ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takaddamar Da Ake Yi Kan Binne Shugabannin Afirka Bayan Sun Mutu

by Sulaiman
4 years ago
Afirka

Cikin jerin bayanai daga ‘yan jaridar Afirka, ‘yar Ghana Elizabeth Ohene ta yi rubutu game da irin rikicin da ake yi kafin binne shugabannin Afirka.

“Ba ni da tabbas ko zan iya ba da wani taKadirin zance, amma ni ban taba sanin cewa kasancewar mutum shugaban wata Kasa a Afirka zai iya haddasa rigima a Kabarinsa ba idan ya rasu.

  • Masanin Masar: Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Wani “Karfi Ne Dake Ingzia Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

Na yi ta bin rikicin da ake yi game da inda za a binne Tsohon Shugaban Kasar Angola José Eduardo dos Santos, wanda ya rasu a Sifaniya ranar 8 ga watan Yuli.

ADVERTISEMENT

Shugaban Kasar mai-ci João Lourenço da kuma matar Dos Santos na son a mayar da gawarsa gida don yi mata jana’izar ban-girma a Kasaitacciyar maKabarta ta musamman – abin da muke gani na girmamawa ga shugabanni a Ghana.

Amma ‘yarsa mai suna Welwitschia “Tchizé” na son a yi masa jana’iza a killace kuma a binne shi a wani Kabari na musamman a Sifaniya ta yadda ‘ya’yansa za su iya ziyartarsa,” in ji ta.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Ta ce wasu daga cikin ‘yan uwanta na goyon bayan Kudirin nata, wadanda ke fuskantar zargin cin hanci kuma za a iya kama su da zarar sun saka Kafa a Angola.

Daya daga cikin ‘ya’yan Dos Santos ya ce ba Kasar ce ke da alhakin daukar nauyin jana’izarsa ba kuma iyalinsa ne ya kamata su yanke hukunci.

Maganar cewa ko Kasa na da iko kan gawar shugabanta ba sabon abu ba ne.
An samu irin wannan lamari a Zimbabwe a 2019, lokacin da Robert Mugabe ya rasu shekara kusan biyu da suka wuce bayan ya shekara 37 a kan mulki – inda shugaba mai-ci Emmerson Mnangagwa ya kawo Karshen mulkin nasa tare da goyon bayan sojoji.

Kowa ya yi tunanin za a binne shi ne a Filin Gwaraza na Kasa ( Heroes’ Acre) da ke Birnin Harare.

Ko ma dai mene ne, shi ne ya gina Heroes’ Acre kuma ya binne da yawa daga cikin abokan gwagwarmayarsa, ciki har da Sally matarsa ta farko.

Mista Mnangagwa ya fara gina Kabari na musamman don binne jagoran neman ‘yancin, amma kuma iyalansa ba su amince da hakan ba ganin yadda aka kore shi daga mulki kuma abokan gwagwarmyarsa suka yaudare shi.

Bayan shafe makonni ana taKaddama, iyalinsa sun yi nasara kuma an binne Mista Mugabe, jagora kuma gwarzo a Zimbabwe, a Kauyensu ba tare da wani wakilin gwamnati ba.

Hatta Kenneth Kaunda – shugaban Kasa na farko bayan ‘yancin kai a Kasar Zambia kuma daya daga cikin ‘yan gwagwarmayar neman ‘yanci – bai iya samun wurin da za a binne shi ba ba tare da rikici ba.

A cewar iyalinsa, ya so a binne shi kusa da matarsa ba inda gwamnati ta tanada ba.

Zuwa yanzu dai iyalin nasa ba su yi wata jayayya ba yayin da “KK” – kamar yadda ake kiran sa da shi – na ci gaba da kwanciya a Embassy Memorial Park da ke Lusaka baban birnin Kasar.

Daga gudun hijira zuwa girmamawa
“Wadannan rikice-rikice kan gawarwaki ba sabbin abubuwa ba ne. A nan Ghana, mun saba da irin wannan.

Shugaban Kasarmu na farko Kwame Nkrumah ya rasu a Bucharest na Romania lokacin da yake jinya.
Da farko an binne shi a Conakry, Guinea bayan ya shafe lokaci yana gudun hijira a can. Daga baya aka mayar da gawarsa Ghana. An yi masa jana’izar gwamnati a Accra sannan aka binne shi a Kauyensu na Nkroful.

A lokuta daban-daban za ka dinga jin iyalansa na cewa a dawo musu da gawarsa.

A 2012, shugaban Kasarmu John Atta-Mills ya rasu yana kan mulki amma samun wurin da za a binne shi ya zama aiki.

Wasu daga cikin iyalansa sun nemi a kai gawarsa Kauyensu, sai dai ba su samu wani goyon baya ba a lokacin.

An Kyale wurin da gwamnati ta haKa a matsayin Kabarinsa saboda bai dace da shi ba. Daga baya aka mayar da shi wani wuri daban.

An tsara cewa wurin shaKatawar da aka binne shi ya zama maKabartar shugabannin Kasa.

Tun daga wannan lokaci, wani shugaban Kasar – Jerry Rwlings – yara su.
Ba kai shi wurin da aka binne Shugaba Atta-Mills kawai ba, iyalansa sun zargi gwamnati da aiwatar da hakan ba tare da izininsa ba.

An binne shi a maKabartar sojoji da ke Accra tare da yi masa jana’izar girmamawa.
‘Yan makonni da suka wuce muka yi bikin cika shekara 10 da mutuwar Atta-Mills.
Har yanzu ana cecekuce a kan kushewarsa: wane ne zai kula da ita kuma me za a rubuta a kanta.

Akwai kuma wasu daga iyalansa da ke son a tono gawarsa daga inda gwamnati ta binne shi a Accra zuwa Kuyensu don a sake binne shi.

Saboda haka ina ganin daya daga cikin matsalolin zama shugaban Kasa a Afirka ita ce ba lallai a samu wurin da za a binne mutum ba idan ya rasu,” a cewar ‘yar jaridar.

Afirka
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Yadda Za Ka Fara Sana’ar Sayar Da Data

Yadda Za Ka Fara Sana'ar Sayar Da Data

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.