• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalolin Ilimi A Nijeriya Da Hanyoyin Gyara Su (1)

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Labarai
0
Matsalolin Ilimi A Nijeriya Da Hanyoyin Gyara Su (1)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matsalolin da ke addabar iilmi na da tarin yawa a Nijeriya, musamman idan aka yi la’akari da yadda aka watsi da shi tare da rashin ba shi muhimmancin da ya dace.

Ilimi wani muhimmin ginshiki ne da ke bayar da damar sanin abubuwan daban-daban, musamman na bangaren ci gaban al’umma baki-daya.

Duk da wannan muhimmanci da ilimi ke da shi, amma ana ci gaba da fuskantar matsaloli a makarantu da sauran wuraren koyar da ilimi a fadin wannan kasa.

Don haka, idan har aka kasa magance matasalolin da suke addabar ilimin, ko shakka babu zai ci gaba da tabarbare ne har zuwa illa masha Allahu.

  • Gwamna Yusuf Zai Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Fannin Ilimi A Kano
  • Gudunmawa 10 Da Ilimi Ke Bayarwa Ga Al’umma (2)

Shahararren masanin nan a bangaren ilimi, Kolawole Yetunde; ya bayyana yadda wadannan matsaloli ke ci wa harkokin ilimi tuwo a kwarya a halin yanzu.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Yetunde ya ce, abu na farko shi ne rashin ware wa bangaren isassun kudade daga gwamnatocin tarayya, jihohi da kuma kananan hukumomi.

A waannan shekara da muke ciki ta 2024, Nijeriya ta ware wa sashen ilimi kaso mafi karanci, wanda ko kadan bai kai kashi 26 cikin 100 na kasafin kudin da aka gabatar ba, kamar yadda Majalisar Dinkin Duniya ta nema.

Majalisar Dinkin Duniyar ta ba da shawara ne kan cewa, kowace kasa ta rika ware wa bangaren ilimi akalla kashi 26 cikin 100 na kasafin kudin kasar, don bunkasa harkokin da suka shafi ilimi.

Sai dai kuma wani abin takaici, tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, a kasafin kudin da ya gabatarwa Majalisar Dattawa a shekakar 2018, kashi 7.04 kacal aka ware wa wannan bangare na ilimi, wanda gaba daya kasafin kudin shekarar Naira tiriliyan 8.6 ne.

Don haka, abin da aka ware wa sashen na ilimi; Naira biliyan 605, inda kuma za a yi amfani da Naira bilyan 435.1 wajen biyan albashi, alawus- alawus da kuma tafiye-tafiye. Haka nan, an ware Naira bilyan 61.73 a matsayin kudaden ayyuka da kuma Naira biliyan109.06 na hukumar kula da ilimin bai-daya.

Haka zalika, rashin iya tafiyar da aiki yadda ya dace da kuma cin hanci da rashawa daga bangaren masu zartarwa, su ne babban manyan dalilan da suka wannan bangare na ilimi ci gaba.

Kazalika, halin ko-in-kula da gwamnati ke nuna a kan harkokin da suka shafi bangaren, su ma suna taimakawa wajen ci gaba da tabarbarewar harkar a Nijeriya.

Bugu da kari, gwamnatocin, jihohi, tarayya da kuma kananan hukumomi, sun yi buris da abubuwan da suka shafi ilimi, domin kuwa ba sa ba shi irin muhimmancin da ya dace, wanda hakan ke matukar kawo wa bangaren koma-baya.

Haka nan, batun cin hanci da rashawa wanda ya riga ya zama ruwan dare a fadin wannan kasa, domin kuwa akwai labarun da ke nuna cewa; har manyan makarantunmu na jami’a, akwai malaman da ke karbar cin hanci daga wurin dalibai; su ba su sakamako mai kyau.

Sannan, masu makarantu na amsar kudi daga wurin dalibai, su aike da sakamakon jarabawarsu zuwa hukumar da ke kula da harkokin yi wa kasa hidima. Kazalika, masu neman a dauke su, don samun gurbin karatu a jami’oi, su ma na ba da kudi kafin a ba su wannan dama.

Wadannan matsaloli kusan haka suke a dukkanin sauran makarantun da suka hada da na fasaha, Kwalejojin ilimi, makarantun Sakandare da kuma na masu zaman kansu.

Rashin kula da ayyukan da aka dora wa jami’i daga bangarori daban-daban, ta fuskar kwarewar aiki; matsalar ba iya ta Nijeriya ce kadai ba, ta shafi kusan yawancin kasashen Afirkabaki-daya.

Har ila yau, har yanzu an kasa gane batun kula da ilimin firamare, yana karkashin kulawar gwamanatin tarayya ne ko jihohi ko kuma kananan hukumomi, wanda wannan ba karamar matsala ba ce; wajen samun ci gaban bangaren ilimin bai-daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Itatuwan Banyan Biyu Suna Shaida Yadda Ake Gadon Tunani Tsakanin Xi Jinping Da Mahaifinsa

Next Post

Sallah: Tinubu Ya Buƙaci Haɗin Kai Da Sadaukarwa A Tsakanin ‘Yan Nijeriya

Related

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Manyan Labarai

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

54 minutes ago
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC
Labarai

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

10 hours ago
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19
Da ɗumi-ɗuminsa

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

11 hours ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Da ɗumi-ɗuminsa

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

12 hours ago
Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar

13 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Da ɗumi-ɗuminsa

Lauyoyin Majalisar Dattawa Sun Ƙaryata Natasha Kan Cewa Kotu Ta Ce Ta Koma Bakin Aiki

15 hours ago
Next Post
Tinubu

Sallah: Tinubu Ya Buƙaci Haɗin Kai Da Sadaukarwa A Tsakanin 'Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

July 7, 2025
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

July 7, 2025
Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

July 7, 2025
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.