ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

LEADERSHIP Ta Cika Shekara Daya Da Fara Gabatar Da Shirye-shiryen PODCAST

by Bello Hamza
4 years ago
LEADERSHIP

A ranar Laraba 22 ga watan Yuni 2022 Kamfanin LEADERSHIP ya cika shekara daya da fara gabatar da shirye-shirye ta hanyar manhajar PODCAST daga dakin watsa shiriye-shirye na zamani na LAST WORD a Abuja, Babban Birnin Tarayyar Nijeriya.

Mahukuntan kamfanin LEADRSHIP sun yi alkawarin kara inganta ayyukan bangaren don jagorantar kafafen watsa labarai na kasar nan a fannin yada labarai ta hanyoyi na zamani, musamman ganin yadda al’umma ke kishi da fatan samun sahihan labarai.

  • Mun Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kai Hari A Cocin Katolika Dake Ondo – Amotekun

Da yake tsokaci a kan cikar sashin shekara daya da kafuwa, shugaban shashen yada labarai na Kamfanin LEADERSHIP, Mista Bayo Amodu, ya ce, “shirye-shiryenmu na Podcast sun samar da mahanga ta musamman a tsarin gabatar da shirye-shirye ta kafafen sadarwa na zamani tun da aka kafa ta, don haka muna yi wa masu bibiyarmu alkawarin inganta yadda ake gabatar da shirye-shirye don samar musu da hirye-shirye masu kayatarwa, ilimantarwa da fadakarwa a cikin shekaru masu zuwa.
“A ranar Laraba 22 ga watan Yuni 2022, aka fara gabatar da shirye-shirye daga dakin watsa shirye-shiryenmu na Podcast.

ADVERTISEMENT

Dalilan fara shirin ta hanyar wannan tsari shi ne yadda muka lura da cewa, bangaren gabatar da shirye-shirye ta kafafen sadarwa na zamani babu kwararrun ‘yan jarida a ciki, galibin masu yi suna kiran kansu da sunaye iri iri, ba sa yin cikakken bincike wajen gabatar da labarunsu, ta haka kuma suke watsa labarai marasa inganci ga al’umma.

“Ina sane da wurare daban-daban da labarun kanzon kurege suka haifar da matsaloli ga al’ummar Nijeriya da dama. Amma mu a Kamfanin LEADERSHIP an san mu da samar da ingattun labarai, mun kuma dade a fagen harkar watsa labarai a kan haka muka shigo don cike gurbin da al’umma ke bukata a fagen watsa labarai ta kafafen sadarwa na zamani.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

“Mun yi gaggarumin kokari a cikin shekarar da ta wuce. Mun samar da tsari na musamman a bangaren aikin jarida ta kafafen sadarwa na zamani, yawan mutane da ke bibiyarmu da kuma sakonnin da muke samu a kullum shaida ne ga yada aka karbe mu, yana kuma nuna irin kokarinmu a wannan fagen.
“Mun samar da shirye-shirye da dama, muna ci gaba da inganta su tare da tsayuwa a kan bayar da sahihan labarai. Za mu nisanci dukkan nau’in labarun kazon kurege, za kuma mu tabbatar da kowa ya samu hakkin fadar albarkacin bakinsa a dukkan lokaci,” in ji shi.

Mista Amodu ya kuma bayana cewa, bayan shirye-shirye ta Podcast, Kamfanin LEADERSHIP Group Limited, na kuma jagorantar buga Jaridar LEADERSHIP Daily, LEADERSHIP Weekend, LEADERSHIP Sunday, LEADERSHIP Hausa da kuma National Economy.

Daga cikin manya manyan shirye shiryen da ake gabatarwa a dakin watsa shirye-shiryen na LAST WORD akwai shirin sashashin Hausa na LEADERSHIP mai lakabin ‘BARKA DA HANTSI NIJERIYA’ wanda ake gabatarwa da misalin karfe 9 na safe daga Litinin har zuwa Juma’a kai-tsaye ta kafofin Facebook a “Leadership Hausa”, YouTube a “Leadership Hausa”, sai kafar Twitter a “@Leadershiphausa”.

LEADERSHIP
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Hadin Gwiwar BRICS Ya Kai Matsayin Koli

Hadin Gwiwar BRICS Ya Kai Matsayin Koli

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.