• English
  • Business News
Tuesday, September 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 3 Sun Rasa Rayukansu Yayin Da Ambaliyar Ruwa Ta Mamaye Ƙauyuka A Bauchi

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Mutum 3 Sun Rasa Rayukansu Yayin Da Ambaliyar Ruwa Ta Mamaye Ƙauyuka A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ƙalla mutum uku ne suka rasa rayukansu yayin da ambaliyar ruwa ta yi awun gaba da mamaye wasu ƙauyuka a ƙananan hukumomi uku na Shira, Giade da kuma Katagum da suke jihar Bauchi.

Darakta-janar na hukumar samar da agajin gaggawa ta jihar Bauchi (SEMA), Mr. Mas’ud Aliyu ne ya sanar da hakan yayin ziyarar duba irin ɓarna da ambaliyar ruwan ta yi a ƙananan hukumomin.

  • Ambaliyar Ruwa Ta Raba Hanyar Bauchi Zuwa Kano
  • Gwamnati Ta Amince Da Aikin Titin Sakkwato Zuwa Badagry Da Ayyukan Gina Madatsun Ruwa 63

Ya ce, sun samu rahotonnin da ke cewa, mutum uku ne suka rasu a ƙaramar hukumar Shira yayin da mutane da dama suka rasa muhallai, kayan abinci, amfani gona da kuma yankewar wasu hanyoyi dukka sakamakon mamayar ruwan.

 

Kazalika, ruwan ya share ƙauyuka da dama inda hakan ya tursasa wa mutanen da ke zaune a yankunan neman inda za su yi gudun hijira.

Labarai Masu Nasaba

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

Ambaliyar ruwa

A ƙaramar hukumar Katagum, shugaban ƙaramar hukumar, Malam Musa Azare ya ce wata ƙauye mai suna Sabon Gari da ke cikin Azare gabaki ɗaya ambaliyar ruwan ya share garin kaf.

 

Ya ce babu wani gida a ƙauyen da ɓarnar bai shafa ba.

 

“Mun samu nasarar kwashe mutanen da ke zaune a ƙauyen zuwa wuraren gwamnati da ke kusa da su bisa taimakon gaggawa da gwamnan jihar Bauchi Bala Mohammed ya samar.

Ambaliyar ruwa

“Abun farin ciki ne mu a Katagum babu asarar rai ko daya da aka samu. Har yanzu muna kan tattara irin ɓarna na ƙadarori da aka samu sakamakon ambaliyar.”

 

Ya gode wa Gwamna Bala Mohammed bisa aiko fa buhunan kayan abinci 900 dabam dabam domin rabar wa jama’a a matsayin agajin gaggawa. Kayan Abincin sun hada da buhun shinkafa 300, dawa 300, masara 300 da kuma katifu guda 250 da kayan rufuwa.

 

“Bugu da ƙari, ina miƙa godiyar mu wa mai martaba sarkin Katagum Alhaji Dr. Umar Farouk II, OON, bisa tallafin Naira miliyan biyu da ya bayar ga waɗanda abun ya shafa. Yayin da mu kuma a matakin ƙaramar hukuma mika bayar da gudunmawar miliyan daya ga waɗanda ambaliyar ta shafa.”

 

A lokacin da yake miƙa kayan abincin da jajanta wa jama’an da ambaliyar ta shafa, sakataren gwamnatin jihar, Ibrahim Muhammad Kashim ya ce sun zo ne domin nuna alhini da kuma taimaka wa waɗanda abun ya shafa musamman a irin wannan halin da suke ciki.

Ambaliyar ruwa

Ya nemi su miƙa lamarin ga Allah kana suke bin shawarorin hukumomi na daina gine-gine a kan magudan ruwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ambaliyar ruwan samaTsadar kayayyakin abinci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Fadadar Sana’ar Jigilar Kaya Cikin Sauri A Sin Na Nuni Ga Bunkasar Sayayyar Kayayyaki A Kasar

Next Post

Babban Bankin Sin Ya Samar Da Karin Dama Ta Lamuni Don Tallafawa Sassan Noma Da Kananan Sana’o’i

Related

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

1 hour ago
Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye
Manyan Labarai

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

6 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Dage Komawa Makaranta Saboda Kidayar Jama’a
Manyan Labarai

Gini Ya Rushe A Jigawa, Mutum 1 Ya Rasu, 7 Sun Jikkata

9 hours ago
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

18 hours ago
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Manyan Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Buƙaci Al’ummar Jihar Kaduna Da Su Yi Rijistar Katin Zaɓe 

23 hours ago
DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu
Manyan Labarai

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

1 day ago
Next Post
Babban Bankin Sin Ya Samar Da Karin Dama Ta Lamuni Don Tallafawa Sassan Noma Da Kananan Sana’o’i

Babban Bankin Sin Ya Samar Da Karin Dama Ta Lamuni Don Tallafawa Sassan Noma Da Kananan Sana’o’i

LABARAI MASU NASABA

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

September 9, 2025
Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

September 9, 2025
Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

September 9, 2025
Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

September 9, 2025
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙara Kan Zargin Ƴansanda Da Cin Zarafinsa A Kaduna

September 9, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Dage Komawa Makaranta Saboda Kidayar Jama’a

Gini Ya Rushe A Jigawa, Mutum 1 Ya Rasu, 7 Sun Jikkata

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

September 8, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

September 8, 2025
Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 8, 2025
'yansanda

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

September 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.