• English
  • Business News
Friday, August 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 50 Suka Amfana Da Zakkar Da Wani Bawan Allah Ya Fitar A Kaduna

by Abubakar Abba
2 years ago
in Zamantakewa
0
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani mai hannu da shuni da ke zaune a Jihar Kaduna, wanda bai bukaci a ambaci sunan sa ba, ya rabar da zakkar kudi ga masu kananan sana’o’i sama da 50 don su kara bunkasa harkokin kasuwancinsu.

Akasarin wadanda suka amafana da zakkar mata ne da kuma matasa da ke yin sana’o’in aski, sayar da abinci, yin tukwane, masu wankin kai, takalma da yin sana’a a kafar internet da sauransu.

Daya daga cikin daraktocin cibiyar samar da daidaito a tsakanin mabiya addinin musulunci da na kirista, Mallam Abdullahi Mohammed Sufi ne ya rabar da zakkar kudin a madadin wannan bawan Allah.

A hirasa da manena labarai jin kadan bayan rabar da zakkar, Sufi ya ce wanda ya bayar da zakkar kudin bai son a ambaci sunnan sa. Ya ce mutumin ya yanke shawarar bayar da zakkar kudin ne ga wadanda suka amfana don su kara bunkasa harkokin kasuwancinsau kuma su ci gaba da zama masu dogaro da kansu, musamman idan aka yi la’akari da yadda masu kanannan sana’o’i a jihar ke fuskantar kalubale masu yawan gaske.

Sufi ya yi kira ga sauran musulmi masu hannu da shuni da ke a daukacin fadin kasar nan da su taimaka wa masu kananan sana’o’i don su kara habaka kasuwancinsu ta yadda suma a nan gaba za su iya taimaka wa sauaran. Sannan ya yi kira musamman ga gwamnatin tarayya da ta samar da kyakyawan yanayi ga masu kananan sana’o’i da ke a kasar nan don su samu damar yin kasuwanci yadda ya kamata.

Labarai Masu Nasaba

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

Matsalolin Da Ke Tattare Da Zawarci Da Rashin Yin Aure Da Wuri

Daya daga cikin wadanda suka amfana da zakkar, Nafisa Zakari Ya’u wacce ke yin kasuwanci ta kafar internet a Kaduna ta gode wa wanda ya ba su kudin, inda ta ce zakkar za ta taimaka mata wajen kara habaka kasuwancinta da kuma magance kalubalen da take fuskanta a baya
Ta yi kira ga sauran masu hannu da shuni da su talllafa wa masu kanannan sana’o’i da jari don su ci gaba da zama masu dogaro da kansu, musamman duba ga yadda ake fuskantar kalubale a fannin kasuwanci a kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kada Ku Sake Bai Wa Gwamnati Mai Barin Gado Bashi —Abba Ga Bankuna

Next Post

Karamin Ministan Man Fetur Timipre Sylva, Ya Yi Murabus Daga Mukaminsa

Related

Budurwa
Taskira

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

2 weeks ago
Matsalolin Da Ke Tattare Da Zawarci Da Rashin Yin Aure Da Wuri
Taskira

Matsalolin Da Ke Tattare Da Zawarci Da Rashin Yin Aure Da Wuri

3 weeks ago
Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3
Ilimi

Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

3 months ago
‘Yansanda Sun Hana Hawan Sallah A Kano Saboda Tsaro
Taskira

Shirye-shiryen Bukukuwan karamar Sallah

4 months ago
Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan
Taskira

Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan

5 months ago
Me Ke Kawo Saurin Talaucewa Bayan Kammala Aikin Gwamnati?
Taskira

Me Ke Kawo Saurin Talaucewa Bayan Kammala Aikin Gwamnati?

6 months ago
Next Post
Karamin Ministan Man Fetur Timipre Sylva, Ya Yi Murabus Daga Mukaminsa

Karamin Ministan Man Fetur Timipre Sylva, Ya Yi Murabus Daga Mukaminsa

LABARAI MASU NASABA

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

August 8, 2025
Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

August 8, 2025
Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

August 8, 2025
Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

August 8, 2025
GORON JUMA’A 8-8-2025

GORON JUMA’A 8-8-2025

August 8, 2025
Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

August 8, 2025
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

August 8, 2025
Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu

Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu

August 8, 2025
Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum

Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum

August 8, 2025
Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.