• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalolin Da Za Su Dabaibaye Harkokin Masana’antu A 2024

by Bello Hamza
1 year ago
in Tattalin Arziki
0
Matsalolin Da Za Su Dabaibaye Harkokin Masana’antu A 2024
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da muke shiga sabuwar shekara 2024, harkokin kasuwanci na fuskantar manyan matsaloli da barazanar da za su bayar da gudummamwar durkusherwar su da hana su walwala.

Shugaban kungiyar masu masana’antu ta kasa, (MAN), Segun Ajayi-Kadir, ya yi hasashen cewa, shekarar 2024 za ta zo da manyan kalubale ga masu masana’antu saboda alamu sun nuna babu kyakyawar fata musamman a cikin watanni 6 na farkon shekarar.

  • Jihar Kaduna Za Ta Ƙarfafa Ƙawancen Tattalin Arziki Da Ƙasar Jamus
  • ‘Yansanda Sun Cafke Wasu Mutane Biyu Da Ake Zargi Da Satar Keke-napep A Kano

Nazari ya nuna cewa, matsalolin za su addabi kanana da manyan masana’natu wadanda za su taso daga harkokin tattalin arziki na ciki da wajen Nijeriya.

Musamman ma kungiyar MAN ta bayyana cewa, za a samu nakasu a bunkasar masana’antu daga kashi 2.4 a shekarar 2021 zuwa kashi 0.48 a zango na uku na shekarar 2023.

Ana iya ganin irin wannan ci bayan a manyan kamfanonin kasashe irin su Chana da Amurka, Nijeriya kuma ba za ta iya kare kanta daga wadannan abubuwan ba.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

Yana da matukar muhimmanci a fahimci cewa, matsalolin cikin gida kama daga karyewar darajar Naira da tashin kudin ruwa suna kawo cikas ga bunkasar kamfanonin kasuwanci da kashi 50 a cikin dai.

Za kuma a iya tuna manyan kamfanoni 6 da suka fice daga Nijeriya a cikin wata shida da suka wuce, wadanda suka hada da kamfanin samar da abinci na ‘Procter & Gamble’, Unileber, GladoSmithKline Consumer Nigeria Plc, Sanofi, French pharmaceutical multinational, Bolt Food da kuma kamfanin hada allura na ‘Jubilee Syringe Manufacturing’.

A ra’ayinmu, tsare-tsaren Babban Bankin Nijeriya CBN a ‘yan shekarun nan bai taimaka ba wajen zaburar da bunkasar kamfanoni da tattalin arzikin Nijeriya ba.

Masu harkokin fitar da kayyakin da ake sarrafawa a Nijeriya suna fuskanta rashin tabbas, basu da damar samun kudaden kasashen waje don gudanar da harkokin kasuwancinsu wanda haka ya taimaka wajen durkushewarsu.

Wani abin takaicin kuma shi ne tsaretsaren da aka samar don dakile hauhawar farashi ya taimaka ne kawai weajen takura kanana da mastaikaitun kamfanoni a fadin tarayyar kasar nan.

A irin wannan yanayin harkokin kasuwanci ba za su samu kwarin gwiwar ci gaba ba, kamar yadda kungiyar masu masana’antu ta zayyana a wani taron shugabannin kamfanoni da aka yi kwanakin baya ta yi.

Kungiyar ta yi hasashen wadannan kalubalen za su ta’azzara har zuwa zango na biyu na sabuwar shekara 2024, ana kuma iya samun farfadowa dan kadan daga baya. A hasashen nasu bangaren masana’antu zai samu bunkasar kasa da kashi 3.2 a wannan shdekarar, yayin da gudumawar bangaren ga tattalin arzikin kasa zai gaza kashi 10.

In har ana son kauce wa fadawa wadannan mastalolin dole a canza tsare-tsaren tattalin arzikin kasa ta yadda zai taimakawa bunkasar harkokin kasuwanci a Nijeriya. Muna bayar da shawara ga Babban Bankin Nijeriya ya bar matsayin harkokin kasuwanci ta nema wa naira daraja, a kuma dawo da ba masu masana’antu muhimmanci a wajen bayar da kudaden kasashen waje. Ya kuma kamata a rage ruwan da ake dorawa basukan da ake ba masu kanana da manyan masana’antu, hakan zai kara jawo masu zuba jari na ciki daga kasashen waje.

Samar da ingantaccen wutar lantarki, ta hanyar sake yi wa sashin garambawul zai matukar taimakawa zai kuma karfafa bunkasar masana’antunmu a cikin wannan shekarar.

Haka kuma ya kamata gwamnatin shugaba Tinubu ta ta tabbatar da an aiwatar da tanade tanaden da ke cikin kasafin kudin 2024 musamman bagarorin da suka nemi ba masu masana’antu tallafin kudade don samar da daidaito ga tattalin arzkin Nijeriya.

Muna kuma karfafa bukatar ‘yan Nijeriya su rika amfani da kayyakin da aka sarrafa a cikin gida, ya kuma kamata gwamnati ta jagoranci wannan yunkurin ta hanyar umartar hukumomi da ma’aikatun gwamnati su rika sayen kayayyakin da aka sarrafa a cikin gida, ta haka za a iya kauce wa durkushewar kamfanoni a wannan shekarar ta 2024.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

AFCON 2023: ‘Yan Wasan Da Tauraruwarsu Ke Haskawa

Next Post

Rikici Ya Ɓarke Bayan Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Sule A Gwamnan Nasarawa

Related

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

2 weeks ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

2 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

3 weeks ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA

3 weeks ago
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Yi Amafani Da Damar Fitar Da Kaya Zuwa Ketare

4 weeks ago
Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97
Tattalin Arziki

Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97

4 weeks ago
Next Post
Rikici Ya Ɓarke Bayan Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Sule A Gwamnan Nasarawa

Rikici Ya Ɓarke Bayan Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Sule A Gwamnan Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.