ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalolin Ilimi A Nijeriya Da Hanyoyin Gyara Su (1)

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago

Matsalolin da ke addabar iilmi na da tarin yawa a Nijeriya, musamman idan aka yi la’akari da yadda aka watsi da shi tare da rashin ba shi muhimmancin da ya dace.

Ilimi wani muhimmin ginshiki ne da ke bayar da damar sanin abubuwan daban-daban, musamman na bangaren ci gaban al’umma baki-daya.

Duk da wannan muhimmanci da ilimi ke da shi, amma ana ci gaba da fuskantar matsaloli a makarantu da sauran wuraren koyar da ilimi a fadin wannan kasa.

ADVERTISEMENT

Don haka, idan har aka kasa magance matasalolin da suke addabar ilimin, ko shakka babu zai ci gaba da tabarbare ne har zuwa illa masha Allahu.

  • Gwamna Yusuf Zai Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Fannin Ilimi A Kano
  • Gudunmawa 10 Da Ilimi Ke Bayarwa Ga Al’umma (2)

Shahararren masanin nan a bangaren ilimi, Kolawole Yetunde; ya bayyana yadda wadannan matsaloli ke ci wa harkokin ilimi tuwo a kwarya a halin yanzu.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Yetunde ya ce, abu na farko shi ne rashin ware wa bangaren isassun kudade daga gwamnatocin tarayya, jihohi da kuma kananan hukumomi.

A waannan shekara da muke ciki ta 2024, Nijeriya ta ware wa sashen ilimi kaso mafi karanci, wanda ko kadan bai kai kashi 26 cikin 100 na kasafin kudin da aka gabatar ba, kamar yadda Majalisar Dinkin Duniya ta nema.

Majalisar Dinkin Duniyar ta ba da shawara ne kan cewa, kowace kasa ta rika ware wa bangaren ilimi akalla kashi 26 cikin 100 na kasafin kudin kasar, don bunkasa harkokin da suka shafi ilimi.

Sai dai kuma wani abin takaici, tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, a kasafin kudin da ya gabatarwa Majalisar Dattawa a shekakar 2018, kashi 7.04 kacal aka ware wa wannan bangare na ilimi, wanda gaba daya kasafin kudin shekarar Naira tiriliyan 8.6 ne.

Don haka, abin da aka ware wa sashen na ilimi; Naira biliyan 605, inda kuma za a yi amfani da Naira bilyan 435.1 wajen biyan albashi, alawus- alawus da kuma tafiye-tafiye. Haka nan, an ware Naira bilyan 61.73 a matsayin kudaden ayyuka da kuma Naira biliyan109.06 na hukumar kula da ilimin bai-daya.

Haka zalika, rashin iya tafiyar da aiki yadda ya dace da kuma cin hanci da rashawa daga bangaren masu zartarwa, su ne babban manyan dalilan da suka wannan bangare na ilimi ci gaba.

Kazalika, halin ko-in-kula da gwamnati ke nuna a kan harkokin da suka shafi bangaren, su ma suna taimakawa wajen ci gaba da tabarbarewar harkar a Nijeriya.

Bugu da kari, gwamnatocin, jihohi, tarayya da kuma kananan hukumomi, sun yi buris da abubuwan da suka shafi ilimi, domin kuwa ba sa ba shi irin muhimmancin da ya dace, wanda hakan ke matukar kawo wa bangaren koma-baya.

Haka nan, batun cin hanci da rashawa wanda ya riga ya zama ruwan dare a fadin wannan kasa, domin kuwa akwai labarun da ke nuna cewa; har manyan makarantunmu na jami’a, akwai malaman da ke karbar cin hanci daga wurin dalibai; su ba su sakamako mai kyau.

Sannan, masu makarantu na amsar kudi daga wurin dalibai, su aike da sakamakon jarabawarsu zuwa hukumar da ke kula da harkokin yi wa kasa hidima. Kazalika, masu neman a dauke su, don samun gurbin karatu a jami’oi, su ma na ba da kudi kafin a ba su wannan dama.

Wadannan matsaloli kusan haka suke a dukkanin sauran makarantun da suka hada da na fasaha, Kwalejojin ilimi, makarantun Sakandare da kuma na masu zaman kansu.

Rashin kula da ayyukan da aka dora wa jami’i daga bangarori daban-daban, ta fuskar kwarewar aiki; matsalar ba iya ta Nijeriya ce kadai ba, ta shafi kusan yawancin kasashen Afirkabaki-daya.

Har ila yau, har yanzu an kasa gane batun kula da ilimin firamare, yana karkashin kulawar gwamanatin tarayya ne ko jihohi ko kuma kananan hukumomi, wanda wannan ba karamar matsala ba ce; wajen samun ci gaban bangaren ilimin bai-daya.

Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Tinubu

Sallah: Tinubu Ya Buƙaci Haɗin Kai Da Sadaukarwa A Tsakanin 'Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.