• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa ‘Yan Wasa Suka Fara Korafi A Kan Yawan Wasannin Da Suke Bugawa?

by Abba Ibrahim Wada
9 months ago
in Wasanni
0
Me Ya Sa ‘Yan Wasa Suka Fara Korafi A Kan Yawan Wasannin Da Suke Bugawa?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ba wannan lokacin bane ‘yan wasan kwallon kafa a duniya suka fara korafi a kan yawan wasannin da suke bugawa wanda hukumomin kwallon kafa na FIFA da EUFA suke kara musu a kan wadanda suke bugawa a baya.

Tun a shekarun baya tsohon kociyan Real Madrid da Manchester United, Jose Mourinho, ya yi korafi a kan yawan wasannin da ake sake karawa ‘yan wasa wanda hakan a cewarsa yana kawo gajiya ga ‘yan wasan kuma baya taimaka musu.

  • Xi Ya Jaddada Ba Da Cikakkiyar Dama Ga Fa’idar Siyasa Ta CPPCC
  • Sarakuna 2 A Kano: Ina Aka Kwana?

Tsohon kociyan Liberpool, Jugen Klopp, da na Manchester City, Pep Guardiola, sun yi korafi a kan yawan wasannin da hukumomi suke karawa wanda hakan yana kawo yawan jin ciwo da rashin kuzari ga ‘yan wasa.

A farkon wannan watan ne shima dan wasan Manchester City da kasar Belgium, Kebin de Bruyne, ya yi korafi a kan cewa suma mutane ne kamar kowa saboda haka wasannin da ake sake karawa sun yi yawa soasai.

Shima dan wasan Manchester City, Rodri ya ce ‘‘yan wasan na dab da yin yajin aiki, sakamakon da aka kara yawan wasannin da za suke bugawa wanda a cewarsa ya kamata a dinga tuntubarsu idan za a kara yawan wasanni saboda su ne suke bugawa.

Labarai Masu Nasaba

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Manchester City ta kara da Inter Milan ranar Laraba a Champions League, wanda aka kara wasa biyu kafin karawar zagaye na biyu a sabon fasalin babbar gasar Zakarun Turai ta bana wanda aka fara a ranar 17 ga wannan watan.

A gasar Club World Cup kuwa, inda Manchester City za ta fafata daga badi, an kara kungiyoyi sun kai 32, an samu karin wasanni da yawa kenan wanda hakan ne ya sa dan wasa Rodri ya ce yana jin suna dab da yin yajin aiki.

Ya ci gaba da cewa idan har an ci gaba da haka, za a kai lokacin da ba su da wani zabi sai dai kawai su tsunduma yajin aiki saboda suma mutane ne kamar kowa kuma suna da iyali kamar kowa amma za su dan kara jira su gani.

A sabon fasalin Champions League da Club World Cup na nufin Manchester City za ta buga karin wasanni hudu a kakar daga bana, fiye da yawan da ta fafata a bara wanda hakan zai kasance ‘yan wasa za su gaji sosai. Wasanni biyu kacal Manchester City ta yi ta kuma lashe Club World Cup a Disamba, amma a kakar badi za ta yi karawa uku a cikin rukuni da hudu a zagayen gaba har kai wa karawar karshe kuma a kakar wasa biyu baya,

Manchester City ta buga wasanni 120 a dukkan fafatawa, yayin da Rodri ya buga wasanni 63 a kwanaki 343 a kakar wasa ta 2023 zuwa 2024.

Rodri, wanda ya buga wa tawagar Sifaniya da Manchester City wasa 63 a bara, ya lashe Premier League da kofin Nahiyar Turai da ya buga cikin wata biyu kuma bayan tashi daga Champions League karawar dab da karshe a gidan Real Madrid, Rodri ya sanar a cikin watan Afirilu cewar yana bukatar hutu.

Hakan ne ma ya sa bai buga wa Manchester City wasanni uku da fara kakar bana ba, ya fara daga 2-1 inda ta doke Brentford a Premier League ranar Asabar, kwana shida tsakani da ya yi wa Sifaniya Nations League.

Bayan kammala kakar wasa ta 2023 zuwa 2024 wadda aka fara daga 6 ga watan Agustan shekarar 2023 da aka kammala a kwana 343, ranar 14 ga watan Yuli, Rodri ya sanar cewar yana bukatar dogon hutu fiye da wanda ake bashi.

Masana suna ganin yawan ciwon da wasu ‘yan wasan suke samu yana da alaka da yawan wasannin da suke bugawa domin ban da wasannin kungiyoyinsu, ‘yan wasan suna wakiltar kasashensu a wasannin gasa daban-daban ko kuma wasannin sada zumunta ko kuma na neman cancantar shiga gasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan WasaKorafiWasanni
ShareTweetSendShare
Previous Post

Su Waye ‘Yan Afirka Da Suka Canja Kungiya A Turai?

Next Post

Fashewar Bam Ta Kashe Da Raunata Daruruwan Mutane A Lebanon

Related

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Wasanni

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

1 day ago
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?
Wasanni

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

1 day ago
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr
Wasanni

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

4 days ago
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi
Wasanni

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

4 days ago
Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford
Wasanni

Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford

5 days ago
Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona
Wasanni

Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

7 days ago
Next Post
Fashewar Bam Ta Kashe Da Raunata Daruruwan Mutane A Lebanon

Fashewar Bam Ta Kashe Da Raunata Daruruwan Mutane A Lebanon

LABARAI MASU NASABA

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.