ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutane 19,000 Sun Amfana Da Tallafin Fadama III A Zamfara

by Hussein Yero
3 years ago
Zamfara

Gwamna Dauda Lawal, a jiya Laraba, ya kaddamar da shirin farfado da tattalin arziki na shirin (N-CARES) na Nijeriya Coronavirus (COVID-19) tare da rarraba kayan amfanin gona da kadarorin noma ga mutane 19,000.

An gudanar da bikin kaddamar da shirin na Fadama III a ma’aikatar noma ta Jihar Zamfara, kuma mutane daga kananan hukumomi shida ne suka amfana da shirin.

  • Masu Fyade Da ’Yan Luwadi 369 Aka Kama A 2023 A Katsina
  • Tsohuwar Ministar Ayyukan Jin-Kai Ta Ki Amsa Gayyatar EFCC

A wajen bikin an raba sama da injinan wutar lantarki 700 da iri na shinkafa da masara ga manoma 19,000.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, gwamnatin Gwamna Dauda Lawal ta kuduri aniyar inganta harkar noma ta hanyar samar da isasshen tallafi ga manoma.

A yayin jawabinsa a wajen taron kaddamarwar, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada kudirin gwamnatinsa na samar da ayyukan yi ga marasa karfi a Zamfara.

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

Ya ce: “Ta hanyar shirin Fadama III, manoma 100,000 ne za a karfafa musu kayan aiki da iri a cikin shekaru hudu masu zuwa, kuma wannan yana ciki kasafin kudin cetonmu na 2024, ya shaida kudurisa na daukar matakan da ake bukata domin ganinmun cimma burinmu a fannin noma, wanda shi ne bangare mafi muhimmanci na tattalin arzikin jiharmu.

“Kamar yadda kuka sani, shirin COVID-19 shiri ne na farfado da tattalin arziki shiri ne da ya kunshi bangarori daban-daban da ke kewaye da yankuna uku masu muhimmanci kuma an tsara shi don magance kalubale da samun damar yin amfani da damar inganta noma.

“A karkashin FADAMA 3, yankin zai mayar da hankali ne kan inganta samar da abinci da kuma tabbatar da amintaccen aikin samar da abinci ga gidajenmu masu rauni.”

Bugu da kari, Gwamna Lawal ya ce gwamnatin Jihar Zamfara za ta bayar da tallafi da ayyuka masu muhimmanci, da ginawa da gyara hanyoyin shiga, tare da ware kadarori domin noma da rage asarar abinci”.

“A wannan zagaye na uku, babban burinmu shi ne mu inganta ayyukan noma 11,760 kai tsaye ta hanyar samar musu da muhimman abubuwa kamar takin zamani, maganin ciyawa, maganin kwari, ingantattun iri, da sinadarai masu sanya iri. Domin noman rani mai zuwa, mun ware buhunan taki 33,000 – wanda ya kunshi buhunan NPK 22,000 da kuma buhunan Urea 11,000.

“Haka zalika, za a raba injinan wutar lantarki sama da 700 da iri na shinkafa da masara ga manoma 19,000. Bugu da kari, kungiyoyi 735 na manoma goma kowannen su za a ba su na’urar wutar lantarki, kuma mutane 2,550 za su karbi kananan dabbobi.”

Zamfara
Hussein Yero
+ postsBio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    ’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Abdulaziz Yari Ya Bukaci Limamai Su Ƙara Addu’a Kan Yaƙi Da Ƴan Bindiga A Zamfara

MASU ALAKA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Next Post
Majalisa Ta Amince Tinubu Ya Ciwo Bashin Naira Tiriliyan 7.5

Majalisa Ta Amince Tinubu Ya Ciwo Bashin Naira Tiriliyan 7.5

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.