna taimaka wa jam’iyyar, suna sa jam’iyyar ta yi kara armashi kamar yadda ya kamata.”

Uzodinma ya kasance tare da Gwamnan Jihar Kuros Riba, Bassey Out da Gwamnan Jihar Ondo, Lucky Aiyedatiwa da takwaransu na Jihar Ekiti, Abiodun Oyebanji a wurin wannan ziyara

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
manja

Lokaci Ya Yi Da Nijeriya Za Rika Fitar Da Manja Kasashen Waje - Kungiyar Dalibai

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version