• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Kaddamar Aikin Titi Mai Tsawon Kilomita 1000 Daga Sakkwato, Kebbi Zuwa Legas 

by Umar Faruk Birnin Kebbi
12 months ago
in Labarai
0
Minista Ya Kaddamar Aikin Titi Mai Tsawon Kilomita 1000 Daga Sakkwato, Kebbi Zuwa Legas 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi, ya kaddamar da babban titin Sokoto-Badagary mai tsawon kilomita 258 a Jihar Kebbi mai nisan kilomita 120.

Da yake kaddamar da ayyukan titunan a ranar Laraba a Birnin Kebbi, ministan ya ce idan aka kammala ayyukan zai bunkasa tattalin arzikin kasar nan.

  • Kwastam Ta Sake Kama Makamai A Filin Jirgin Saman Legas
  • Mutum 2 Sun Mutu, An Kone Gidaje A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Jigawa

Ya ce za a shinfida titin mai tsawon kilomita 915, haka kuma titin zai kawo abubuwan more rayuwa, yayin da zai fassara zuwa ingantaccen ƙira, rage cunkoson ababen hawa da haɓaka aminci tsakanin jihohi da ma kasashen Afirka.

Sanata Umahi, ya bayyana cewa aikin shimfida titin zai ba da damar hada fasahohin zamani, da inganta tsarin sufuri mai inganci da dorewar kasuwanci a tsakanin jihohi da kasashen Afirka.

Minista

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

Ministan, ya ci gaba da bayyana cewa, ayyukan da aka tsara za su kaucewa matsalolin da lalacewar kalubalen hanyoyi da jama’ar kasar nan ke fuskanta.

Haka kuma za a dauki tsawon lokaci kafin fuskanta matsalar gyaran hanyoyin da ake fama da su a shekarun baya, yayin da hanyar za ta ratsa jihohi bakwai da suka hada da; Jihar Kebbi mai fadin titin kilomita 258.

Ya kara da cewa za a yi ta ne ta hanyar Katami, Dabai, Gudale, Jabaka, Argungu, Ambursa, Gwandu, Tambuwal, Kambaza, Aliero, Jega, Maiyema, Karaye, Suru Asarara da Kwaifa.

Sauran sun hada da; Kalgo, Dakingari, Zagga, Bagudo, Gendini, Yamusa, Kwasara, Bahindi, Gwamba, Ka’oje da Buya, inda ya ce hakan zai hada da kara kaimi zuwa Birnin Kebbi.

Minista Umahi, ya yaba wa kokarin gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris bisa jajircewarsa na ganin an samu ci gaba cikin sauri a jihar.

“Na gamsu da ayyukan raya kasa na wannan gwamnati, nan ba da dadewa ba Jihar Kebbi za ta yi gogayya da Amurka, kan samun ayyukan masu amfani ga jama’ar jihar,” in ji shi.

Minista

A nasa jawabin gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris ya gode wa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, kan ajandar sabunta begensa, inda ya kara da cewa ajandar na da tasiri kai-tsaye ga rayuwar talakawan kasar nan.

Ya yaba da kokarin Ministocin Ayyuka, Kasafin Kudi da Tsare-Tsare Tattalin Arziki da karamin Ministan Ilimi da kuma ‘yan Majalisar Dokoki ta Kasa (Sanatoci da Wakilai) bisa gagarumin goyon bayan da suke bayarwa wajen cimma manufofin da aka ambata.

“Mun gamsu da manufa da hangen nesa na Shugaban kasa kan ‘Renewed Hope Agenda’, shiri ne da ya taba rayuwar ‘yan Nijeriya, muna biyayya ga APC daga sama har kasa,” in ji shi.

Minista

Wadanda suka gabatar da jawabai a wajen taron sun hada da; Ministan Kasafin Kudi da Tsare Tattalin Arziki, Sanata Abubakar Atiku Bagudu, Sanata mai wakiltar Kebbi ta Tsakiya, Sanata Muhammadu Adamu Aliero, tsohon Gwamnan Jihar Kebbi, Alhaji Sa’idu Usman Dakingari, Shugaban Kwamitin Ayyuka na Majalisar Dattawa, Shugaban Kwamitin Ayyuka na Majalisar dokokin na tarayya, Sanata Aminu Waziri Tambuwal da sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KebbiƘaddamar Da AikiMinistaTiti
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwastam Ta Sake Kama Makamai A Filin Jirgin Saman Legas

Next Post

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen Sin-SCO A Astana

Related

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

2 hours ago
Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga
Labarai

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

4 hours ago
Kawayen amarya
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

6 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Labarai

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

8 hours ago
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

10 hours ago
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC
Labarai

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

19 hours ago
Next Post
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen Sin-SCO A Astana

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen Sin-SCO A Astana

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

June 26, 2025
Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

June 26, 2025
Kawayen amarya

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

June 26, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

June 26, 2025
Tinubu

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

June 26, 2025
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

June 25, 2025
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

June 25, 2025
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

June 25, 2025
MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

June 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.