• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 50 Suka Amfana Da Zakkar Da Wani Bawan Allah Ya Fitar A Kaduna

by Abubakar Abba
3 years ago

Wani mai hannu da shuni da ke zaune a Jihar Kaduna, wanda bai bukaci a ambaci sunan sa ba, ya rabar da zakkar kudi ga masu kananan sana’o’i sama da 50 don su kara bunkasa harkokin kasuwancinsu.

Akasarin wadanda suka amafana da zakkar mata ne da kuma matasa da ke yin sana’o’in aski, sayar da abinci, yin tukwane, masu wankin kai, takalma da yin sana’a a kafar internet da sauransu.

Daya daga cikin daraktocin cibiyar samar da daidaito a tsakanin mabiya addinin musulunci da na kirista, Mallam Abdullahi Mohammed Sufi ne ya rabar da zakkar kudin a madadin wannan bawan Allah.

A hirasa da manena labarai jin kadan bayan rabar da zakkar, Sufi ya ce wanda ya bayar da zakkar kudin bai son a ambaci sunnan sa. Ya ce mutumin ya yanke shawarar bayar da zakkar kudin ne ga wadanda suka amfana don su kara bunkasa harkokin kasuwancinsau kuma su ci gaba da zama masu dogaro da kansu, musamman idan aka yi la’akari da yadda masu kanannan sana’o’i a jihar ke fuskantar kalubale masu yawan gaske.

Sufi ya yi kira ga sauran musulmi masu hannu da shuni da ke a daukacin fadin kasar nan da su taimaka wa masu kananan sana’o’i don su kara habaka kasuwancinsu ta yadda suma a nan gaba za su iya taimaka wa sauaran. Sannan ya yi kira musamman ga gwamnatin tarayya da ta samar da kyakyawan yanayi ga masu kananan sana’o’i da ke a kasar nan don su samu damar yin kasuwanci yadda ya kamata.

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Wasu Maza Ke Gudun Auren Mata ‘Yan Boko Masu Kwarewa Da Wayewa?

Yadda Wasu Iyaye Ke Hana ‘Ya’yansu Auren Matan Da Suka Girme Su Da Zawarawa

Daya daga cikin wadanda suka amfana da zakkar, Nafisa Zakari Ya’u wacce ke yin kasuwanci ta kafar internet a Kaduna ta gode wa wanda ya ba su kudin, inda ta ce zakkar za ta taimaka mata wajen kara habaka kasuwancinta da kuma magance kalubalen da take fuskanta a baya
Ta yi kira ga sauran masu hannu da shuni da su talllafa wa masu kanannan sana’o’i da jari don su ci gaba da zama masu dogaro da kansu, musamman duba ga yadda ake fuskantar kalubale a fannin kasuwanci a kasar nan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Me Ya Sa Wasu Maza Ke Gudun Auren Mata ‘Yan Boko Masu Kwarewa Da Wayewa?
Taskira

Me Ya Sa Wasu Maza Ke Gudun Auren Mata ‘Yan Boko Masu Kwarewa Da Wayewa?

August 31, 2025
Yadda Wasu Iyaye Ke Hana ‘Ya’yansu Auren Matan Da Suka Girme Su Da Zawarawa
Taskira

Yadda Wasu Iyaye Ke Hana ‘Ya’yansu Auren Matan Da Suka Girme Su Da Zawarawa

August 17, 2025
Mata
Taskira

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
Next Post
Karamin Ministan Man Fetur Timipre Sylva, Ya Yi Murabus Daga Mukaminsa

Karamin Ministan Man Fetur Timipre Sylva, Ya Yi Murabus Daga Mukaminsa

LABARAI MASU NASABA

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.