• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsayin Jami’o’in Nijeriya A Ma’aunin Jami’o’in Duniya (Ra’ayinmu)

by Sulaiman
3 years ago
Nijeriya

Fiye da wani lokaci, rahoton da aka fitar na matsayin jami’o’in Nijeriya a ma’aunin jami’o’i na duniya ya nuna cewa, wannan ne lokaci fiye da wani lokacin da ake bukatar a maida da hankali a kan halin da harkar ilimi ta ciki a kasar nan musamman ilimin jami’a a kasar nan.

Rahoton da Cibiyar ‘Times Higher Education’ ta fitar ya nuna cewa, gwarzuwar jami’a a Nijeriya ita ce, Jami’ar Afe Babalola (ABUAD) da ke Ado-Ekiti, wadda ta yi ta 400 a jerin jami’o’in duniya.

  • 2023: Kwankwaso Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Yi Watsi Da APC Da PDP

Cibiyar ta karbu a fadin duniya saboda sahihancin rahotannin da take fitarwa, cikin abubuwan da take lura dasu wajen yanke hukuncin zabar kwazon jami’a sun hada da abin da ya shafi bangaren karantarwa da bincike da kuma yadda jami’ar ta karbuwa a sassan duniya.

Yakamata a fahinci cewa, a shekarar 2022 cibiyar ta nazarci jami’o’i 1, 600 a kasashe 99. Cibiyar ta yi nazarin mukala fiye da Miliyan 108 da kuma kundin bincike da jami’o’i fiye da Miliyan 14.4 ta kuma karbi amsar tambayoyi daga masana fiye da 22,000 a fadin duniya.

Babu wata kasar Afrika data zo cikin jami’o’i na 100 na farko a jerin gwarazan jami’o’i duniya. Gwarzuwar jami’a data fi tsari a Afrika ita ce jami’ar kasar Afirka ta Kudu ‘Unibersity of Cape Town’ inda ta zo ta 183 a duniya. A Nijeriya kuma Jami’ar Ibadan da ta Legas suka zo na 401 da 501.

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

A yayin da muke taya Jami’ar ABUAD murnar wannan nasarar, mun lura da cewa, wannan yana nuna irin tsananin yadda harkar ilimi ta tabarbarewar a kasar nan.

Duk da matukar muhimmancinta a wajen tafiyar da tattalin arzikin kasa gwamnatocin da suka gabata sun yi watsi da harkar ilimi, ta hanyar nakasa kasafin kudin da ake tanadar wa bangaren ilimin.

Akwai bukatar a sake nazarin kasafin kudin da jihohin kasar nan 36 ke samar wa bangaren ilimi musamman ma ganin kowacce jiha a halin yanzu ta mallaki jami’a ta kanta. Yayin da hukumar Majalisar Dinkin Duniya ta nemi a ware kashi 25 na kasafin kudin da aka kiyasta kashe ga bangaren ilimi har yanzu Nijeriya bata kai ga samar da kashi 15 ba.

A kasafin kudin shakarar 2022 gwmanatin Nijeriya ta ware wa bangaren ilimi Naira Tiriliyan 1.29 wanda ke nuna cewa kashi 7.9 kenan na kasasfin kudin da aka yi a shekarar. Wannan na nuna cewa an yi wa bangaren ilimi kashi 10 kenan duk kuwa da cewa, Majalisar Dinkin Duniya ta nemi ne aware kashi 25 na kasafin kudin a duk shekara don tallafa wa harkar ilimin al’umma.

Idan za a iya tunawa gwamnatin Buhari ta kasafta kashe Naira Tiriliyan 55.3 don gudanar da harkokin gwamnati a cikin shakara 6 na mulkinta amma Naira Tiriliyan 3.5 kawai aka ware wa bangaren ilimi wanda ke nuna kashin yana kasa da kashi 10, wanda ke nuna karara lamarin ilimi ba abin da gwamnatin ta dauka da muhimmanci bane.

Abin takaici a nan shi ne bangaren ilimi ya yi fama da matsalar kudade ga rashin kayan aiki da kuma karancin albashi ga kuma karancin ma’aikata wanda duk suna taimakawa wajen haifar da matsaloli ga bangaren ilimin tun daga firamare, sakandare har zuwa manyan makarantu.

Yawancin masana a bangaren ilimi basu yi mamakin ganin jami’o’in Nijeriya basu tabuka abin a zo a gani ba a tantancewa tare da matsayin su a tsakanin jami’o’in duniya, wannan yana faruwa ne saboda yawan yajin aikin da malaman jami’a ke shiga wanda ke haifar da cikas a abin da ya shafi bincike da karantarwa, fiye da wata 4 kenan malaman jami’o’i a Nijeriya ke yajin aiki har yanzu ba a kai ga warware matsalar ba.

A karkashin wannan gwamnatin kawai Malaman Jami’a sun yi yajin aiki na fiye da wata 13, wannan ba karamin asara ba ne ga harkar ilimi a Nijeriya.

Wadannan na daga cikin matsalolin da suka haifar da tabarbarewar ilimi a kasar nan kuma in har ba a magance su ba lamarin ilimi zai cigaba da tabarbarewa a kullum, hakan kuma abin kunya ne ga Nijeriya a idon duniya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin
Rahotonni

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

October 3, 2025
Next Post
Sama Da Mutum 150 Ke Hannun ‘Yan Bindiga A Jibiya – Shugaban Karamar Hukumar

Sama Da Mutum 150 Ke Hannun 'Yan Bindiga A Jibiya – Shugaban Karamar Hukumar

LABARAI MASU NASABA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.