• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Duƙufa Tabbatar Da Tsaron Iyakokin Nijeriya – CGI Isah Jere

Ya Ziyarci Jami'an NIS Da Aka Farmake Su A Jigawa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Mun Duƙufa Tabbatar Da Tsaron Iyakokin Nijeriya – CGI Isah Jere
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa, CGI Isah Jere Idris ya bayyana cewa sun duƙufa a kan tabbatar da tsaron iyakokin Nijeriya da ya kai tsawon kilomita sama da 5000 a sassan ƙasar domin zaman lafiya da ci gaban ƙasa.

Ya bayyana haka ne lokacin da ya ziyarci Jihar Jigawa a yau Asabar domin ta’aziyya da kuma jaje ga jami’an hukumar da ‘yan bindiga suka kai wa hari a ranar 9 ga Agustan 2022.

Tsaro
CGI Isah Jere (a tsakiya) tare da tawagarsa a fadar mai martaba Sarkin Dutse da ke Jihar Jigawa

A wani jawabi da ya yi wa manema labarai, CGI Isah Jere ya bayyana cewa, “Bari na sake jaddada cewa mun duƙufa a kan tabbatar da tsaron iyakokin ƙasar nan babu fashi, za mu ƙara himma da ƙwazo a wannan bangaren. Za mu cigaba da tabbatar da kare dukkanin iyakokin Nijeriya domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali kasar nan.”

  • Yadda Tsare-tsaren Gwamnatin Tarayya Suka Habaka Noma A Nijeriya

Kwanturola Janar na hukumar ta NIS ya sanar da cewa yanzu haka suna amfani da na’urorin zamani wajen inganta aikin tsaron iyakokin kasa.

Isah Jere Idris ya nemi hadin kan jama’a wajen cimma nasarori kan harkokin tsaro, “Muna neman haɗin guiwar jama’a da ‘yan jarida wajen cimma nasarorin inganta tsaro.”

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

Tsaro
CGI Isah Jere (a tsakiya) da sauran jami’an NIS na reshen Jihar Jigawa

Ya ƙara da cewa yanzu haka hukumar ta maida hankali wajen amfani da fasahar zamani wajen kyautatawa da inganta tsaro a iyakokin kasar nan.

Jere ya ce ya ziyarci Jihar Jigawa ce domin ganawa da jami’ansa na jihar tare da jajanta wa iyalan jami’insa Abdullahi Mohammed da ya rasu a lokacin da yake bakin aikinsa na kare ƙasa.

“Na zo nan Jigawa domin jinjina irin ƙwazo da ƙoƙari da haziƙancin jami’inmu bisa sadaukar da kai da jarumtarsa wajen kare kasar nan da kiyaye kimarta. Za mu ci gaba da tuna Abdullahi Mohammed a matsayin jarumi kuma haziki. Ina tabbatar wa iyalan mamacin cewa tabbas jininsa bai tafi a banza ba. Muna addu’ar Allah ya jikansa ya gafarta masa.”

A cewarsa: “Marigayi Abdullahi Mohammed da abokan aikinsa suna sintiri ne a hanyar Galadi zuwa Birniwa a ranar 9 ga watan Agustan 2022 yayin da wasu marasa kishin ƙasa suka kai musu farmaki a yayin da suke bakin aikinsu. Shi Abdullahi da abokan aikinsa irin su Abba Musa Kiyawa (DSI) da Zubairu Garba (AII) sun jajirce tare da mayar da martani ga waɗanda suka kawo musu harin, abin takaici ya gamu da raunuka sakamakon hakan ya rigamu gidan gaskiya.”

Kazalika, Jere ya kai irin wannan ziyarar ta jajantawa ga sauran abokan aikinsu biyu da suka gamu da raunuka a sakamakon harin, “Suna amsar kulawar Likitoci a nan Jigawa. Tun lokacin da na karɓi ragamar shugabanci na mayar sha’anin kula da jin daɗi da walwalar jami’aina a matsayin abu mai matukar muhimmanci a tsare-tsarena.”

Shugaban hukumar ta NIS ula ya kuma shaida cewar, kyautata jin dadi da walwalar jami’an hukumar shi ne ya sanya a gaba kuma ya bai wa muhimmanci domin tabbatar da jami’an na samun yanayin gudanar da aiki yadda ya kamata.

Ya ce, yana tabbatar da kula da jin dadin nasu ne domin ba su ƙwarin guiwar gudanar da ayyukansu yadda ya dace don tabbatar da kare kasa a kowani lokaci, “Kuma na himmatu a wannan fannin zan kuma ci gaba tabbatar da jami’aina na samun kyakkyawar yanayin aiki a kowani lokaci.”

Shugaban ya ƙara da cewa irin wannan kulawar tasa ce ma ta sanya shi da kansa ya kai ziyarar ta’aziyyar jami’insa da ya rasa ransa a fagen aiki tare da ziyarartar wadanda suka jikkata a gadon asibiti duk da tarin ayyukan da suke gabansa amma ya jingine su don kai wannan ziyarar.

Tsaro
CGI Isah Jere Idris yayin da aka tarbe shi a Dutse, Jihar Jigawa

A wani labarin kuma wani kamfanin da ke harkar ƙawance da hukumar ta NIS wato Contect Global Services Ltd ya ba da tallafin naira miliyan huɗu (N4,000,000) ga iyalan mamacin da kuma wadanda suke jinya.

CGI Isah Jere dai ya sake nanata aniyar NIS ta ba da muhimmanci sosai ga tsaron iyakoki domin tallafa wa tsaron ƙasa da samun ci gaba mai ma’ana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kama Sojoji 2 Kan Zargin Suna Da Hannu A Kisan Wani Malamin Addinin Musulunci A Yobe

Next Post

Takaddamar Da Ake Yi Kan Binne Shugabannin Afirka Bayan Sun Mutu

Related

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

49 minutes ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

3 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

4 hours ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

12 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

12 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

14 hours ago
Next Post
Takaddamar Da Ake Yi Kan Binne Shugabannin Afirka Bayan Sun Mutu

Takaddamar Da Ake Yi Kan Binne Shugabannin Afirka Bayan Sun Mutu

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.