• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Da Hujjojin Magudi A Zaben Fid Da Gwanin PDP Na Kaduna Ta Tsakiya – Lauya

by Shehu Yahaya
3 years ago
PDP

Lauyan dan takarar kujerar sanata a shiyyar Kaduna ta tsakiya, Honarabul Usman Ibrahim, wanda aka fi sani da Sardaunan Badarawa da ya fafata a zaben fid da gwani na jam’iyyar PDP da aka kammala, ya bayyana cewa yana rike da hujjojin faifan bidiyo da ke nuna yadda wakilai suka kada kuri’a da arangizon da aka yi a matsayin hujja.

Wani Babban Lauyan Nijeriya (SAN), Samuel Atung ne ya bayyana haka a wata hirar da ya yi da manema labarai a babban kotun tarayya da ke Kaduna.
Lauyan ya bayyana cewa zaben fid da gwanin da ya samar da Lawal Adamu (Mr. LA) a matsayin dan takarar jam’iyyar PDP na Kaduna ta tsakiya, an tafka kura-kurai da arangizon kuri’u.

  • Dokar Da Amurka Ta Sanya Mai Nasaba Da Xinjiang Alama Ce Ta Yunkurin Dakile Tsarin Masana’antun Kasa Da Kasa

Ya kara da cewa wanda yake karewa yana rike da hujjojin faifan bidiyo da na hoton da ke nuna yadda wakilai suka kada kuri’a da ya yi nuni da cewa sun ruguza sakamakon zaben fid da gwani na jam’iyyar PDP.

Ya ce “Bayan jam’iyyar PDP ta Kaduna ta tsakiya ta tsayar da dan takararta na zaben 2023, wanda shi da muke karewa ya rubuta koke ga kwamitin daukaka kara na jam’iyyar yana kalubalantar sakamakon zaben, mun shigar da karar kotu.

“Muna da hujjojin faifan bidiyo a kan haka kuma kwamitin ya yi la’akari da koken da muka yi tare da mika shawararsa ga kwamitin gudanarwa na jam’iyar, wanda a hikimarsa ya bukaci a sake zaben fid da gwani.

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

“Jam’iyyar PDP ta rubuta wa INEC wasika, inda ta sanar da ‘yan sandan Nijeriya, jami’an tsaron farin kaya da sauran masu ruwa da tsaki kan matakin da ta dauka na sake gudanar da zaben fid da gwani na shiyyar sanatan Kaduna ta tsakiya, wanda abin farin ciki ne, sai kuma ba a yi hakan ba.”

“Abin takaici a ranar da aka saka za a yi zaben, shi wanda muke karewa ya tattaro magoya bayansa zuwa wurin da za a sake zaben fid da gwanin, sai aka ce ba za a sake gudanar da zaben ba saboda yadda jam’iyyar ta tsara kenan.

“Mun zo kotu ne muna neman a tilasta wa jam’iyyar PDP ta mika sunan kowane dan takara domin tabbatar da gaskiya da adalci a zaben 2023 har sai bayan an sake zaben fid da gwanin.

“Muna da kudirin dokar hana PDP mika sunan kowane dan takara ga INEC har sai an sake zaben fid da gwani”, in ji Lauyan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Next Post
LEADERSHIP Ta Cika Shekara Daya Da Fara Gabatar Da Shirye-shiryen PODCAST

LEADERSHIP Ta Cika Shekara Daya Da Fara Gabatar Da Shirye-shiryen PODCAST

LABARAI MASU NASABA

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.