ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutane 19,000 Sun Amfana Da Tallafin Fadama III A Zamfara

by Hussein Yero
2 years ago
Zamfara

Gwamna Dauda Lawal, a jiya Laraba, ya kaddamar da shirin farfado da tattalin arziki na shirin (N-CARES) na Nijeriya Coronavirus (COVID-19) tare da rarraba kayan amfanin gona da kadarorin noma ga mutane 19,000.

An gudanar da bikin kaddamar da shirin na Fadama III a ma’aikatar noma ta Jihar Zamfara, kuma mutane daga kananan hukumomi shida ne suka amfana da shirin.

  • Masu Fyade Da ’Yan Luwadi 369 Aka Kama A 2023 A Katsina
  • Tsohuwar Ministar Ayyukan Jin-Kai Ta Ki Amsa Gayyatar EFCC

A wajen bikin an raba sama da injinan wutar lantarki 700 da iri na shinkafa da masara ga manoma 19,000.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, gwamnatin Gwamna Dauda Lawal ta kuduri aniyar inganta harkar noma ta hanyar samar da isasshen tallafi ga manoma.

A yayin jawabinsa a wajen taron kaddamarwar, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada kudirin gwamnatinsa na samar da ayyukan yi ga marasa karfi a Zamfara.

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Ya ce: “Ta hanyar shirin Fadama III, manoma 100,000 ne za a karfafa musu kayan aiki da iri a cikin shekaru hudu masu zuwa, kuma wannan yana ciki kasafin kudin cetonmu na 2024, ya shaida kudurisa na daukar matakan da ake bukata domin ganinmun cimma burinmu a fannin noma, wanda shi ne bangare mafi muhimmanci na tattalin arzikin jiharmu.

“Kamar yadda kuka sani, shirin COVID-19 shiri ne na farfado da tattalin arziki shiri ne da ya kunshi bangarori daban-daban da ke kewaye da yankuna uku masu muhimmanci kuma an tsara shi don magance kalubale da samun damar yin amfani da damar inganta noma.

“A karkashin FADAMA 3, yankin zai mayar da hankali ne kan inganta samar da abinci da kuma tabbatar da amintaccen aikin samar da abinci ga gidajenmu masu rauni.”

Bugu da kari, Gwamna Lawal ya ce gwamnatin Jihar Zamfara za ta bayar da tallafi da ayyuka masu muhimmanci, da ginawa da gyara hanyoyin shiga, tare da ware kadarori domin noma da rage asarar abinci”.

“A wannan zagaye na uku, babban burinmu shi ne mu inganta ayyukan noma 11,760 kai tsaye ta hanyar samar musu da muhimman abubuwa kamar takin zamani, maganin ciyawa, maganin kwari, ingantattun iri, da sinadarai masu sanya iri. Domin noman rani mai zuwa, mun ware buhunan taki 33,000 – wanda ya kunshi buhunan NPK 22,000 da kuma buhunan Urea 11,000.

“Haka zalika, za a raba injinan wutar lantarki sama da 700 da iri na shinkafa da masara ga manoma 19,000. Bugu da kari, kungiyoyi 735 na manoma goma kowannen su za a ba su na’urar wutar lantarki, kuma mutane 2,550 za su karbi kananan dabbobi.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN
Labarai

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Next Post
Majalisa Ta Amince Tinubu Ya Ciwo Bashin Naira Tiriliyan 7.5

Majalisa Ta Amince Tinubu Ya Ciwo Bashin Naira Tiriliyan 7.5

LABARAI MASU NASABA

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

December 20, 2025
An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.