• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Nijeriya Ba Daga APC Ba Ce – Gwamna Uzodimma

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
1 year ago
APC

Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma ya bayyana cewa jam’iyya mai mulki ta APC ta yi iya bakin kokarinta wajen ciyar da kasar nan. Ya ce kalubalen tattalin arzikin da ake fuskanta a kasar nan duka a duniya ne.

Uzodimma, wanda shi ne shugaban kungiyar gwamnonin APC (PGF), ya bayyana haka a Abuja lokacin da ya jagoranci zababbun gwamnonin jam’iyyar APC a ziyarar da suka kai wa shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Ganduje, wanda yake jagorantar kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyya mai mulki.

  • 2027: A Kasar Da Babu Manufa Kadai Kwankwaso Zai Iya Zama Shugaban Kasa – APC
  • Jamus Ta Sanar Da Shirin Ficewar Dakarunta Daga Nijar

Gwamnan ya ce, “Gaskiyar magana ita ce, jam’iyyar APC ta yi kokari sosai a Nijeriya. Abin da ke faruwa a halin yanzu matsalar ce na tattalin arzikin duniya baki daya.

“Mu a Nijeriya karkashin jagorancinmu na Shugaban kasa, Bola Tinubu mun fitar da tsare-tsare don magance matsin tattalin arziki, idan aka yi la’akari da irin tattalin arzikin da yake ciki duba da irin yanayin da ya samu kansa. Ina da yakinin cewa nan ba da dadewa ba ‘yan Nijeriya za su dara.”

Dangane da damar da jam’iyyar take da shi na samun nasara a zaben gwamnonin Edo da Ondo duba da halin kuncin da kasar nan ke ciki, Uzodimma ya ce jam’iyyar APC ce ke rike da jihohi 20 cikin 30 na kasar nan, tare da shugabancin kasa, kuma idan har zabe abu ne wanda yake tattare da wayan jama’a, lallai masu rinjaye ne za su samu shugabanci.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

A nasa bangaren, Ganduje ya ce shugabannin jam’iyyar za su yi kokarin kulla kyakkyawar alaka da gwamnoni a karkashin tutar jam’iyyar APC.

Ya ce, “Babu shakka mun yi matukar farin ciki a yau da na samu labarin kuna zuwa. Don haka, ina ganin wannan wata ni’ima ce mai girma a gare mu. Saboda haka, mun yi farin ciki da wannan ziyara kuma muna da kwarin gwiwa a kanku.

“Za mu yi duk mai yiwuwa don ganin mun ci gaba da wanzar da kyautata alaka da gwamnoninmu a fadin kasar nan, kuma za mu taimaka wajen kare muradunsu wanda ko shakka babu su ma suna taimaka wa jam’iyyar, suna sa jam’iyyar ta yi kara armashi kamar yadda ya kamata.”

Uzodinma ya kasance tare da Gwamnan Jihar Kuros Riba, Bassey Out da Gwamnan Jihar Ondo, Lucky Aiyedatiwa da takwaransu na Jihar Ekiti, Abiodun Oyebanji a wurin wannan ziyara

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
manja

Lokaci Ya Yi Da Nijeriya Za Rika Fitar Da Manja Kasashen Waje - Kungiyar Dalibai

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.