• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa ‘Yan Wasa Suka Fara Korafi A Kan Yawan Wasannin Da Suke Bugawa?

by Abba Ibrahim Wada
10 months ago
in Wasanni
0
Me Ya Sa ‘Yan Wasa Suka Fara Korafi A Kan Yawan Wasannin Da Suke Bugawa?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ba wannan lokacin bane ‘yan wasan kwallon kafa a duniya suka fara korafi a kan yawan wasannin da suke bugawa wanda hukumomin kwallon kafa na FIFA da EUFA suke kara musu a kan wadanda suke bugawa a baya.

Tun a shekarun baya tsohon kociyan Real Madrid da Manchester United, Jose Mourinho, ya yi korafi a kan yawan wasannin da ake sake karawa ‘yan wasa wanda hakan a cewarsa yana kawo gajiya ga ‘yan wasan kuma baya taimaka musu.

  • Xi Ya Jaddada Ba Da Cikakkiyar Dama Ga Fa’idar Siyasa Ta CPPCC
  • Sarakuna 2 A Kano: Ina Aka Kwana?

Tsohon kociyan Liberpool, Jugen Klopp, da na Manchester City, Pep Guardiola, sun yi korafi a kan yawan wasannin da hukumomi suke karawa wanda hakan yana kawo yawan jin ciwo da rashin kuzari ga ‘yan wasa.

A farkon wannan watan ne shima dan wasan Manchester City da kasar Belgium, Kebin de Bruyne, ya yi korafi a kan cewa suma mutane ne kamar kowa saboda haka wasannin da ake sake karawa sun yi yawa soasai.

Shima dan wasan Manchester City, Rodri ya ce ‘‘yan wasan na dab da yin yajin aiki, sakamakon da aka kara yawan wasannin da za suke bugawa wanda a cewarsa ya kamata a dinga tuntubarsu idan za a kara yawan wasanni saboda su ne suke bugawa.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

Manchester City ta kara da Inter Milan ranar Laraba a Champions League, wanda aka kara wasa biyu kafin karawar zagaye na biyu a sabon fasalin babbar gasar Zakarun Turai ta bana wanda aka fara a ranar 17 ga wannan watan.

A gasar Club World Cup kuwa, inda Manchester City za ta fafata daga badi, an kara kungiyoyi sun kai 32, an samu karin wasanni da yawa kenan wanda hakan ne ya sa dan wasa Rodri ya ce yana jin suna dab da yin yajin aiki.

Ya ci gaba da cewa idan har an ci gaba da haka, za a kai lokacin da ba su da wani zabi sai dai kawai su tsunduma yajin aiki saboda suma mutane ne kamar kowa kuma suna da iyali kamar kowa amma za su dan kara jira su gani.

A sabon fasalin Champions League da Club World Cup na nufin Manchester City za ta buga karin wasanni hudu a kakar daga bana, fiye da yawan da ta fafata a bara wanda hakan zai kasance ‘yan wasa za su gaji sosai. Wasanni biyu kacal Manchester City ta yi ta kuma lashe Club World Cup a Disamba, amma a kakar badi za ta yi karawa uku a cikin rukuni da hudu a zagayen gaba har kai wa karawar karshe kuma a kakar wasa biyu baya,

Manchester City ta buga wasanni 120 a dukkan fafatawa, yayin da Rodri ya buga wasanni 63 a kwanaki 343 a kakar wasa ta 2023 zuwa 2024.

Rodri, wanda ya buga wa tawagar Sifaniya da Manchester City wasa 63 a bara, ya lashe Premier League da kofin Nahiyar Turai da ya buga cikin wata biyu kuma bayan tashi daga Champions League karawar dab da karshe a gidan Real Madrid, Rodri ya sanar a cikin watan Afirilu cewar yana bukatar hutu.

Hakan ne ma ya sa bai buga wa Manchester City wasanni uku da fara kakar bana ba, ya fara daga 2-1 inda ta doke Brentford a Premier League ranar Asabar, kwana shida tsakani da ya yi wa Sifaniya Nations League.

Bayan kammala kakar wasa ta 2023 zuwa 2024 wadda aka fara daga 6 ga watan Agustan shekarar 2023 da aka kammala a kwana 343, ranar 14 ga watan Yuli, Rodri ya sanar cewar yana bukatar dogon hutu fiye da wanda ake bashi.

Masana suna ganin yawan ciwon da wasu ‘yan wasan suke samu yana da alaka da yawan wasannin da suke bugawa domin ban da wasannin kungiyoyinsu, ‘yan wasan suna wakiltar kasashensu a wasannin gasa daban-daban ko kuma wasannin sada zumunta ko kuma na neman cancantar shiga gasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan WasaKorafiWasanni
ShareTweetSendShare
Previous Post

Su Waye ‘Yan Afirka Da Suka Canja Kungiya A Turai?

Next Post

Fashewar Bam Ta Kashe Da Raunata Daruruwan Mutane A Lebanon

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

13 hours ago
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe
Wasanni

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

24 hours ago
Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa
Wasanni

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

4 days ago
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

5 days ago
Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo
Wasanni

Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo

5 days ago
Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro
Wasanni

Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro

6 days ago
Next Post
Fashewar Bam Ta Kashe Da Raunata Daruruwan Mutane A Lebanon

Fashewar Bam Ta Kashe Da Raunata Daruruwan Mutane A Lebanon

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.