ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takaddamar Da Ake Yi Kan Binne Shugabannin Afirka Bayan Sun Mutu

by Sulaiman
4 years ago
Afirka

Cikin jerin bayanai daga ‘yan jaridar Afirka, ‘yar Ghana Elizabeth Ohene ta yi rubutu game da irin rikicin da ake yi kafin binne shugabannin Afirka.

“Ba ni da tabbas ko zan iya ba da wani taKadirin zance, amma ni ban taba sanin cewa kasancewar mutum shugaban wata Kasa a Afirka zai iya haddasa rigima a Kabarinsa ba idan ya rasu.

  • Masanin Masar: Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Wani “Karfi Ne Dake Ingzia Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

Na yi ta bin rikicin da ake yi game da inda za a binne Tsohon Shugaban Kasar Angola José Eduardo dos Santos, wanda ya rasu a Sifaniya ranar 8 ga watan Yuli.

ADVERTISEMENT

Shugaban Kasar mai-ci João Lourenço da kuma matar Dos Santos na son a mayar da gawarsa gida don yi mata jana’izar ban-girma a Kasaitacciyar maKabarta ta musamman – abin da muke gani na girmamawa ga shugabanni a Ghana.

Amma ‘yarsa mai suna Welwitschia “Tchizé” na son a yi masa jana’iza a killace kuma a binne shi a wani Kabari na musamman a Sifaniya ta yadda ‘ya’yansa za su iya ziyartarsa,” in ji ta.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Ta ce wasu daga cikin ‘yan uwanta na goyon bayan Kudirin nata, wadanda ke fuskantar zargin cin hanci kuma za a iya kama su da zarar sun saka Kafa a Angola.

Daya daga cikin ‘ya’yan Dos Santos ya ce ba Kasar ce ke da alhakin daukar nauyin jana’izarsa ba kuma iyalinsa ne ya kamata su yanke hukunci.

Maganar cewa ko Kasa na da iko kan gawar shugabanta ba sabon abu ba ne.
An samu irin wannan lamari a Zimbabwe a 2019, lokacin da Robert Mugabe ya rasu shekara kusan biyu da suka wuce bayan ya shekara 37 a kan mulki – inda shugaba mai-ci Emmerson Mnangagwa ya kawo Karshen mulkin nasa tare da goyon bayan sojoji.

Kowa ya yi tunanin za a binne shi ne a Filin Gwaraza na Kasa ( Heroes’ Acre) da ke Birnin Harare.

Ko ma dai mene ne, shi ne ya gina Heroes’ Acre kuma ya binne da yawa daga cikin abokan gwagwarmayarsa, ciki har da Sally matarsa ta farko.

Mista Mnangagwa ya fara gina Kabari na musamman don binne jagoran neman ‘yancin, amma kuma iyalansa ba su amince da hakan ba ganin yadda aka kore shi daga mulki kuma abokan gwagwarmyarsa suka yaudare shi.

Bayan shafe makonni ana taKaddama, iyalinsa sun yi nasara kuma an binne Mista Mugabe, jagora kuma gwarzo a Zimbabwe, a Kauyensu ba tare da wani wakilin gwamnati ba.

Hatta Kenneth Kaunda – shugaban Kasa na farko bayan ‘yancin kai a Kasar Zambia kuma daya daga cikin ‘yan gwagwarmayar neman ‘yanci – bai iya samun wurin da za a binne shi ba ba tare da rikici ba.

A cewar iyalinsa, ya so a binne shi kusa da matarsa ba inda gwamnati ta tanada ba.

Zuwa yanzu dai iyalin nasa ba su yi wata jayayya ba yayin da “KK” – kamar yadda ake kiran sa da shi – na ci gaba da kwanciya a Embassy Memorial Park da ke Lusaka baban birnin Kasar.

Daga gudun hijira zuwa girmamawa
“Wadannan rikice-rikice kan gawarwaki ba sabbin abubuwa ba ne. A nan Ghana, mun saba da irin wannan.

Shugaban Kasarmu na farko Kwame Nkrumah ya rasu a Bucharest na Romania lokacin da yake jinya.
Da farko an binne shi a Conakry, Guinea bayan ya shafe lokaci yana gudun hijira a can. Daga baya aka mayar da gawarsa Ghana. An yi masa jana’izar gwamnati a Accra sannan aka binne shi a Kauyensu na Nkroful.

A lokuta daban-daban za ka dinga jin iyalansa na cewa a dawo musu da gawarsa.

A 2012, shugaban Kasarmu John Atta-Mills ya rasu yana kan mulki amma samun wurin da za a binne shi ya zama aiki.

Wasu daga cikin iyalansa sun nemi a kai gawarsa Kauyensu, sai dai ba su samu wani goyon baya ba a lokacin.

An Kyale wurin da gwamnati ta haKa a matsayin Kabarinsa saboda bai dace da shi ba. Daga baya aka mayar da shi wani wuri daban.

An tsara cewa wurin shaKatawar da aka binne shi ya zama maKabartar shugabannin Kasa.

Tun daga wannan lokaci, wani shugaban Kasar – Jerry Rwlings – yara su.
Ba kai shi wurin da aka binne Shugaba Atta-Mills kawai ba, iyalansa sun zargi gwamnati da aiwatar da hakan ba tare da izininsa ba.

An binne shi a maKabartar sojoji da ke Accra tare da yi masa jana’izar girmamawa.
‘Yan makonni da suka wuce muka yi bikin cika shekara 10 da mutuwar Atta-Mills.
Har yanzu ana cecekuce a kan kushewarsa: wane ne zai kula da ita kuma me za a rubuta a kanta.

Akwai kuma wasu daga iyalansa da ke son a tono gawarsa daga inda gwamnati ta binne shi a Accra zuwa Kuyensu don a sake binne shi.

Saboda haka ina ganin daya daga cikin matsalolin zama shugaban Kasa a Afirka ita ce ba lallai a samu wurin da za a binne mutum ba idan ya rasu,” a cewar ‘yar jaridar.

Afirka
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Yadda Za Ka Fara Sana’ar Sayar Da Data

Yadda Za Ka Fara Sana'ar Sayar Da Data

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.