ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NAPTIP Ta Kama Mutum 5 Da Ake Zargi Da Safarar Mutane A Filin Jirgin Saman Abuja, Ta Ceto Mutane 24

by Sadiq
8 months ago
NAPTIP

Hukumar NAPTIP ta kama mutane biyar da ake zargi da safarar mutane a Filin Jirgin Saman Nnamdi Azikiwe, da ke Abuja.

Hukumar ta kuma ceto mutane 24 da ake so yin safarar su.

  • Da Haɗin Kai Da Jajircewa Ake Iya Tabbatar Da Dimokuraɗiyya – Shugaban AYCF
  • NNPCL Ya Ƙulla Sabuwar Yarjejeniya Ta Samar Da Ɗanyen Mai Na Shekaru Biyu Da Matatar Dangote

Shugabar Hukumar NAPTIP, Binta Adamu Bello ce, ta jagoranci wannan samame na musamman a ranar Laraba.

ADVERTISEMENT

Mai magana da yawun hukumar, Vincent Adekoye, ya bayyana cewa ɗaya daga cikin waɗanda aka kama tsohon jami’in tsaro ne, wanda ake zargin babban ɗan kungiyar masu safarar mutane ne da ke aiki a jihohin Kudu Maso Yamma.

Adekoye, ya ce wannan aikin na daga cikin sabon shirin da hukumar ta ƙaddamar domin yaƙi da safarar mutane, wanda ya shafi cibiyoyin ɗaukar ma’aikata da sauran wurare.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Bello, ta kuma bayar da umarnin ƙara tsaro a duk faɗin ƙasar na , musamman a tashoshin mota, hanyoyin ruwa a jihohin da ke bakin teku, da kuma filayen jiragen sama na ƙasa da ƙasa.

Samamen ya biyo bayan bayanan sirri daga masu ruwa da tsaki da abokan hulɗa, waɗanda suka sanar da hukumar cewa akwai mutane da ake shirin safararsu a filin jirgin Abuja.

Bayan kusan sa’o’i 6 da aka gudanar ana bincike, an kama mutane biyar da ake zargi, sannan an ceto mutane 24 da aka so yin safarar su.

Adekoye ya ce waɗanda aka ceto, masu shekaru tsakanin 15 zuwa 26 ne, kuma an ɗauko su daga jihohin Kano, Katsina, Oyo, Ondo da Ribas.

An shirya kai su Iraq, Sudan, Masar, Saudiyya, Bahrain da Afghanistan.

Wasu daga cikinsu ba su ma san inda ake son kai su ba.

Ɗaya daga cikin matasan ta ce an fada mata cewa za a kaita Turai domin ta yi aiki ta samu kuɗi a dalar Amurka, kuma iyayenta sun amince.

Wata kuma ta ce mahaifinta ne ya yaudare ta domin a yi tafiyar da ita,kuma ta rantse za ta kai shi ƙara.

Shugabar hukumar ta nuna musu bidiyon wasu ’yan Nijeriya da ke cikin mawuyacin hali a ƙasashen waje sakamakon irin wannan safara.

Ɗaya daga cikin matasan ta ce: “Na yi ƙoƙari na riƙe hawayena lokacin da na kalli bidiyon waɗanda ake azabtarwa. Idan haka ne ba zan je ba. Na fusata da mahaifina saboda ya yaudare ni.”

Bello ta yi Allah-wadai da masu safarar mutane da masu ɗaukar ma’aikata ba bisa ƙa’ida ba, waɗanda ke yaudarar ’yan Nijeriya domin su yi amfani da su ta hanyoyi daban-daban.

Ta ce ta gamsu da sakamakon aikin domin an samu nasarar karya hanyar wata babbar ƙungiyar masu safarar mutane da ke tura mutane zuwa ƙasashe masu hatsari, musamman a Gabas ta Tsakiya.

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Kamfanin Kasar Sin Ya Fara Aikin Gina Muhimmin Titin Yankunan Karkara A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Kasar Sin Ya Fara Aikin Gina Muhimmin Titin Yankunan Karkara A Babban Birnin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.