• English
  • Business News
Thursday, July 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Yi Rashin Jagora, Buhari Ne Ya Ƙarfafa Min Guiwa Na Yi Takarar Gwamna A Kaduna — El-Rufai

by Muhammad
3 days ago
in Manyan Labarai
0
Chelsea Ta Kafa Babban Tarihi Bayan Lashe Kofin Duniya Na Ƙungiyoyi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana marigayi tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari, a matsayin jagoran siyasarsa, wanda ya ƙarfafa masa guiwa har ya tsaya takarar gwamnan Kaduna.

A sakon ta’aziyyarsa, El-Rufai ya ce Buhari ya tsaya tsayin daka don ci gaban Nijeriya, ya bayar da gudummawa mai tsoka a matsayinsa na soja kuma shugaban ƙasa na mulkin soja da kuma zaɓaɓɓen shugaban ƙasa.

  • Rasuwar Buhari: Na Yi Rashin Ɗan’uwa, Aboki, Ɗan Ƙasa Nagari —Babangida
  • Rasuwar Buhari Babbar Asara Ce Ga Nijeriya — Obasanjo

El-Rufai ya ce Buhari ya kasance jarumi mai juriya wanda duk da tsige shi daga mulki a 1985, ya dawo kuma ya lashe zaɓe a 2015.

“Ko da yake bai cika magana ba, yana da natsuwa da barkwanci. Yana da hali mai sauƙi da ya sa talakawa ke ƙaunarsa, saboda suna ganin shi mutum ne mai gaskiya da amana.”

“Ko bayan faɗuwarsa a zaɓen shugaban ƙasa sau uku, ya sake tashi suka kafa jam’iyyar APC a 2013, wanda ya kayar da shugaban ƙasa mai ci a 2015. Ya kuma miƙa mulki cikin nasara a 2023, wanda hakan ya kafa tarihi.”

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

Ya ƙara da cewa ya samu damar yin aiki da Buhari a jam’iyyar CPC bayan zaɓen 2011, inda Buhari ya sa shi ya jagoranci kwamitin farfado da jam’iyyar. Kwamitin ne ya ba da shawarar haɗakar CPC da ACN da sauran jam’iyyu don tunkarar zaɓen 2015.

“Shugaba Buhari shi ne jagoran siyasa ta. Shi ya karfafa min guiwa na tsaya takarar gwamnan Kaduna. Ya halarci ƙaddamar da kamfe ɗina a watan Nuwamba 2014, kuma ya tsaya min har na kai ga nasara. Ina godiya sosai da goyon bayansa a lokacin gwamnatina, har da damar da na samu na tattaunawa da shi a kowane lokaci, ko da kuwa muna da saɓani a wasu manufofi.”

El-Rufai ya roƙi Allah Ya gafarta wa Buhari, Ya sanya shi a Aljannatul Firdaus, tare da bai wa iyalansa, musamman Hajiya Aisha Buhari da ’ya’yansa, hakurin rashinsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariEl-RufaiKadunaLandanRasuawaRasuwar Buhari
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rasuwar Buhari: Na Yi Rashin Ɗan’uwa, Aboki, Ɗan Ƙasa Nagari —Babangida

Next Post

Shugaban ECOWAS Julius Bio, Ya Yi Wa Tinubu Da ‘Yan Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Buhari

Related

Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu
Manyan Labarai

Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

28 minutes ago
Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili
Manyan Labarai

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

16 hours ago
Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya
Manyan Labarai

Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya

17 hours ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Manyan Labarai

Omokri Da Sarki Sun Soki Obi Saboda Rashin Halartar Jana’izar Buhari

18 hours ago
Kotu Ta Wanke Fayose Daga Zargin Zambar Naira Biliyan 3.3
Manyan Labarai

Kotu Ta Wanke Fayose Daga Zargin Zambar Naira Biliyan 3.3

20 hours ago
Kasa Da Wata Biyu Ya Bar Mulki, Shin Ko Buhari Ya Cika Wa ‘Yan Nijeriya Alkawarin Da Ya Yi Mu Su?
Manyan Labarai

EU, Turkiyya Da Sauran Ƙasashe Sun Yi Ta’aziyyar Rasuwar Buhari

1 day ago
Next Post
Shugaban ECOWAS Julius Bio, Ya Yi Wa Tinubu Da ‘Yan Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Buhari

Shugaban ECOWAS Julius Bio, Ya Yi Wa Tinubu Da 'Yan Nijeriya Ta'aziyyar Rasuwar Buhari

LABARAI MASU NASABA

Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

July 17, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

July 16, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

July 16, 2025
Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

July 16, 2025
Dubun Wasu Mutane 20 Da Ake Zargi Da Safarar Makamai A Kwara Ta Cika

Dubun Wasu Mutane 20 Da Ake Zargi Da Safarar Makamai A Kwara Ta Cika

July 16, 2025
Jarin Kasar Sin Ya Bada Gudunmawa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Zimbabwe

Jarin Kasar Sin Ya Bada Gudunmawa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Zimbabwe

July 16, 2025
Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya

Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya

July 16, 2025
An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin

An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin

July 16, 2025
PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

July 16, 2025
Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

July 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.