• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago
Nafdac

Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta ƙasa (NAFDAC) ta rufe manyan shagunan ƴan China guda biyu da ke unguwar Jabi a Abuja, tare da kulle shagunan kayan shafe-shafe guda takwas a kasuwar Wuse saboda karya ƙa’idojin sayarwa, da rarrabawa da kuma rubuta sunayen kayayyaki.

A cikin sanarwar da mataimakin daraktan hulɗa da jama’a na hukumar, Adegboyega Osiyemi, ya fitar a ranar Juma’a, an ce wannan mataki ya biyo bayan umarnin daraktar hukumar, Farfesa Mojisola Adeyeye, inda tawagar NAFDAC ta kwace kayayyakin da ba su dace ba da darajarsu ta kai sama da Naira miliyan 170.

  • Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar UNGA Da Jamus
  • NAPTIP Ta Kama Mutum 5 Da Ake Zargi Da Safarar Mutane A Filin Jirgin Saman Abuja, Ta Ceto Mutane 24

Hukumar ta bayyana cewa an rufe shagunan da ke Mike Akhigbe Way da Ebitu Ukiwe Street bayan rahotanni daga masu amfani da kayayyaki da kuma bincike sun tabbatar da cewa shagunan na sayar da abinci da aka rubuta sunayensu da Sinanci kawai, ba tare da fassarar Turanci ba, lamarin da ya saɓawa tsarin Nijeriya. Kuma jami’an NAFDAC sun gano cewa ɗaya daga cikin shagunan yana aiki da cikakken kayan da ba a yi musu rajista ba.

Haka nan, a kasuwar Wuse an rufe shagunan kayan shafe-shafe guda takwas da ake zargi da sayar da kayayyaki da aka haramta, waɗanda wa’adin su ya ƙare, da kuma waɗanda ba su da rajista. Bincike ya gano cewa wasu ƴan kasuwa suna shiga irin ta likitocin fata da masu bayar da magani, suna rubuta kayayyaki masu haɗari ga mutane da nufin sanya fata fari, da gyaran jiki ko ƙara kuzarin jima’i.

Daga cikin kayan da aka kwace akwai magungunan sanya fata fari, da ƙwayoyin ƙara kuzari, da wasu magungunan gargajiya da kayan shafe-shafe da ake danganta su da haɗarin cutar da ƙoda, da fita daga hayyaci da ciwon daji na fata.

LABARAI MASU NASABA

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

Farfesa Adeyeye ta jaddada ƙudirin NAFDAC na kare lafiyar ƴan Nijeriya, tare da shawartar al’umma da su rika amfani da kayayyaki da aka tabbatar da rajistarsu a hukumar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)
Manyan Labarai

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

October 25, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar
Manyan Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
Next Post
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

LABARAI MASU NASABA

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

October 25, 2025
Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.