ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Rubutu A Kan Rayuwar Yau Da Kullum Domin Mutane Su Wa’azantu – Fatima Sunusi

by Sadiq
2 years ago
RUbutu

LABARAI MASU NASABA

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

EFCC Ta Kama Mutum 11 Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba A Kwara

ADVERTISEMENT

Daya daga cikin hazikan marubutan littattafan Hausa na yanar gizo wato FATIMA SUNUSI RABI’U wacce aka fi sani da UMMU AFFAN, ta bayyana wa masu karatu dalilinta na fara rubutun littafin Hausa tare da irin nasarorin da ta samu game da rubutun, har ma da wasu batutuwan masu yawa. Ga dai tattaunawar tare da PRINCESS FATIMA ZARAH MAZADU kamar haka:

Ya sunan malamar?

To cikakken sunana shi ne; Fatima Sunusi Rabi’u, amma a ‘media’ an fi sani na da Ummu Affan.

Ko za ki fada wa masu karatu dan takaitaccen tarihinki?

An haife ni a shekarar Alif da dari tara da casa’in da bakwai (1997), a Jihar Katsina karamar hukumar Funtuwa. Na yi karatuna tun daga firamare zuwa karamar Sakandare a can, yayin da rayuwata ta dawo garin Kaduna anan na dora daga SS 1 har nayi kandi a 2015. Karatun addini ma Alhamdulillah nayi sauka sannan kuma ina da aure ma.

Me ya ja hankalinki har kika fara rubutu?

To gaskiya da farko sha’awa ce, domin tun ina karama nake sha’awar rubutu. Sannan na kasance makaranciyar littattafan Hausa hakan ne ma ya kara sa mini jin sha’awar rubutun har nake jin zan iya. Na kan sami littafi guda da biro na rubuta labari. A da, ina rubutawa na tara da niyyar watarana zan buga, kafin daga baya na ga ana rubutu a online ni ma na ce bari to na fara a nan.

Ya gwagwarmayar farawar ta kasance?

To Alhamdu lillahi ban sha wata wahala ba, kasancewar a midiya nake rubutun nawa, duk da dai da farko ni kadai nake fostin har daga baya kuma na ga wasu ma suna taya ni ba tare da na sani ba, to sai dai hamdala.

Ya batun iyaye lokacin da kika fara sanar musu kina son fara rubutu, shin kin samu wani kalubale daga gare su ko kuwa?

Ban fuskanci kalubale ba, don tun ina gida mahaifiyata na kara mini kwarin gwiwa. Shi ma mahaifina ban samu matsala da shi ba, ban sani ba ko dan sai da na yi aure sannan na fada masa ina rubutun tunda da ina gida ban buga ba sai bayan aurena na fara rubutu a Online.

Ya farkon fara rubutun ya kasance?

Gaskiya da farko ban sha wahala sosai ba, tun da ni ‘Online Writer’ ce, nakan yi rubutu ne kuma na tura, tun littafina na farko gaskiya Alhamdu lillah ya samu karbuwa sosai.

Kamar wanne bangare kika fi maida hankali akai wajen yin rubutu?

Ina rubutuna a kan rayuwar yau da kullum, fadakarwa, soyayya, nishadi da sauransu, maganar gaskiya babu inda bana tabawa indai na sami jigo to zan rubutu a kai domin masu irin abin su wa’azantu.

Kin rubuta labarai sun kai kamar guda nawa?

Eh! to gaskiya na rubuta labarai a kallah guda goma sha takwas 18, bayan gajerun labarai na shiga gasa da na dan rubuta a kalla bakwai.

Wanne labari ne ya zamo bakandamiyarki cikin wadanda ki ka rubuta?

Duka littattafaina ina kaunarsu kam, amma zan iya cewa ‘MU GANI A KASA…’ Yanzu shi ne bakandamiyata.

Wanne labari ne ya fi baki wahala wajen rubuta shi?

Littafina ‘SANDAR MAKAUNIYA’ kasancewar akwai siyasa a cikin labarin da tsaface-tsaface da kuma aljanu na dan sha wahala, musamman a kan aljanin da ke jikin yarinyar tun da ba jinsina ba ne, na dan sha wahala wajen ganin na rubuta abin da yake tamkar a zahiri.

Cikin labaran da ki ka rubuta ko akwai wanda ki ka buga?

Eh Alhamdu lillah akwai wata gasa da aka saka wani malaminmu ne a nan online na shiga cikin mutum biyar da aka buga wa labaransu, an buga mini BAKAR FURA… kuma ni ma na saka kudi aka kara yi min wasu, daga baya kuma na buga MU GANI A KASA… shi ma.

Za mu ci gaba mako mai zuwa

MASU ALAKA

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Zambar Kudi: Kotu Ta Tasa Keyar Dillalin Gidaje Zuwa Gidan Kaso
Adabi

EFCC Ta Kama Mutum 11 Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba A Kwara

February 6, 2026
CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki
Adabi

CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki

January 30, 2026
Next Post
nauru

Ministan Harkokin Wajen Nauru: Dawo Da Huldar Diplomasiyya Tsakanin Sin Da Nauru Muhimmin Lokaci Ne A Tarihi

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.