• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Fara Shirin Lashe Firimiya Ta Gaba –Slot

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
5 months ago
in Wasanni
0
Mun Fara Shirin Lashe Firimiya Ta Gaba –Slot
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kociyan kungiyar kwallon kafa ta Liverpool, Arne Slot, ya bayyana cewa shirye-shirye sun yin isa wajen ganin sun sake lashe gasar firimiya ta kakar wasa mai zuwa wato kakar wasa ta 2025 zuwa 2026 domin dorawa daga nasarar da suka samu ta lashe gasar firimiya ta bana.

Slot ya bayyana haka ne jim kadan bayan ya jagoranci kungiyar Liberpool ta lashe Premier League na 2024 zuwa 2025 na 20 jimilla, bayan da ta caskara kungiyar kwallon kafa ta Tottenham 5-1 ranar Lahadi a filin wasa na Anfield.

  • Liverpool Sun Zama Zakaran Gasar Premier Bayan Lallasa Tottenham
  • Yadda Wasu Mata Ke Gallaza Wa ‘Ya’yansu Domin Bakanta Wa Mazajensu

Tottenham ce ta fara cin kwallo ta hannun Dominic Solanke minti 12 da fara wasa, sai dai minti hudu tsakani Liberpool ta farke ta hannun Luis Diaz, sannan Mac Allister ya kara ta biyu.

 

Daf da za su je hutu ne kuma sai kungiyar ta Liberpool ta kara kwallo ta uku ta hannun Cody Gakpo, sai Mohamed Salah ya kara ta hudu, sannan Tottenham ta ci gida ta hannun Destiny Udogie. Kenan Liverpool ta samu damar daukar kofin Premier League na bana na 20 jimilla, iri daya da yawan na Manchester United. Liverpool ta samu damar lashe kofin bana, saura wasa hudu-hudu a karkare gasar ta bana, bayan da Arsenal ta tashi 2-2 da Crystal Palace ranar Laraba a filin wasa na Emirates kuma Liberpool ta dauki Premier na bana da maki 82, bayan cin wasanni 25 da canjaras bakwai aka doke ta wasa biyu. Arsenal ce ta biyun teburi mai maki 67, bayan cin wasa 18 da canjaras 13 da rashin nasara uku a babbar gasar ta Ingila.

Labarai Masu Nasaba

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

 

Liverpool ta yi wannan kwazon karkashin sabon koci, Arne Slot da ta dauka kan a fara kakar nan, wanda ya maye gurbin Jurgen Klopp, wanda ya yi ritaya. Tun farko Liberpool ta yi fatan lashe kofi hudu a kakar nan, sai dai an yi waje da ita a League da FA Cup. Haka kuma ta yi ban kwana da Kofin Zakarun Turai na kakar nan, bayan da Paris St Germain ta yi waje da ita a zagaye na biyu.

 

Tuni dai an samu gurbi ukun da suka yi ban kwana da Premier League da za su koma buga Championship a badi da suka hada da Ipswich da Leicester da kuma Southampton.

 

Yanzu inda ake tata-burza shi ne gurbin da za su wakilci Ingila a badi a gasar zakarun Turai. Kungiya biyar ce za ta wakilci Ingila a badi a Kofin Zakarun Turai, yayin da watakila su zama shida da zarar Manchester United ko Tottenham daya a cikinsu ta lashe Europa League. Manchester United da Tottenham duk sun kai zagayen daf da karshe a Europa League.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Maniyyata Daga Turai Akan Dawakai Sun Isa Kasar Saudiyya Domin Yin Aikin Hajjin 2025

Next Post

Yawan Mutanen Da Suka Sayi Inshorar Kula Da Tsoffi A Kasar Sin Ya Zarce Biliyan 1.07 

Related

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or
Wasanni

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

6 hours ago
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya
Wasanni

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

9 hours ago
Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya
Wasanni

Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

12 hours ago
Lamine Yamal Zai Shafe Mako 3 Yana Jinya
Wasanni

Lamine Yamal Zai Shafe Mako 3 Yana Jinya

1 day ago
PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai
Wasanni

PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai

3 days ago
Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 
Wasanni

Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 

4 days ago
Next Post
Yawan Mutanen Da Suka Sayi Inshorar Kula Da Tsoffi A Kasar Sin Ya Zarce Biliyan 1.07 

Yawan Mutanen Da Suka Sayi Inshorar Kula Da Tsoffi A Kasar Sin Ya Zarce Biliyan 1.07 

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.