• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 3 Sun Rasa Rayukansu Yayin Da Ambaliyar Ruwa Ta Mamaye Ƙauyuka A Bauchi

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
9 months ago
in Manyan Labarai
0
Mutum 3 Sun Rasa Rayukansu Yayin Da Ambaliyar Ruwa Ta Mamaye Ƙauyuka A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ƙalla mutum uku ne suka rasa rayukansu yayin da ambaliyar ruwa ta yi awun gaba da mamaye wasu ƙauyuka a ƙananan hukumomi uku na Shira, Giade da kuma Katagum da suke jihar Bauchi.

Darakta-janar na hukumar samar da agajin gaggawa ta jihar Bauchi (SEMA), Mr. Mas’ud Aliyu ne ya sanar da hakan yayin ziyarar duba irin ɓarna da ambaliyar ruwan ta yi a ƙananan hukumomin.

  • Ambaliyar Ruwa Ta Raba Hanyar Bauchi Zuwa Kano
  • Gwamnati Ta Amince Da Aikin Titin Sakkwato Zuwa Badagry Da Ayyukan Gina Madatsun Ruwa 63

Ya ce, sun samu rahotonnin da ke cewa, mutum uku ne suka rasu a ƙaramar hukumar Shira yayin da mutane da dama suka rasa muhallai, kayan abinci, amfani gona da kuma yankewar wasu hanyoyi dukka sakamakon mamayar ruwan.

 

Kazalika, ruwan ya share ƙauyuka da dama inda hakan ya tursasa wa mutanen da ke zaune a yankunan neman inda za su yi gudun hijira.

Labarai Masu Nasaba

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Ambaliyar ruwa

A ƙaramar hukumar Katagum, shugaban ƙaramar hukumar, Malam Musa Azare ya ce wata ƙauye mai suna Sabon Gari da ke cikin Azare gabaki ɗaya ambaliyar ruwan ya share garin kaf.

 

Ya ce babu wani gida a ƙauyen da ɓarnar bai shafa ba.

 

“Mun samu nasarar kwashe mutanen da ke zaune a ƙauyen zuwa wuraren gwamnati da ke kusa da su bisa taimakon gaggawa da gwamnan jihar Bauchi Bala Mohammed ya samar.

Ambaliyar ruwa

“Abun farin ciki ne mu a Katagum babu asarar rai ko daya da aka samu. Har yanzu muna kan tattara irin ɓarna na ƙadarori da aka samu sakamakon ambaliyar.”

 

Ya gode wa Gwamna Bala Mohammed bisa aiko fa buhunan kayan abinci 900 dabam dabam domin rabar wa jama’a a matsayin agajin gaggawa. Kayan Abincin sun hada da buhun shinkafa 300, dawa 300, masara 300 da kuma katifu guda 250 da kayan rufuwa.

 

“Bugu da ƙari, ina miƙa godiyar mu wa mai martaba sarkin Katagum Alhaji Dr. Umar Farouk II, OON, bisa tallafin Naira miliyan biyu da ya bayar ga waɗanda abun ya shafa. Yayin da mu kuma a matakin ƙaramar hukuma mika bayar da gudunmawar miliyan daya ga waɗanda ambaliyar ta shafa.”

 

A lokacin da yake miƙa kayan abincin da jajanta wa jama’an da ambaliyar ta shafa, sakataren gwamnatin jihar, Ibrahim Muhammad Kashim ya ce sun zo ne domin nuna alhini da kuma taimaka wa waɗanda abun ya shafa musamman a irin wannan halin da suke ciki.

Ambaliyar ruwa

Ya nemi su miƙa lamarin ga Allah kana suke bin shawarorin hukumomi na daina gine-gine a kan magudan ruwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ambaliyar ruwan samaTsadar kayayyakin abinci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Fadadar Sana’ar Jigilar Kaya Cikin Sauri A Sin Na Nuni Ga Bunkasar Sayayyar Kayayyaki A Kasar

Next Post

Babban Bankin Sin Ya Samar Da Karin Dama Ta Lamuni Don Tallafawa Sassan Noma Da Kananan Sana’o’i

Related

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

7 hours ago
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai
Manyan Labarai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

8 hours ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

17 hours ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

21 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

21 hours ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

24 hours ago
Next Post
Babban Bankin Sin Ya Samar Da Karin Dama Ta Lamuni Don Tallafawa Sassan Noma Da Kananan Sana’o’i

Babban Bankin Sin Ya Samar Da Karin Dama Ta Lamuni Don Tallafawa Sassan Noma Da Kananan Sana’o’i

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.