ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Karin Kamfanonin Ketare Suka Samu Ra’ayin Bai Daya Kan Zuwa Kasar Sin Don Raya Kansu?

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

Bisa kididdigar da ma’aikatar kasuwanci ta kasar Sin ta fitar a kwanan nan, an ce yawan kudin jarin waje da kasar ta yi amfani da shi a watanni uku na farkon shekarar bana, ya kai kudin Sin Yuan biliyan 408.45, adadin da ya karu da kaso 4.9 cikin dari bisa na makamancin lokaci na bara, lamarin da ya shaida cigaban tattalin arzikin Sin ba tare da tangarda ba.

A cikin wannan adadi, yawan sabbin kamfanonin ketare ya zarce dubu 10, wanda ya karu da kaso 25.5 cikin dari bisa makamancin lokaci na bara. Yadda kamfanoni ke shiga kasar Sin don kara samun bunkasuwa ya riga ya zama wani muhimmin batu da manyan kafofin watsa labarai na kasa da kasa suke tattaunawa a yanzu.

  • Tasirin Matsalolin Tsaro, Karancin Kudi Da Tsadar Rayuwa Ga Bukukuwan Sallar Bana

Akwai hasashen cewa, yawan kudin jarin da za a rika zuba wa sauran kasashe zai ci gaba da raguwa a shekarar 2023. Bisa wannan yanayin da ake ciki, kasar Sin ta sha wuya wajen samun wannan sakamako na jawon jarin waje, amma hakan ba abu ne da ya wuce zato ba.

ADVERTISEMENT

Dalili kuwa shi ne, idan muka duba fannonin da kamfanonin suke zubawa jari, za a iya gano cewa, sun fi zuba wa kasar Sin jari ne a fannonin kimiyya da fasahohin zamani, da karin ingancin masana’antu, a kokarin more damammakin cigaban kasar Sin mai inganci.

A matsayin babbar kasuwa ta biyu ta sayen kayayyaki ta duniya, da babbar kasuwa ta farko ta sayar da kayayyaki ta yanar gizo ta duniya, babu shakka kasar Sin ta zama tamkar wani babban kek ga jarin waje. A waje daya kuma, kasar Sin da ke bude kofarta ga waje, na son more wannan kek na ta tare da sauran kasashen waje, tare da kara girmansa.

LABARAI MASU NASABA

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Kamfanin Tesla, da Airbus, da Astrazeneca, sun sanar da kafa masana’antu, da kara zuba jari a kasar Sin daya bayan daya, lamarin da ya shaida cewa, kamfanonin ketare na da kwarin gwiwa game da kasar Sin, domin sun gane cewa, zuba jari ga kasar Sin shi ne kokarin kago makoma mai haske.

Wasu rahotannin baya bayan nan sun bayyana cewa, ana sa ran shugaba Joe Biden na Amurka, zai sanya hannu kan wata dokar shugaba nan da wasu makwanni kadan masu zuwa, wadda za ta takaitawa kamfanonin Amurka adadin jarin da za su iya zubawa, a wasu muhimman fannonin tattalin arzikin kasar Sin, ciki har da fannin kirar bangarorin harhada na’urorin latironi na “semiconductors”, da fannin kwaikwayon tunanin bil adama na AI.

Da yake tsokaci game da hakan, yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa na yau Jumma’a, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Wang Wenbin, ya ce ainihin dalilin Amurka na kakaba takunkumi a fannin jarin da ake iya zubawa a Sin, shi ne dakile ikon Sin din na samun ci gaba.

Wang ya kara da cewa, Sin na matukar adawa da wannan mataki, za ta kuma lura matuka da yanda abubuwa ke gudana, tare da daukar matakin kare hakkoki, da moriyar ta yadda ya kamata. (Kande Gao, Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam
Daga Birnin Sin

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa
Daga Birnin Sin

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya
Daga Birnin Sin

CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

November 11, 2025
Next Post
Sin A shirye Take Ta Tallafawa Ci Gaban Kasar Gambia

Sin A shirye Take Ta Tallafawa Ci Gaban Kasar Gambia

LABARAI MASU NASABA

Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025
CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

November 11, 2025
CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

November 11, 2025
Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

November 11, 2025
CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

November 11, 2025
Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?

Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.