• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutane 19,000 Sun Amfana Da Tallafin Fadama III A Zamfara

by Hussein Yero
2 years ago
Zamfara

Gwamna Dauda Lawal, a jiya Laraba, ya kaddamar da shirin farfado da tattalin arziki na shirin (N-CARES) na Nijeriya Coronavirus (COVID-19) tare da rarraba kayan amfanin gona da kadarorin noma ga mutane 19,000.

An gudanar da bikin kaddamar da shirin na Fadama III a ma’aikatar noma ta Jihar Zamfara, kuma mutane daga kananan hukumomi shida ne suka amfana da shirin.

  • Masu Fyade Da ’Yan Luwadi 369 Aka Kama A 2023 A Katsina
  • Tsohuwar Ministar Ayyukan Jin-Kai Ta Ki Amsa Gayyatar EFCC

A wajen bikin an raba sama da injinan wutar lantarki 700 da iri na shinkafa da masara ga manoma 19,000.

A cewarsa, gwamnatin Gwamna Dauda Lawal ta kuduri aniyar inganta harkar noma ta hanyar samar da isasshen tallafi ga manoma.

A yayin jawabinsa a wajen taron kaddamarwar, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada kudirin gwamnatinsa na samar da ayyukan yi ga marasa karfi a Zamfara.

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Ya ce: “Ta hanyar shirin Fadama III, manoma 100,000 ne za a karfafa musu kayan aiki da iri a cikin shekaru hudu masu zuwa, kuma wannan yana ciki kasafin kudin cetonmu na 2024, ya shaida kudurisa na daukar matakan da ake bukata domin ganinmun cimma burinmu a fannin noma, wanda shi ne bangare mafi muhimmanci na tattalin arzikin jiharmu.

“Kamar yadda kuka sani, shirin COVID-19 shiri ne na farfado da tattalin arziki shiri ne da ya kunshi bangarori daban-daban da ke kewaye da yankuna uku masu muhimmanci kuma an tsara shi don magance kalubale da samun damar yin amfani da damar inganta noma.

“A karkashin FADAMA 3, yankin zai mayar da hankali ne kan inganta samar da abinci da kuma tabbatar da amintaccen aikin samar da abinci ga gidajenmu masu rauni.”

Bugu da kari, Gwamna Lawal ya ce gwamnatin Jihar Zamfara za ta bayar da tallafi da ayyuka masu muhimmanci, da ginawa da gyara hanyoyin shiga, tare da ware kadarori domin noma da rage asarar abinci”.

“A wannan zagaye na uku, babban burinmu shi ne mu inganta ayyukan noma 11,760 kai tsaye ta hanyar samar musu da muhimman abubuwa kamar takin zamani, maganin ciyawa, maganin kwari, ingantattun iri, da sinadarai masu sanya iri. Domin noman rani mai zuwa, mun ware buhunan taki 33,000 – wanda ya kunshi buhunan NPK 22,000 da kuma buhunan Urea 11,000.

“Haka zalika, za a raba injinan wutar lantarki sama da 700 da iri na shinkafa da masara ga manoma 19,000. Bugu da kari, kungiyoyi 735 na manoma goma kowannen su za a ba su na’urar wutar lantarki, kuma mutane 2,550 za su karbi kananan dabbobi.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
Labarai

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Next Post
Majalisa Ta Amince Tinubu Ya Ciwo Bashin Naira Tiriliyan 7.5

Majalisa Ta Amince Tinubu Ya Ciwo Bashin Naira Tiriliyan 7.5

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.