ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Fara Shirin Lashe Firimiya Ta Gaba –Slot

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
1 year ago
Slot

Kociyan kungiyar kwallon kafa ta Liverpool, Arne Slot, ya bayyana cewa shirye-shirye sun yin isa wajen ganin sun sake lashe gasar firimiya ta kakar wasa mai zuwa wato kakar wasa ta 2025 zuwa 2026 domin dorawa daga nasarar da suka samu ta lashe gasar firimiya ta bana.

Slot ya bayyana haka ne jim kadan bayan ya jagoranci kungiyar Liberpool ta lashe Premier League na 2024 zuwa 2025 na 20 jimilla, bayan da ta caskara kungiyar kwallon kafa ta Tottenham 5-1 ranar Lahadi a filin wasa na Anfield.

  • Liverpool Sun Zama Zakaran Gasar Premier Bayan Lallasa Tottenham
  • Yadda Wasu Mata Ke Gallaza Wa ‘Ya’yansu Domin Bakanta Wa Mazajensu

Tottenham ce ta fara cin kwallo ta hannun Dominic Solanke minti 12 da fara wasa, sai dai minti hudu tsakani Liberpool ta farke ta hannun Luis Diaz, sannan Mac Allister ya kara ta biyu.

ADVERTISEMENT

 

Daf da za su je hutu ne kuma sai kungiyar ta Liberpool ta kara kwallo ta uku ta hannun Cody Gakpo, sai Mohamed Salah ya kara ta hudu, sannan Tottenham ta ci gida ta hannun Destiny Udogie. Kenan Liverpool ta samu damar daukar kofin Premier League na bana na 20 jimilla, iri daya da yawan na Manchester United. Liverpool ta samu damar lashe kofin bana, saura wasa hudu-hudu a karkare gasar ta bana, bayan da Arsenal ta tashi 2-2 da Crystal Palace ranar Laraba a filin wasa na Emirates kuma Liberpool ta dauki Premier na bana da maki 82, bayan cin wasanni 25 da canjaras bakwai aka doke ta wasa biyu. Arsenal ce ta biyun teburi mai maki 67, bayan cin wasa 18 da canjaras 13 da rashin nasara uku a babbar gasar ta Ingila.

LABARAI MASU NASABA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

 

Liverpool ta yi wannan kwazon karkashin sabon koci, Arne Slot da ta dauka kan a fara kakar nan, wanda ya maye gurbin Jurgen Klopp, wanda ya yi ritaya. Tun farko Liberpool ta yi fatan lashe kofi hudu a kakar nan, sai dai an yi waje da ita a League da FA Cup. Haka kuma ta yi ban kwana da Kofin Zakarun Turai na kakar nan, bayan da Paris St Germain ta yi waje da ita a zagaye na biyu.

 

Tuni dai an samu gurbi ukun da suka yi ban kwana da Premier League da za su koma buga Championship a badi da suka hada da Ipswich da Leicester da kuma Southampton.

 

Yanzu inda ake tata-burza shi ne gurbin da za su wakilci Ingila a badi a gasar zakarun Turai. Kungiya biyar ce za ta wakilci Ingila a badi a Kofin Zakarun Turai, yayin da watakila su zama shida da zarar Manchester United ko Tottenham daya a cikinsu ta lashe Europa League. Manchester United da Tottenham duk sun kai zagayen daf da karshe a Europa League.

Slot
Abba Ibrahim Wada
Website |  + posts Bio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?
Slot
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Next Post
Yawan Mutanen Da Suka Sayi Inshorar Kula Da Tsoffi A Kasar Sin Ya Zarce Biliyan 1.07 

Yawan Mutanen Da Suka Sayi Inshorar Kula Da Tsoffi A Kasar Sin Ya Zarce Biliyan 1.07 

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.