ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

LEADERSHIP Ta Cika Shekara Daya Da Fara Gabatar Da Shirye-shiryen PODCAST

by Bello Hamza
4 years ago
LEADERSHIP

A ranar Laraba 22 ga watan Yuni 2022 Kamfanin LEADERSHIP ya cika shekara daya da fara gabatar da shirye-shirye ta hanyar manhajar PODCAST daga dakin watsa shiriye-shirye na zamani na LAST WORD a Abuja, Babban Birnin Tarayyar Nijeriya.

Mahukuntan kamfanin LEADRSHIP sun yi alkawarin kara inganta ayyukan bangaren don jagorantar kafafen watsa labarai na kasar nan a fannin yada labarai ta hanyoyi na zamani, musamman ganin yadda al’umma ke kishi da fatan samun sahihan labarai.

  • Mun Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kai Hari A Cocin Katolika Dake Ondo – Amotekun

Da yake tsokaci a kan cikar sashin shekara daya da kafuwa, shugaban shashen yada labarai na Kamfanin LEADERSHIP, Mista Bayo Amodu, ya ce, “shirye-shiryenmu na Podcast sun samar da mahanga ta musamman a tsarin gabatar da shirye-shirye ta kafafen sadarwa na zamani tun da aka kafa ta, don haka muna yi wa masu bibiyarmu alkawarin inganta yadda ake gabatar da shirye-shirye don samar musu da hirye-shirye masu kayatarwa, ilimantarwa da fadakarwa a cikin shekaru masu zuwa.
“A ranar Laraba 22 ga watan Yuni 2022, aka fara gabatar da shirye-shirye daga dakin watsa shirye-shiryenmu na Podcast.

ADVERTISEMENT

Dalilan fara shirin ta hanyar wannan tsari shi ne yadda muka lura da cewa, bangaren gabatar da shirye-shirye ta kafafen sadarwa na zamani babu kwararrun ‘yan jarida a ciki, galibin masu yi suna kiran kansu da sunaye iri iri, ba sa yin cikakken bincike wajen gabatar da labarunsu, ta haka kuma suke watsa labarai marasa inganci ga al’umma.

“Ina sane da wurare daban-daban da labarun kanzon kurege suka haifar da matsaloli ga al’ummar Nijeriya da dama. Amma mu a Kamfanin LEADERSHIP an san mu da samar da ingattun labarai, mun kuma dade a fagen harkar watsa labarai a kan haka muka shigo don cike gurbin da al’umma ke bukata a fagen watsa labarai ta kafafen sadarwa na zamani.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

“Mun yi gaggarumin kokari a cikin shekarar da ta wuce. Mun samar da tsari na musamman a bangaren aikin jarida ta kafafen sadarwa na zamani, yawan mutane da ke bibiyarmu da kuma sakonnin da muke samu a kullum shaida ne ga yada aka karbe mu, yana kuma nuna irin kokarinmu a wannan fagen.
“Mun samar da shirye-shirye da dama, muna ci gaba da inganta su tare da tsayuwa a kan bayar da sahihan labarai. Za mu nisanci dukkan nau’in labarun kazon kurege, za kuma mu tabbatar da kowa ya samu hakkin fadar albarkacin bakinsa a dukkan lokaci,” in ji shi.

Mista Amodu ya kuma bayana cewa, bayan shirye-shirye ta Podcast, Kamfanin LEADERSHIP Group Limited, na kuma jagorantar buga Jaridar LEADERSHIP Daily, LEADERSHIP Weekend, LEADERSHIP Sunday, LEADERSHIP Hausa da kuma National Economy.

Daga cikin manya manyan shirye shiryen da ake gabatarwa a dakin watsa shirye-shiryen na LAST WORD akwai shirin sashashin Hausa na LEADERSHIP mai lakabin ‘BARKA DA HANTSI NIJERIYA’ wanda ake gabatarwa da misalin karfe 9 na safe daga Litinin har zuwa Juma’a kai-tsaye ta kafofin Facebook a “Leadership Hausa”, YouTube a “Leadership Hausa”, sai kafar Twitter a “@Leadershiphausa”.

LEADERSHIP
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

LEADERSHIP
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
LEADERSHIP
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Hadin Gwiwar BRICS Ya Kai Matsayin Koli

Hadin Gwiwar BRICS Ya Kai Matsayin Koli

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.