ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Badaƙalar Bashin Kaduna: Abin Da Ya Sa Ba Mu Gayyaci el-Rufai Ba – Hon. Lawal

by Shehu Yahaya
2 years ago
Kaduna

Dan majalisar dokikin Jihar Kaduna kuma daya daga cikin ‘yan kwamitin wucin gadi da ke bincikar tsohuwar gwamnatin Jihar Kaduna, Honorabul Mahmoud Lawal Isma’la, ya bayyana cewa bisa samun gamsassan bayanai kan yadda tsohuwar gwamnatin jihar ta karkatar da kudaden jihar ya sa ba su gayyaci Nasiru el-Rufai ba, domin gurfana a gaban kwamitin binciken.

Honorabul Lawal wanda aka fi sani da Bola Ige, ya ce kwamitinsu ya gano cewa daga shekarar 2015 zuwa 2023, Jihar Kaduna ta samu kudaden tallafi daga wajen jihar na naira tiriliyan 3, amma ba su san abin da aka yi da su ba, baya ga bashin ‘yan kwangila da suke bin gwamnatin na naira biliyan 311, sabanin yadda tsohuwar gwamnatin ta ce bashin ‘yan kwangilan na naira biliyan 115 ne.

  • Wakilin Sin Ya Yi Bayani Kan Matsayin Sin Kan Kare Hakkin Dan Adam
  • HOTUNA: Zanga-zanga Ta Barke A Kaduna Kan Bukatar Gurfanar Da El-Rufai

Dan majalisar ya bayyana haka ne a bayyana haka ne a cikin Shirin Barka Da Hantsi Nijeriya na LEADERSHIP Hausa da ake gabatarwa kai-tsaye a shafukan sadarwar zamani daga ranakun Litinin zuwa Juma’a da misalin karfe 9 na safe. Inda ya kara da cewa, yadda aka yi wasa da dukiyar al’ummar Jihar Kaduna abin ya wuce misali.

ADVERTISEMENT

“Dalilin da sanya ba mu gayyaci el-rufai ba shi ne, duk abin da za mu tambaye shi mutanan da muka gayyata sun ba mu amsarsu, saboda haka sai muka ga ba ma bukatar gyayatarsa.

“Akwai kuma wata takarda da el-rufai ya rubuta ya ce ya dakatar da hukumar da take tsarawa da ba da kwangila ta Jihar Kaduna (KADPPA), daga ba da duk wata kwangila, haka kuma ya cire hannunsa daga ba da kwangila a jihar. Wannan takarda ita kadai ta wadatar da kwamitinmu. Haka kuma duk wata takarda da ta shafi kudin ‘yan kwangila ita ce ta zame mana jagora.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

“Akwai kwamishinan el-rufai da ya ce duk bashin da aka ci babu amincewar majalisar tarayya wanda hakan ya saba wa dokar kabar bashin kasashen waje.

“Hadimin el-Rufai, Jimmy Lawal, da muka gayyata ya ce ba zai iya yin magana kan bashin da el-Rufai ya ci ba, abin da ya sani shi ne, lolacin da aka ciwo bashin majalisa ba ta zauna ba. Saboda haka duk abin da ya kamata mu ji daga bakin el-Rufai kwamishinoninsa sun fayyace mana.

“Akwai kwamishinan kudin el-Rufai ya tabbatar mana da cewa duk kudaden da aka karba domin a yi aiki tun kamin kudin su zo an riga an yi aikin, saboda haka da zarar kudin sun zo sai a karkatar da su zuwa wani wurin.”

Ya ci gaba da cewa tsohuwar gwamnati ta ce ta biya ‘yan kwangila naira biliyan 36, wanda kudin ya fi karfin aikin da suka yi, lamarin da ya sanya kwamitin suka zagaya duk inda aka bayar da aikin domin tabbatar da halin da ake ciki.

A cewarsa, kudin da aka biya ‘yan kwangila na nunka aikin da suka yi sau uku.

“A takarar barin gwamnati da el-Rufai ya bai wa Gwamna Uba Sani ya nuna cewa naira biliyan 115 ‘yan kwangila suke bin gwamnati, amma da muka bincika sai muka ga kudin ya haura haka ya kai naira biliyan 311, daga ciki an biya su naira biliyan 200, kuma ba su yi aikin da ya kai haka ba. Duk kwangilar da ka bayar akwai wadanda an kara musu kudin aikin, wasu kuma ba su yi aikin ba, yayin da wasu sun fara aikin sun bari, saboda haka duk bashin da aka karbo a Jihar Kaduna an karbo ne ba bisa ka’ida ba,” in ji shi.

Ya ce kwamitin ba shi da niyyar cin mutuncin wani ko muzanta wani ba, yana mai cewa, “Tun lokacin da muka fara aikin, gwamnan Jihar Kaduna Uba Sani bai taba kiranmu ba, hasalima bai san halin da kwamitin yake ciki ba, saboda babu hannunsa a cikin aikin kwamitinmu.

“Bukatar kwamitinmu shi ne, a dawo da makudan kudaden da aka sace domin yi wa al’ummar Jihar Kaduna aiki da su.” Ya bukaci al’ummar Jihar Kaduna da su ci gaba bai wa gwamnati goyon baya wajen ganin an kara samun ayyukan ci gaba a fadin jihar baki daya.

Kaduna
Shehu Yahaya
+ postsBio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA
Labarai

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Next Post
‘Yansanda Sun Cafke Ɗan Banga Kan Zargin Kashe Mutum 2 Kan Rikicin Gona A Adamawa

'Yansanda Sun Cafke Ɗan Banga Kan Zargin Kashe Mutum 2 Kan Rikicin Gona A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.