ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mayar Da CBN Legas: Muna Roko A Mayar Da Ma’aikatar Kasuwanci Kano, NNPCL, NIMASA, NPA Zuwa Neja Delta

by Sulaiman
2 years ago
CBN

Tsohon Mataimakin Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar APC na Kasa, Hon. Yekini Nabena, ya bukaci shugaban kasa Bola Tinubu da ya amince da mayar da kamfanin man fetur na kasa (NNPCL) zuwa yankin Neja Delta.

Ya kuma bukaci Tinubu da ya mayar da ma’aikatar noma da raya karkara ta tarayya zuwa jihar Binuwai inda amfanin noma ke da yawa don yin daidaito kan kudirin mayar da wasu sassan babban bankin Nijeriya (CBN) da hukumar kula da filayen tashi da saukar jiragen sama ta kasa FAAN daga Babban Birnin Tarayya (FCT) zuwa Legas.

  • Tinubu Ya Tafi Faransa Domin Yin Wata Ziyarar Sirri
  • Ba Mu Kama Shugaban Miyetti Allah Ba – DSS

Gwamnatin tarayya karkashin jagorancin Shugaba Bola Tinubu, ta nuna sha’awarta na maida wani bangare na CBN da FAAN zuwa jihar Legas, ta ce, hakan zai fi da cewa. Duk da cewa, yunkurin ya jawo mahawara mai zaifi na daga goyon baya da adawa, musamman daga bangaren Arewacin Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Nabena, wanda ke zargin munanan manufar yin irin wannan yunkuri, ya ce, Shugaba Bola Tinubu tuni dama bai yi imani da kasancewar Nijeriya a matsayin kasa daya ba kafin ya zama shugaban kasa.

Jigon na APC a wata sanarwa da ya fitar a Abuja ranar Laraba, ya nanata cewa, hukumomin tarayya alamomin hadin kan Nijeriya ne kuma bai kamata a yi wasa da su ba.

LABARAI MASU NASABA

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Nabena ya ce: “Idan har ingancin wadannan sassa a ka duba don mayar da su inda ya fi da cewa (Legas), mu ‘yan yankin Neja Delta muna rokon cewa, NNPCPL, NIMASA, NPA da sauran su za su fi da cewa a jihohin Bayelsa, Rivers ko Delta.

“Haka zalika ma’aikatar ma’adinai da karafa ta tarayya ta koma jihar Kogi inda muke da Babbar masana’anta ta Karfe da ke Ajaokuta.

“Na kuma yi imanin cewa, ko dai a mayar da ma’aikatar ciniki da zuba jari ta tarayya zuwa Kano ko kuma a mayar da ita jihar Anambra inda ake da manyan kasuwanni, haka ma a kai ma’aikatar noma ta tarayya jihar Binuwai, domin takenta shi ne ‘kwandon abinci na Kasa.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Next Post
Sudan: Aiwatar Da “Yarjejeniyar Jiddah” Za Ta Shimfida Zaman Lafiya – Gwamnati

Sudan: Aiwatar Da “Yarjejeniyar Jiddah” Za Ta Shimfida Zaman Lafiya - Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.