• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalolin Ilimi A Nijeriya Da Hanyoyin Gyara Su (1)

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Labarai
0
Matsalolin Ilimi A Nijeriya Da Hanyoyin Gyara Su (1)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matsalolin da ke addabar iilmi na da tarin yawa a Nijeriya, musamman idan aka yi la’akari da yadda aka watsi da shi tare da rashin ba shi muhimmancin da ya dace.

Ilimi wani muhimmin ginshiki ne da ke bayar da damar sanin abubuwan daban-daban, musamman na bangaren ci gaban al’umma baki-daya.

Duk da wannan muhimmanci da ilimi ke da shi, amma ana ci gaba da fuskantar matsaloli a makarantu da sauran wuraren koyar da ilimi a fadin wannan kasa.

Don haka, idan har aka kasa magance matasalolin da suke addabar ilimin, ko shakka babu zai ci gaba da tabarbare ne har zuwa illa masha Allahu.

  • Gwamna Yusuf Zai Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Fannin Ilimi A Kano
  • Gudunmawa 10 Da Ilimi Ke Bayarwa Ga Al’umma (2)

Shahararren masanin nan a bangaren ilimi, Kolawole Yetunde; ya bayyana yadda wadannan matsaloli ke ci wa harkokin ilimi tuwo a kwarya a halin yanzu.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Yetunde ya ce, abu na farko shi ne rashin ware wa bangaren isassun kudade daga gwamnatocin tarayya, jihohi da kuma kananan hukumomi.

A waannan shekara da muke ciki ta 2024, Nijeriya ta ware wa sashen ilimi kaso mafi karanci, wanda ko kadan bai kai kashi 26 cikin 100 na kasafin kudin da aka gabatar ba, kamar yadda Majalisar Dinkin Duniya ta nema.

Majalisar Dinkin Duniyar ta ba da shawara ne kan cewa, kowace kasa ta rika ware wa bangaren ilimi akalla kashi 26 cikin 100 na kasafin kudin kasar, don bunkasa harkokin da suka shafi ilimi.

Sai dai kuma wani abin takaici, tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, a kasafin kudin da ya gabatarwa Majalisar Dattawa a shekakar 2018, kashi 7.04 kacal aka ware wa wannan bangare na ilimi, wanda gaba daya kasafin kudin shekarar Naira tiriliyan 8.6 ne.

Don haka, abin da aka ware wa sashen na ilimi; Naira biliyan 605, inda kuma za a yi amfani da Naira bilyan 435.1 wajen biyan albashi, alawus- alawus da kuma tafiye-tafiye. Haka nan, an ware Naira bilyan 61.73 a matsayin kudaden ayyuka da kuma Naira biliyan109.06 na hukumar kula da ilimin bai-daya.

Haka zalika, rashin iya tafiyar da aiki yadda ya dace da kuma cin hanci da rashawa daga bangaren masu zartarwa, su ne babban manyan dalilan da suka wannan bangare na ilimi ci gaba.

Kazalika, halin ko-in-kula da gwamnati ke nuna a kan harkokin da suka shafi bangaren, su ma suna taimakawa wajen ci gaba da tabarbarewar harkar a Nijeriya.

Bugu da kari, gwamnatocin, jihohi, tarayya da kuma kananan hukumomi, sun yi buris da abubuwan da suka shafi ilimi, domin kuwa ba sa ba shi irin muhimmancin da ya dace, wanda hakan ke matukar kawo wa bangaren koma-baya.

Haka nan, batun cin hanci da rashawa wanda ya riga ya zama ruwan dare a fadin wannan kasa, domin kuwa akwai labarun da ke nuna cewa; har manyan makarantunmu na jami’a, akwai malaman da ke karbar cin hanci daga wurin dalibai; su ba su sakamako mai kyau.

Sannan, masu makarantu na amsar kudi daga wurin dalibai, su aike da sakamakon jarabawarsu zuwa hukumar da ke kula da harkokin yi wa kasa hidima. Kazalika, masu neman a dauke su, don samun gurbin karatu a jami’oi, su ma na ba da kudi kafin a ba su wannan dama.

Wadannan matsaloli kusan haka suke a dukkanin sauran makarantun da suka hada da na fasaha, Kwalejojin ilimi, makarantun Sakandare da kuma na masu zaman kansu.

Rashin kula da ayyukan da aka dora wa jami’i daga bangarori daban-daban, ta fuskar kwarewar aiki; matsalar ba iya ta Nijeriya ce kadai ba, ta shafi kusan yawancin kasashen Afirkabaki-daya.

Har ila yau, har yanzu an kasa gane batun kula da ilimin firamare, yana karkashin kulawar gwamanatin tarayya ne ko jihohi ko kuma kananan hukumomi, wanda wannan ba karamar matsala ba ce; wajen samun ci gaban bangaren ilimin bai-daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Itatuwan Banyan Biyu Suna Shaida Yadda Ake Gadon Tunani Tsakanin Xi Jinping Da Mahaifinsa

Next Post

Sallah: Tinubu Ya Buƙaci Haɗin Kai Da Sadaukarwa A Tsakanin ‘Yan Nijeriya

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Da ɗumi-ɗuminsa

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

8 hours ago
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a
Labarai

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

9 hours ago
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson
Labarai

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

10 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

13 hours ago
Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas
Labarai

Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas

16 hours ago
Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos
Labarai

Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos

17 hours ago
Next Post
Tinubu

Sallah: Tinubu Ya Buƙaci Haɗin Kai Da Sadaukarwa A Tsakanin 'Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.