ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Rubutu A Kan Rayuwar Yau Da Kullum Domin Mutane Su Wa’azantu – Fatima Sunusi

by Sadiq
2 years ago
RUbutu

LABARAI MASU NASABA

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

EFCC Ta Kama Mutum 11 Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba A Kwara

ADVERTISEMENT

Daya daga cikin hazikan marubutan littattafan Hausa na yanar gizo wato FATIMA SUNUSI RABI’U wacce aka fi sani da UMMU AFFAN, ta bayyana wa masu karatu dalilinta na fara rubutun littafin Hausa tare da irin nasarorin da ta samu game da rubutun, har ma da wasu batutuwan masu yawa. Ga dai tattaunawar tare da PRINCESS FATIMA ZARAH MAZADU kamar haka:

Ya sunan malamar?

To cikakken sunana shi ne; Fatima Sunusi Rabi’u, amma a ‘media’ an fi sani na da Ummu Affan.

Ko za ki fada wa masu karatu dan takaitaccen tarihinki?

An haife ni a shekarar Alif da dari tara da casa’in da bakwai (1997), a Jihar Katsina karamar hukumar Funtuwa. Na yi karatuna tun daga firamare zuwa karamar Sakandare a can, yayin da rayuwata ta dawo garin Kaduna anan na dora daga SS 1 har nayi kandi a 2015. Karatun addini ma Alhamdulillah nayi sauka sannan kuma ina da aure ma.

Me ya ja hankalinki har kika fara rubutu?

To gaskiya da farko sha’awa ce, domin tun ina karama nake sha’awar rubutu. Sannan na kasance makaranciyar littattafan Hausa hakan ne ma ya kara sa mini jin sha’awar rubutun har nake jin zan iya. Na kan sami littafi guda da biro na rubuta labari. A da, ina rubutawa na tara da niyyar watarana zan buga, kafin daga baya na ga ana rubutu a online ni ma na ce bari to na fara a nan.

Ya gwagwarmayar farawar ta kasance?

To Alhamdu lillahi ban sha wata wahala ba, kasancewar a midiya nake rubutun nawa, duk da dai da farko ni kadai nake fostin har daga baya kuma na ga wasu ma suna taya ni ba tare da na sani ba, to sai dai hamdala.

Ya batun iyaye lokacin da kika fara sanar musu kina son fara rubutu, shin kin samu wani kalubale daga gare su ko kuwa?

Ban fuskanci kalubale ba, don tun ina gida mahaifiyata na kara mini kwarin gwiwa. Shi ma mahaifina ban samu matsala da shi ba, ban sani ba ko dan sai da na yi aure sannan na fada masa ina rubutun tunda da ina gida ban buga ba sai bayan aurena na fara rubutu a Online.

Ya farkon fara rubutun ya kasance?

Gaskiya da farko ban sha wahala sosai ba, tun da ni ‘Online Writer’ ce, nakan yi rubutu ne kuma na tura, tun littafina na farko gaskiya Alhamdu lillah ya samu karbuwa sosai.

Kamar wanne bangare kika fi maida hankali akai wajen yin rubutu?

Ina rubutuna a kan rayuwar yau da kullum, fadakarwa, soyayya, nishadi da sauransu, maganar gaskiya babu inda bana tabawa indai na sami jigo to zan rubutu a kai domin masu irin abin su wa’azantu.

Kin rubuta labarai sun kai kamar guda nawa?

Eh! to gaskiya na rubuta labarai a kallah guda goma sha takwas 18, bayan gajerun labarai na shiga gasa da na dan rubuta a kalla bakwai.

Wanne labari ne ya zamo bakandamiyarki cikin wadanda ki ka rubuta?

Duka littattafaina ina kaunarsu kam, amma zan iya cewa ‘MU GANI A KASA…’ Yanzu shi ne bakandamiyata.

Wanne labari ne ya fi baki wahala wajen rubuta shi?

Littafina ‘SANDAR MAKAUNIYA’ kasancewar akwai siyasa a cikin labarin da tsaface-tsaface da kuma aljanu na dan sha wahala, musamman a kan aljanin da ke jikin yarinyar tun da ba jinsina ba ne, na dan sha wahala wajen ganin na rubuta abin da yake tamkar a zahiri.

Cikin labaran da ki ka rubuta ko akwai wanda ki ka buga?

Eh Alhamdu lillah akwai wata gasa da aka saka wani malaminmu ne a nan online na shiga cikin mutum biyar da aka buga wa labaransu, an buga mini BAKAR FURA… kuma ni ma na saka kudi aka kara yi min wasu, daga baya kuma na buga MU GANI A KASA… shi ma.

Za mu ci gaba mako mai zuwa

MASU ALAKA

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Zambar Kudi: Kotu Ta Tasa Keyar Dillalin Gidaje Zuwa Gidan Kaso
Adabi

EFCC Ta Kama Mutum 11 Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba A Kwara

February 6, 2026
CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki
Adabi

CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki

January 30, 2026
Next Post
nauru

Ministan Harkokin Wajen Nauru: Dawo Da Huldar Diplomasiyya Tsakanin Sin Da Nauru Muhimmin Lokaci Ne A Tarihi

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.