• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 3 Sun Rasa Rayukansu Yayin Da Ambaliyar Ruwa Ta Mamaye Ƙauyuka A Bauchi

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
11 months ago
in Manyan Labarai
0
Mutum 3 Sun Rasa Rayukansu Yayin Da Ambaliyar Ruwa Ta Mamaye Ƙauyuka A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ƙalla mutum uku ne suka rasa rayukansu yayin da ambaliyar ruwa ta yi awun gaba da mamaye wasu ƙauyuka a ƙananan hukumomi uku na Shira, Giade da kuma Katagum da suke jihar Bauchi.

Darakta-janar na hukumar samar da agajin gaggawa ta jihar Bauchi (SEMA), Mr. Mas’ud Aliyu ne ya sanar da hakan yayin ziyarar duba irin ɓarna da ambaliyar ruwan ta yi a ƙananan hukumomin.

  • Ambaliyar Ruwa Ta Raba Hanyar Bauchi Zuwa Kano
  • Gwamnati Ta Amince Da Aikin Titin Sakkwato Zuwa Badagry Da Ayyukan Gina Madatsun Ruwa 63

Ya ce, sun samu rahotonnin da ke cewa, mutum uku ne suka rasu a ƙaramar hukumar Shira yayin da mutane da dama suka rasa muhallai, kayan abinci, amfani gona da kuma yankewar wasu hanyoyi dukka sakamakon mamayar ruwan.

 

Kazalika, ruwan ya share ƙauyuka da dama inda hakan ya tursasa wa mutanen da ke zaune a yankunan neman inda za su yi gudun hijira.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Ambaliyar ruwa

A ƙaramar hukumar Katagum, shugaban ƙaramar hukumar, Malam Musa Azare ya ce wata ƙauye mai suna Sabon Gari da ke cikin Azare gabaki ɗaya ambaliyar ruwan ya share garin kaf.

 

Ya ce babu wani gida a ƙauyen da ɓarnar bai shafa ba.

 

“Mun samu nasarar kwashe mutanen da ke zaune a ƙauyen zuwa wuraren gwamnati da ke kusa da su bisa taimakon gaggawa da gwamnan jihar Bauchi Bala Mohammed ya samar.

Ambaliyar ruwa

“Abun farin ciki ne mu a Katagum babu asarar rai ko daya da aka samu. Har yanzu muna kan tattara irin ɓarna na ƙadarori da aka samu sakamakon ambaliyar.”

 

Ya gode wa Gwamna Bala Mohammed bisa aiko fa buhunan kayan abinci 900 dabam dabam domin rabar wa jama’a a matsayin agajin gaggawa. Kayan Abincin sun hada da buhun shinkafa 300, dawa 300, masara 300 da kuma katifu guda 250 da kayan rufuwa.

 

“Bugu da ƙari, ina miƙa godiyar mu wa mai martaba sarkin Katagum Alhaji Dr. Umar Farouk II, OON, bisa tallafin Naira miliyan biyu da ya bayar ga waɗanda abun ya shafa. Yayin da mu kuma a matakin ƙaramar hukuma mika bayar da gudunmawar miliyan daya ga waɗanda ambaliyar ta shafa.”

 

A lokacin da yake miƙa kayan abincin da jajanta wa jama’an da ambaliyar ta shafa, sakataren gwamnatin jihar, Ibrahim Muhammad Kashim ya ce sun zo ne domin nuna alhini da kuma taimaka wa waɗanda abun ya shafa musamman a irin wannan halin da suke ciki.

Ambaliyar ruwa

Ya nemi su miƙa lamarin ga Allah kana suke bin shawarorin hukumomi na daina gine-gine a kan magudan ruwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ambaliyar ruwan samaTsadar kayayyakin abinci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Fadadar Sana’ar Jigilar Kaya Cikin Sauri A Sin Na Nuni Ga Bunkasar Sayayyar Kayayyaki A Kasar

Next Post

Babban Bankin Sin Ya Samar Da Karin Dama Ta Lamuni Don Tallafawa Sassan Noma Da Kananan Sana’o’i

Related

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

10 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

1 day ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

1 day ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

1 day ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

1 day ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

1 day ago
Next Post
Babban Bankin Sin Ya Samar Da Karin Dama Ta Lamuni Don Tallafawa Sassan Noma Da Kananan Sana’o’i

Babban Bankin Sin Ya Samar Da Karin Dama Ta Lamuni Don Tallafawa Sassan Noma Da Kananan Sana’o’i

LABARAI MASU NASABA

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.