ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Duƙufa Tabbatar Da Tsaron Iyakokin Nijeriya – CGI Isah Jere

Ya Ziyarci Jami'an NIS Da Aka Farmake Su A Jigawa

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Tsaro

Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa, CGI Isah Jere Idris ya bayyana cewa sun duƙufa a kan tabbatar da tsaron iyakokin Nijeriya da ya kai tsawon kilomita sama da 5000 a sassan ƙasar domin zaman lafiya da ci gaban ƙasa.

Ya bayyana haka ne lokacin da ya ziyarci Jihar Jigawa a yau Asabar domin ta’aziyya da kuma jaje ga jami’an hukumar da ‘yan bindiga suka kai wa hari a ranar 9 ga Agustan 2022.

Tsaro
CGI Isah Jere (a tsakiya) tare da tawagarsa a fadar mai martaba Sarkin Dutse da ke Jihar Jigawa

A wani jawabi da ya yi wa manema labarai, CGI Isah Jere ya bayyana cewa, “Bari na sake jaddada cewa mun duƙufa a kan tabbatar da tsaron iyakokin ƙasar nan babu fashi, za mu ƙara himma da ƙwazo a wannan bangaren. Za mu cigaba da tabbatar da kare dukkanin iyakokin Nijeriya domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali kasar nan.”

ADVERTISEMENT
  • Yadda Tsare-tsaren Gwamnatin Tarayya Suka Habaka Noma A Nijeriya

Kwanturola Janar na hukumar ta NIS ya sanar da cewa yanzu haka suna amfani da na’urorin zamani wajen inganta aikin tsaron iyakokin kasa.

Isah Jere Idris ya nemi hadin kan jama’a wajen cimma nasarori kan harkokin tsaro, “Muna neman haɗin guiwar jama’a da ‘yan jarida wajen cimma nasarorin inganta tsaro.”

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

Tsaro
CGI Isah Jere (a tsakiya) da sauran jami’an NIS na reshen Jihar Jigawa

Ya ƙara da cewa yanzu haka hukumar ta maida hankali wajen amfani da fasahar zamani wajen kyautatawa da inganta tsaro a iyakokin kasar nan.

Jere ya ce ya ziyarci Jihar Jigawa ce domin ganawa da jami’ansa na jihar tare da jajanta wa iyalan jami’insa Abdullahi Mohammed da ya rasu a lokacin da yake bakin aikinsa na kare ƙasa.

“Na zo nan Jigawa domin jinjina irin ƙwazo da ƙoƙari da haziƙancin jami’inmu bisa sadaukar da kai da jarumtarsa wajen kare kasar nan da kiyaye kimarta. Za mu ci gaba da tuna Abdullahi Mohammed a matsayin jarumi kuma haziki. Ina tabbatar wa iyalan mamacin cewa tabbas jininsa bai tafi a banza ba. Muna addu’ar Allah ya jikansa ya gafarta masa.”

A cewarsa: “Marigayi Abdullahi Mohammed da abokan aikinsa suna sintiri ne a hanyar Galadi zuwa Birniwa a ranar 9 ga watan Agustan 2022 yayin da wasu marasa kishin ƙasa suka kai musu farmaki a yayin da suke bakin aikinsu. Shi Abdullahi da abokan aikinsa irin su Abba Musa Kiyawa (DSI) da Zubairu Garba (AII) sun jajirce tare da mayar da martani ga waɗanda suka kawo musu harin, abin takaici ya gamu da raunuka sakamakon hakan ya rigamu gidan gaskiya.”

Kazalika, Jere ya kai irin wannan ziyarar ta jajantawa ga sauran abokan aikinsu biyu da suka gamu da raunuka a sakamakon harin, “Suna amsar kulawar Likitoci a nan Jigawa. Tun lokacin da na karɓi ragamar shugabanci na mayar sha’anin kula da jin daɗi da walwalar jami’aina a matsayin abu mai matukar muhimmanci a tsare-tsarena.”

Shugaban hukumar ta NIS ula ya kuma shaida cewar, kyautata jin dadi da walwalar jami’an hukumar shi ne ya sanya a gaba kuma ya bai wa muhimmanci domin tabbatar da jami’an na samun yanayin gudanar da aiki yadda ya kamata.

Ya ce, yana tabbatar da kula da jin dadin nasu ne domin ba su ƙwarin guiwar gudanar da ayyukansu yadda ya dace don tabbatar da kare kasa a kowani lokaci, “Kuma na himmatu a wannan fannin zan kuma ci gaba tabbatar da jami’aina na samun kyakkyawar yanayin aiki a kowani lokaci.”

Shugaban ya ƙara da cewa irin wannan kulawar tasa ce ma ta sanya shi da kansa ya kai ziyarar ta’aziyyar jami’insa da ya rasa ransa a fagen aiki tare da ziyarartar wadanda suka jikkata a gadon asibiti duk da tarin ayyukan da suke gabansa amma ya jingine su don kai wannan ziyarar.

Tsaro
CGI Isah Jere Idris yayin da aka tarbe shi a Dutse, Jihar Jigawa

A wani labarin kuma wani kamfanin da ke harkar ƙawance da hukumar ta NIS wato Contect Global Services Ltd ya ba da tallafin naira miliyan huɗu (N4,000,000) ga iyalan mamacin da kuma wadanda suke jinya.

CGI Isah Jere dai ya sake nanata aniyar NIS ta ba da muhimmanci sosai ga tsaron iyakoki domin tallafa wa tsaron ƙasa da samun ci gaba mai ma’ana.

Tsaro
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

MASU ALAKA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya
Labarai

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Next Post
Takaddamar Da Ake Yi Kan Binne Shugabannin Afirka Bayan Sun Mutu

Takaddamar Da Ake Yi Kan Binne Shugabannin Afirka Bayan Sun Mutu

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.