ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalolin Ilimi A Nijeriya Da Hanyoyin Gyara Su (2)

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
Ilimi

Makarantu da dama a halin yanzu, ba su da kayan aikin da ya kamata a ce suna da su, musamman domin taimaka wa koyarwar ta kasance cikin sauki.

Haka nan, idan ana maganar darussan da suka shafi harkokin kimiyya da fasaha, makarantun da suke da wadannan kayan aiki har gara ma a ce ba su da su; sakamakon rashin ingancinsu.

  • Yadda Wike Ya Kafa Tirihin Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba A Abuja
  • Badaƙalar Bashin Kaduna: Abin Da Ya Sa Ba Mu Gayyaci el-Rufai Ba – Hon. Lawal

Kazali, dakunan karatu babu littattafan zamani da mukalu da kuma mujallun da za su taimaka wa harkokin koyo da koyarwar.

ADVERTISEMENT

Rashin tarbiyya na taimakawa wajen aikata magudin jarabawa, shiga kungiyar asiri, fyade da sauransu, wadanda ke taimakawa wajen gurgunta ci gaban ilimi.

Bincike ya gano cewa, akwai wasu cibiyoyin rubuta jarabawa; inda iyaye ke ba da kudi, domin ‘ya’yansu su samu sakamako mai kyau a jarrabawar kammala sakandare tare kuma da samun makin da ya dace, don samun cancantar shiga jami’a ko sauran makarantun da ke gaba da sakarandire.

LABARAI MASU NASABA

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

Har ila yau, rashin kulawar iyaye shi ne babban abin da ya sa ake haduwa ko samun nakasu a bangaren ilimi. Domin kuwa, su ne garkuwa wajen kulawa da rayuwar ‘ya’yansu, musamman ta fuskar ba su tarbiyya da karatunsu da kuma sauran al’amuran rayuwarsu.

Akwai abubuwan da suke taimaka wa malamai wajen aikinsu na koyarwa, wadanda da ma da su ne suke amfani wajen jan hankalin dalibai; don mayar da hankalinsu kan abubuwan da ake koya masu.

Wadannan abubuwa sun hada da wadanda za su ji da na gani, littattafai, komfuta da sauransu, ba a samar wa malamai irin wadannan kayayyakin da za su taimaka musu wajen gudanar da aikinsu daga karshe, sai koyarwar ta zamar musu da wahala.

Babu wani tsarin ilimi da aka sama wa malamai, don yadda za su samar da ilimi mai nagarta ga dalibai, shi ya sa yawancin makarantu ba sa iya tafiya da tsari ko wani abu mi tasiri wanda zai yi kama da irin tsarin Kasar Ingila.

Ba kamar sauran sassa ko bangare ba, inda dalibai suke rubibin samun gurbinsu na makaranta, sai dai shi sashen ilimi da kuma kwalejin ilimi ba kowa ne yake son ya karanta bangaren ilimin ba, domin ya san maganar koyarwa ce.

Wani binciken da aka yi a shekarar 2015, na wadanda ke son shiga jami’oi; an samu kasa da kashi biyar daga cikin 1, 700,000 na wadanda suke son sashen ilmi, ba don komai ba sai don ba su da sha’awar yin aikin koyarwa.

Rashin tsare-tsaren aikin koyarwa masu nagarta yasa kwararrun da suka karanta sashen koyarwa, suka koma wasu wuraren da ake kula da hakkin ma’aikata daidai gwargwado, ko shakka babu irin hakan ne ke sa su ki maida hankalinsu kamar yadda ya dace ga lamarin aikin nasu na koyarwa.

Batun mafi karanci albashi a Nijeriya a lokacin da yana Naira 18,000, zai yi matukar wuya ga masu iyali su iya tafiyar da gida kamar yadda ya dace, kamar a bangaren tura ‘ya’yansu makaranta, saboda tsadar kudin makarantar da na littattafai da dai sauran makamantansu.

Littattafan da suka dace su rika taimaka wa dalibai wajen kara fahimtar abubuwan da ake koya masu, abu biyu ne a nan; na farko ko dai su kasance suna da wuyar samuwa ko kuma akwai dan karan tsada, ga su daliban ko malaman su saya su yi amfani da su.

Da Zarar an gano dalilan da suke sa ake samun matsaloli, duk abin da ake hange bai wuce a samu maganin matsalolin ba tare da bata lokaci.

Wannan dalili ne ya sa Johnson Olawale ya samar da hanyoyin da za a yi amafani da su wajen magance matsalolin da suke shafar ilimi a Nijeriya.

Matakin farko da ya dace a yi amafani da shi wajen kawo gyara kan matsalar ilimi a Nijeriya, wukar da naman na hannun gwamnati. Da akwai bukatar daukar matakai wadanda suka dace kasancewar su dole sai da su lamarin zai gyaru, idan har ana fatan a samu ceto sashen na ilimi.

Gwamantocin tarayya, jihohi da kuma kananan hukumomi, akwai bukatar su kara zage damtse, don ganin sun daidaita tare da gyara matsayin ilimi ya kasance a matsayin iri daya da na sauran kasashe.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu
Ilimi

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

November 8, 2025
gombe
Ilimi

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma
Ilimi

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
Next Post
Aikin Bututun Gas Na AKK Zai Bunƙasa Tattalin Arziƙin Arewacin Nijeriya – Minista

Aikin Bututun Gas Na AKK Zai Bunƙasa Tattalin Arziƙin Arewacin Nijeriya – Minista

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.