• English
  • Business News
Tuesday, September 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Da Hujjojin Magudi A Zaben Fid Da Gwanin PDP Na Kaduna Ta Tsakiya – Lauya

by Shehu Yahaya
3 years ago
in Siyasa
0
Muna Da Hujjojin Magudi A Zaben Fid Da Gwanin PDP Na Kaduna Ta Tsakiya – Lauya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Lauyan dan takarar kujerar sanata a shiyyar Kaduna ta tsakiya, Honarabul Usman Ibrahim, wanda aka fi sani da Sardaunan Badarawa da ya fafata a zaben fid da gwani na jam’iyyar PDP da aka kammala, ya bayyana cewa yana rike da hujjojin faifan bidiyo da ke nuna yadda wakilai suka kada kuri’a da arangizon da aka yi a matsayin hujja.

Wani Babban Lauyan Nijeriya (SAN), Samuel Atung ne ya bayyana haka a wata hirar da ya yi da manema labarai a babban kotun tarayya da ke Kaduna.
Lauyan ya bayyana cewa zaben fid da gwanin da ya samar da Lawal Adamu (Mr. LA) a matsayin dan takarar jam’iyyar PDP na Kaduna ta tsakiya, an tafka kura-kurai da arangizon kuri’u.

  • Dokar Da Amurka Ta Sanya Mai Nasaba Da Xinjiang Alama Ce Ta Yunkurin Dakile Tsarin Masana’antun Kasa Da Kasa

Ya kara da cewa wanda yake karewa yana rike da hujjojin faifan bidiyo da na hoton da ke nuna yadda wakilai suka kada kuri’a da ya yi nuni da cewa sun ruguza sakamakon zaben fid da gwani na jam’iyyar PDP.

Ya ce “Bayan jam’iyyar PDP ta Kaduna ta tsakiya ta tsayar da dan takararta na zaben 2023, wanda shi da muke karewa ya rubuta koke ga kwamitin daukaka kara na jam’iyyar yana kalubalantar sakamakon zaben, mun shigar da karar kotu.

“Muna da hujjojin faifan bidiyo a kan haka kuma kwamitin ya yi la’akari da koken da muka yi tare da mika shawararsa ga kwamitin gudanarwa na jam’iyar, wanda a hikimarsa ya bukaci a sake zaben fid da gwani.

Labarai Masu Nasaba

Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike

Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai

“Jam’iyyar PDP ta rubuta wa INEC wasika, inda ta sanar da ‘yan sandan Nijeriya, jami’an tsaron farin kaya da sauran masu ruwa da tsaki kan matakin da ta dauka na sake gudanar da zaben fid da gwani na shiyyar sanatan Kaduna ta tsakiya, wanda abin farin ciki ne, sai kuma ba a yi hakan ba.”

“Abin takaici a ranar da aka saka za a yi zaben, shi wanda muke karewa ya tattaro magoya bayansa zuwa wurin da za a sake zaben fid da gwanin, sai aka ce ba za a sake gudanar da zaben ba saboda yadda jam’iyyar ta tsara kenan.

“Mun zo kotu ne muna neman a tilasta wa jam’iyyar PDP ta mika sunan kowane dan takara domin tabbatar da gaskiya da adalci a zaben 2023 har sai bayan an sake zaben fid da gwanin.

“Muna da kudirin dokar hana PDP mika sunan kowane dan takara ga INEC har sai an sake zaben fid da gwani”, in ji Lauyan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Birnin Legas Ya Zama Na Biyu Mafi Muni Wajen Yin Rayuwa A Duniya

Next Post

LEADERSHIP Ta Cika Shekara Daya Da Fara Gabatar Da Shirye-shiryen PODCAST

Related

Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike
Siyasa

Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike

23 hours ago
Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai
Siyasa

Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai

1 day ago
Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027
Siyasa

Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027

2 days ago
Peter Obi Ya Caccaki Gwamnati Kan Ƙarin Kuɗin Fasfo
Siyasa

Peter Obi Ya Caccaki Gwamnati Kan Ƙarin Kuɗin Fasfo

4 days ago
Ba Zan Nemi Kujerar Siyasa A 2027 Ba — El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Nemi Kujerar Siyasa A 2027 Ba — El-Rufai

5 days ago
ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi
Manyan Labarai

ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi

5 days ago
Next Post
LEADERSHIP Ta Cika Shekara Daya Da Fara Gabatar Da Shirye-shiryen PODCAST

LEADERSHIP Ta Cika Shekara Daya Da Fara Gabatar Da Shirye-shiryen PODCAST

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Masu Safarar Makamai A Katsina, Sun Ƙwato Makamai

September 2, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Sace Adaidaita Sahu A Borno

September 2, 2025
Zargin Cin Hanci: Babu Wani Shirin Tsige El-Rufai – Kakakin Majalisar Dokokin Kaduna

Gwamnatin Kaduna Ta Gargaɗi El-Rufai Kan Yunƙurin Tayar Da Rikici A Jihar

September 2, 2025
Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike

2027: Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Zawarcin Peter Obi

September 2, 2025
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Daba 107 A Kano, Sun Ƙwato Makamai Da Ƙwayoyi

September 2, 2025
Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

September 1, 2025
Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

September 1, 2025
Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

September 1, 2025
AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

September 1, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Ƙarin Kasafin Naira Biliyan 215.3 A Na 2025

September 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.