• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Naja’atu Mohammed: Mace Ta Farko Shugabar Kungiyar Daliban Jami’ar ABU

by Bello Hamza
3 years ago
in Rahotonni
0
Naja’atu Mohammed: Mace Ta Farko Shugabar Kungiyar Daliban Jami’ar ABU
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hajiiya Naja’atu Bala Mohammed, wadda aka fi kiranta da Hajia Naja musamman a tsakanin ‘yan gwagwarmaya da ‘yan siyasa a fadin tarayyar Nijeriya. Ta yi fice a fagen a fafutkar kare hakkin mata da al’umam gaba daya a fadin Nijeriya.

Ita ce kuma mace ta farko da ta lashe zaben kujerar majalisar dattawa mai wakiltar mazabar Kano ta tsakiya, haka kuma ita be mace ta farko da ta zama shugabar kungiyar daliban Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya a zangon karatu na shekarar 1982/83.

  • Tsare-tsaren CBN Don Samar Da Kyakkyawar Alkibla Ga Tattalin Arzikin Nijeriya
  • ‘Yan Bindiga Kamar Dabbobi Suke, Mun Samu Makamin Da Zai Datsa Su Biyu —Matawalle

An haifi Hajiya Naja’atu Bala Muhammad ne a shekarar 1956 a garin Kanon Dabo, mahaifinta Alhaji Ali Abdullahi, ciakknen dan Jami’yyar NEPU ne da ya yi zamani da Malam Aminu Kano.

Ta yi karatu a makarantar ‘St. Louis Pribate School’ Kano, ta kuma yi karatun koyon aikin malanta a ‘Women’s Teachers’ College’ kafin ta zarce zuwa Jami’ar Ahmadu Bello Zariya inda ta samu kammala karatu a fannin digiri a tarihi.

Naja’atu Bala Mohammed ta auri marigayi Dakta Bala Mohammed wanda shi ne mai ba Marigayi Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abubakar Rimi, shawara a kan bangaren harkokin siyasa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

A ranar 10 ga watan Yuli 1981 wasu gungun masu tarzoma suka kashe shi, kafin rasuwarsa mutum ne da ya yi Imani da akidun siyasar Jam’iyyar PRP na Marigayi Aminu Kano.

Naja’tu Bala Mohammed ta bayyana baiwa da Allah ya bata na shbugabanci tunlokacin da ta shiga harkar siysaa a jami’a ta kuma samu nasarar tafiyar da harkokin dalibai yadda ya kamata a wannan lokacin.

Tabbas ta kafa tarihi na zama shugabar kungiyar daliban jami’ar ABU ta kuma zama mataimakiyar shugabar kungiyar dalibai na kasa wato NANS.

Shighar Naja’atu Bala Mohammed harkokin siyaasa ya taimaka wajen zaburar da matan arewacin Nijeriya inda aka kai ga samun mata da ma sun shiga don a dama da su a harkar gudanar da mulkin al’umma.

Ta rike mukamai da dama da suka hada na shiga tsakani don sasanta rikicin ‘yan Boko Haram da gwamnatin tarayya, ba ta taba ganin aikinta cikin maza wani abu ne da zai hana bayar da nata gundummawar ba, tana daukar haka a matsayin sama ce na ta bayar da na gudumawar don daukaka kasarta Nijeriya, musamman abin da ya shafi tabbatar da zaman lafiya.

A wasu lokutta ta ki karbar wasu nadin da aka yi mata na mukamai, musanmman nadin da aka yi mata na zama ‘yar kwamitin gudanarwar Jam’iar Gwamnatin Tarayya da ke Dutse, inda ta ce ba a kai ga tuntubarta ba kafin a yi mata nadin. A halin yanzu ta karbi mukamin kwamishiniya a hukumar kula da aikin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ABUBuhariDalibaiKungiyaMaceNaja'atu MohammedNANS
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shekara 62 Da Samun ‘Yancin Kai: Na Damu Da Halin Da ‘Yan Nijeriya Ke Ciki – Buhari

Next Post

An Sake Yin Juyin Mulki A Burkina Faso Bayan Wata 8

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

4 weeks ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

1 month ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

1 month ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

1 month ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

1 month ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
An Sake Yin Juyin Mulki A Burkina Faso Bayan Wata 8

An Sake Yin Juyin Mulki A Burkina Faso Bayan Wata 8

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.