• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Aikin Hukumar Da Tinubu Ya Bai Wa Ali Nuhu Shugabanci?

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
in Nishadi
0
Mene Ne Aikin Hukumar Da Tinubu Ya Bai Wa Ali Nuhu Shugabanci?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 12 ga watan Janairu na shekarar 2024 da muke ciki shugaba Bola Ahmed Tinubu na Nijeriya ya nada shahararren jarumin fina finan Kannywood Ali Nuhu matsayin shugaban hukumar shirya fina finai ta Nijeriya (Nigeria Film Cooperation).

Hakan ya sa LEADERSHIP Hausa ta yi dogon bincike domin bayyanawa masu karatu ainahin aikin wannan hukuma.

  • Ina Rubutu A Kan Rayuwar Yau Da Kullum Domin Mutane Su Wa’azantu – Fatima Sunusi
  •  ‘Yansanda Sun Cafke Wasu Da Ake Zargi Da Satar Mutane A Abuja

Nigeria Film Corporation hukuma ce mallakin gwamnati da ke sarrafa fina-finan Nijeriya wadda aka kafa ta a cikin shekarar 1979 a karkashin doka mai lamba 61 na kundin tsarin mulkin Nijeriya 1979.

Hukumar ta NFC a takaice tana aiki ne a matsayin cibiyar gwamnatin tarayya wacce aka dorawa duk wani alhaki na ganin masana’antar fina finan Nijeriya ta tsayu da kafafunta kuma ta fitar da kyawawan halaye da al’adun yan Nijeriya a idon duniya.

Ma’aikatar Yada Labarai da Al’adu ta Tarayya ke kula da ita kuma ta bata duk wani iko da take bukata domin bunkasa al’adu ta hanyar sinima a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ta hanyar ayyukanta hukumar tana bayarda gudummawa sosai ga ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin al’umma.

Samar da fina-finai don amfanin gida da fitar da su zuwa kasashen waje na daga cikin muhimman aiyuka da wannan hukuma take gudanarwa.

Wasu daga cikin aiyukan wannan hukuma shine samarwa da kuma kula da kayan aikin shirya fina-finai,karfafa gwiwar shirya fina-finai da ‘yan Nijeriya ke yi ta hanyar kudi da sauran nau’o’in taimako,samar da wuraren horarwa da adana fina-finai, kayan sauti da na bidiyo da sauransu.

Saye tareda rarraba fina-finai ga wuraren da suka kamata,tallafawa masana’antun shirya fina finai,shirya bukukuwan baje kolin fina finai da fasaha na cikin gida  Nijeriya da kuma na kasa da kasa,gudanar da bincike kan abubuwan da suka shafi fim da masana’antu baki daya.

Wadannan sune muhimman ayyuka da wannan hukuma da aka baiwa jarumi Ali Nuhu shugabanci take gudanarwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

AFCON 2023: Nijeriya Ta Tsallaka Zuwa Matakin Zagayen Dabda Kusa Da Na Karshe

Next Post

Farashin Shinkafa Zai Ƙaru Da Kashi 40%, Masara Da Kashi 25% A Shekarar 2024 – AFEX

Related

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan
Nishadi

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

2 days ago
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango
Nishadi

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

3 days ago
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Nishadi

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

1 week ago
Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba
Nishadi

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

2 weeks ago
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

3 weeks ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

1 month ago
Next Post
Farashin Shinkafa Zai Ƙaru Da Kashi 40%, Masara Da Kashi 25% A Shekarar 2024 – AFEX

Farashin Shinkafa Zai Ƙaru Da Kashi 40%, Masara Da Kashi 25% A Shekarar 2024 - AFEX

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.