• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 3 Sun Rasa Rayukansu Yayin Da Ambaliyar Ruwa Ta Mamaye Ƙauyuka A Bauchi

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
10 months ago
in Manyan Labarai
0
Mutum 3 Sun Rasa Rayukansu Yayin Da Ambaliyar Ruwa Ta Mamaye Ƙauyuka A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ƙalla mutum uku ne suka rasa rayukansu yayin da ambaliyar ruwa ta yi awun gaba da mamaye wasu ƙauyuka a ƙananan hukumomi uku na Shira, Giade da kuma Katagum da suke jihar Bauchi.

Darakta-janar na hukumar samar da agajin gaggawa ta jihar Bauchi (SEMA), Mr. Mas’ud Aliyu ne ya sanar da hakan yayin ziyarar duba irin ɓarna da ambaliyar ruwan ta yi a ƙananan hukumomin.

  • Ambaliyar Ruwa Ta Raba Hanyar Bauchi Zuwa Kano
  • Gwamnati Ta Amince Da Aikin Titin Sakkwato Zuwa Badagry Da Ayyukan Gina Madatsun Ruwa 63

Ya ce, sun samu rahotonnin da ke cewa, mutum uku ne suka rasu a ƙaramar hukumar Shira yayin da mutane da dama suka rasa muhallai, kayan abinci, amfani gona da kuma yankewar wasu hanyoyi dukka sakamakon mamayar ruwan.

 

Kazalika, ruwan ya share ƙauyuka da dama inda hakan ya tursasa wa mutanen da ke zaune a yankunan neman inda za su yi gudun hijira.

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

Ambaliyar ruwa

A ƙaramar hukumar Katagum, shugaban ƙaramar hukumar, Malam Musa Azare ya ce wata ƙauye mai suna Sabon Gari da ke cikin Azare gabaki ɗaya ambaliyar ruwan ya share garin kaf.

 

Ya ce babu wani gida a ƙauyen da ɓarnar bai shafa ba.

 

“Mun samu nasarar kwashe mutanen da ke zaune a ƙauyen zuwa wuraren gwamnati da ke kusa da su bisa taimakon gaggawa da gwamnan jihar Bauchi Bala Mohammed ya samar.

Ambaliyar ruwa

“Abun farin ciki ne mu a Katagum babu asarar rai ko daya da aka samu. Har yanzu muna kan tattara irin ɓarna na ƙadarori da aka samu sakamakon ambaliyar.”

 

Ya gode wa Gwamna Bala Mohammed bisa aiko fa buhunan kayan abinci 900 dabam dabam domin rabar wa jama’a a matsayin agajin gaggawa. Kayan Abincin sun hada da buhun shinkafa 300, dawa 300, masara 300 da kuma katifu guda 250 da kayan rufuwa.

 

“Bugu da ƙari, ina miƙa godiyar mu wa mai martaba sarkin Katagum Alhaji Dr. Umar Farouk II, OON, bisa tallafin Naira miliyan biyu da ya bayar ga waɗanda abun ya shafa. Yayin da mu kuma a matakin ƙaramar hukuma mika bayar da gudunmawar miliyan daya ga waɗanda ambaliyar ta shafa.”

 

A lokacin da yake miƙa kayan abincin da jajanta wa jama’an da ambaliyar ta shafa, sakataren gwamnatin jihar, Ibrahim Muhammad Kashim ya ce sun zo ne domin nuna alhini da kuma taimaka wa waɗanda abun ya shafa musamman a irin wannan halin da suke ciki.

Ambaliyar ruwa

Ya nemi su miƙa lamarin ga Allah kana suke bin shawarorin hukumomi na daina gine-gine a kan magudan ruwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ambaliyar ruwan samaTsadar kayayyakin abinci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Fadadar Sana’ar Jigilar Kaya Cikin Sauri A Sin Na Nuni Ga Bunkasar Sayayyar Kayayyaki A Kasar

Next Post

Babban Bankin Sin Ya Samar Da Karin Dama Ta Lamuni Don Tallafawa Sassan Noma Da Kananan Sana’o’i

Related

Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

4 hours ago
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno
Manyan Labarai

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

7 hours ago
Sanusi
Manyan Labarai

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

18 hours ago
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

21 hours ago
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus
Manyan Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

24 hours ago
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

1 day ago
Next Post
Babban Bankin Sin Ya Samar Da Karin Dama Ta Lamuni Don Tallafawa Sassan Noma Da Kananan Sana’o’i

Babban Bankin Sin Ya Samar Da Karin Dama Ta Lamuni Don Tallafawa Sassan Noma Da Kananan Sana’o’i

LABARAI MASU NASABA

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

June 4, 2025
DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.