• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 2 Sun Mutu, 9 Sun Bace Bayan Jirgin Ruwa Ya Nutse Tsakanin Japan Da Koriya Ta Kudu 

by Sadiq
3 years ago
Jirgin Ruwa

Ma’aikatan jirgin ruwa biyu ne aka tabbatar da mutuwarsu yayin da wasu tara suka bace a ranar Laraba bayan da jirgin dako ya nutse a cikin ruwa tsakanin kasar Japan da Koriya ta Kudu, in ji hukumomin Japan.

Jami’an tsaron gabar teku na kasashen biyu, tare da jirgin soji da wani jirgin ruwa mai zaman kansa, sun gano 13 daga cikin mutane 22 da ke cikin jirgin Jin Tian, ​​kamar yadda wani jami’in tsaron gabar ruwan Japan ya bayyana.

  • An Fara Aiki Da Sashen Farko Na Layin Dogon Da Sin Ta Gina A Lagos 
  • Da Dumi-Dumi: Dan Takarar Gwamnan Jihar Abia Na Jam’iyyar PDP Ya Rasu

Amma daga baya hukumomin kiwon lafiya na Japan sun tabbatar da cewa biyu daga cikin wadanda aka dawo da su sun mutu, kamar yadda jami’in ya shaida wa AFP.

Ma’aikatan jirgin sun fito ne daga China da Myanmar, amma ba a san takamaiman ainihin wadanda suka mutu, wadanda aka ceto da kuma wadanda suka bace ba, in ji shi.

Ya kara da cewa “Tasoshinmu za su ci gaba da zama a yankin kuma za su ci gaba da gudanar da bincike cikin dare.”

LABARAI MASU NASABA

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

Jin Tian ya aike da sakon kar ta kwana da yammacin ranar Talata daga wani wuri mai tazarar kilomita 110 yamma da tsibirin Danjo mai nisa da kudu maso yammacin Japan.

Jiragen ruwa masu zaman kansu uku ne a yankin kuma sun taimaka wajen daukar biyar daga cikin ma’aikatan jirgin da ya makale, in ji jami’an tsaron gabar tekun Japan.

Tasoshin ruwa da jiragen sama da yawa daga jami’an tsaron gabar tekun Japan da na soja, da kuma masu tsaron gabar tekun Koriya ta Kudu da wani jirgin ruwa mai zaman kansa, sun shiga aikin laluben wadanda suka bace.

Kyaftin din jirgin ya yi amfani da waya, inda ya shaidawa jami’an tsaron gabar tekun Koriya ta Kudu cewa shi da ma’aikatan jirgin na neman dauki daga jirgin da ya nutse a ruwan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya
Labarai

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

October 10, 2025
Nijeriya
Labarai

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Next Post
Ministan Harkokin Wajen Argentina: Sin Muhimmiyar Abokiyar Cinikayya Ce Ta Argentina

Ministan Harkokin Wajen Argentina: Sin Muhimmiyar Abokiyar Cinikayya Ce Ta Argentina

LABARAI MASU NASABA

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho

October 10, 2025
Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

October 10, 2025
peter

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

October 10, 2025
Jonathan

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

October 10, 2025
Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

October 10, 2025
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

October 10, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

October 10, 2025
Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.