ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NAPTIP Ta Kama Mutum 5 Da Ake Zargi Da Safarar Mutane A Filin Jirgin Saman Abuja, Ta Ceto Mutane 24

by Sadiq
10 months ago
NAPTIP

Hukumar NAPTIP ta kama mutane biyar da ake zargi da safarar mutane a Filin Jirgin Saman Nnamdi Azikiwe, da ke Abuja.

Hukumar ta kuma ceto mutane 24 da ake so yin safarar su.

  • Da Haɗin Kai Da Jajircewa Ake Iya Tabbatar Da Dimokuraɗiyya – Shugaban AYCF
  • NNPCL Ya Ƙulla Sabuwar Yarjejeniya Ta Samar Da Ɗanyen Mai Na Shekaru Biyu Da Matatar Dangote

Shugabar Hukumar NAPTIP, Binta Adamu Bello ce, ta jagoranci wannan samame na musamman a ranar Laraba.

ADVERTISEMENT

Mai magana da yawun hukumar, Vincent Adekoye, ya bayyana cewa ɗaya daga cikin waɗanda aka kama tsohon jami’in tsaro ne, wanda ake zargin babban ɗan kungiyar masu safarar mutane ne da ke aiki a jihohin Kudu Maso Yamma.

Adekoye, ya ce wannan aikin na daga cikin sabon shirin da hukumar ta ƙaddamar domin yaƙi da safarar mutane, wanda ya shafi cibiyoyin ɗaukar ma’aikata da sauran wurare.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Bello, ta kuma bayar da umarnin ƙara tsaro a duk faɗin ƙasar na , musamman a tashoshin mota, hanyoyin ruwa a jihohin da ke bakin teku, da kuma filayen jiragen sama na ƙasa da ƙasa.

Samamen ya biyo bayan bayanan sirri daga masu ruwa da tsaki da abokan hulɗa, waɗanda suka sanar da hukumar cewa akwai mutane da ake shirin safararsu a filin jirgin Abuja.

Bayan kusan sa’o’i 6 da aka gudanar ana bincike, an kama mutane biyar da ake zargi, sannan an ceto mutane 24 da aka so yin safarar su.

Adekoye ya ce waɗanda aka ceto, masu shekaru tsakanin 15 zuwa 26 ne, kuma an ɗauko su daga jihohin Kano, Katsina, Oyo, Ondo da Ribas.

An shirya kai su Iraq, Sudan, Masar, Saudiyya, Bahrain da Afghanistan.

Wasu daga cikinsu ba su ma san inda ake son kai su ba.

Ɗaya daga cikin matasan ta ce an fada mata cewa za a kaita Turai domin ta yi aiki ta samu kuɗi a dalar Amurka, kuma iyayenta sun amince.

Wata kuma ta ce mahaifinta ne ya yaudare ta domin a yi tafiyar da ita,kuma ta rantse za ta kai shi ƙara.

Shugabar hukumar ta nuna musu bidiyon wasu ’yan Nijeriya da ke cikin mawuyacin hali a ƙasashen waje sakamakon irin wannan safara.

Ɗaya daga cikin matasan ta ce: “Na yi ƙoƙari na riƙe hawayena lokacin da na kalli bidiyon waɗanda ake azabtarwa. Idan haka ne ba zan je ba. Na fusata da mahaifina saboda ya yaudare ni.”

Bello ta yi Allah-wadai da masu safarar mutane da masu ɗaukar ma’aikata ba bisa ƙa’ida ba, waɗanda ke yaudarar ’yan Nijeriya domin su yi amfani da su ta hanyoyi daban-daban.

Ta ce ta gamsu da sakamakon aikin domin an samu nasarar karya hanyar wata babbar ƙungiyar masu safarar mutane da ke tura mutane zuwa ƙasashe masu hatsari, musamman a Gabas ta Tsakiya.

MASU ALAKA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Next Post
Kamfanin Kasar Sin Ya Fara Aikin Gina Muhimmin Titin Yankunan Karkara A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Kasar Sin Ya Fara Aikin Gina Muhimmin Titin Yankunan Karkara A Babban Birnin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.