• English
  • Business News
Wednesday, June 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nathan Tella: Matashin Da Ke Fatan Buga Wa Nijeriya Wasa

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
Nathan Tella: Matashin Da Ke Fatan Buga Wa Nijeriya Wasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matashin dan wasa Nathan Tella ya ce burinsa zai cika yayin da yake shirin buga wa Nijeriya wasa a gasar neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta FIFA ta 2026 a wannan makon.

An sanya sunan dan wasan, mai shekara 24 da haihuwa, wanda ke wasa a kungiyar Bayer Leberkusen, cikin tawagar Super Eagles ta Nijeriya da za ta kara da Lesotho da kuma Zimbabwe.

  • CGTN Ya Gabatar Da Shiri Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • Ganawar San Francisco: Tsaraba Daga Jawabin Shugaba Xi Kan Bukatar Sin Da Amurka Su Nuna Su Manya Ne A Aikace

An haife shi a Lambeth, da ke kasar Ingila, amma ya cancanci buga wa Nijeriya ta dalilin iyayensa, makomarsa ta kasa da kasa ta kasance batu mai mahimmanci tun lokacin da ya fara yin tasiri a bangaren matasa a Arsenal.

Tella ya shaida wa manema labarai cewa, a kullum batunsa wakiltar Nijeriya ne saboda iyalinsa za su kasance cikin matukar farin ciki domin ganin ya cika wannan burin.

“Ina alfahari da asalina na dan Birtaniya da Nijeriya kuma na yi sa’a da samun al’adu biyu, tabbas mun hada al’adun bangarorin biyu, amma gidanmu cikkaken gidan ‘yan Nijeriya ne ta fannin abinci, da al’adu” in ji dan wasan.

Labarai Masu Nasaba

Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

Atalanta Na Neman Yuro Miliyan 50 Daga Duk Kungiyar Da Ke Son Daukar Lookman

Tella ya kasance daya daga cikin fitattun ‘yan wasan kungiyar Burnley a kakar wasan da ta gabata yayin da kungiyar ta samu gurbin komawa matakin gasar Firimiya, amma ya koma asalin kungiyarsa ta Southampton a karshen kakar wasan.

Dan wasan gaban, wanda zai iya buga wasa a gefe ko kuma ta tsakiya, ya bayar da gudunmawar kwallaye 22 a kakar wasan da ta gabata kuma ya koma Leberkusen a kan farashin fam miliyan 20 a watan Agusta.

Sabuwar kungiyarsa ba ta yi rashin nasara ba a gasar Bundesliga na Jamus bayan wasanni 10 kuma ana tunanin bajintarsa za ta kara wa tawagar Super Eagles karfi a bangaren ‘yan wasan gaba.

Bayan rashin halartar gasar cin kofin duniya da za a yi a Katar a shekarar 2022, ‘yan Afirkan ta Yamman sun fara yakin neman gurbin shiga gasar ta 2026 inda za su fafata da Lesotho da Zimbabwe a ranakun 16 da 19 ga watan Nuwamba.

Ana sa ran Nijeriya za ta tsallake daga rukunin C a saman takwarorinta na Afirka ta Kudu da Benin, inda kasashen da suka yi nasara a rukunin za su tabbatar da samun gurbi a gasar da za a yi a kasashen Canada da Medico da kuma Amurka bayan da aka kara yawan kasashe daga 32 zuwa 48.
Tawagar Nijeriya a wasannin watan Nuwamba da aka gayyata.

Masu tsaron raga: Francis Uzoho (Omonia Nicosia, Cyprus), Olorunleke Ojo
(Enyimba), Maduka Okoye (Udinese, Italy).

‘Yan wasan baya: Ola Aina (Nottingham Forest, England), Chidozie Awaziem
(Boabista, Portugal), Bright Osayi-Samuel (Fenerbahce, Turkey), Bruno Onyemaechi (Boabista, Portugal), Kenneth Omeruo (Kasimpasa, Turkey), Semi Ajayi (West Bromwich Albion, England), Calbin Bassey (Fulham, England), Jamilu Collins (Cardiff, Wales).

‘Yan wasan tsakiya: Raphael Onyedika (Club Bruges, Belgium), Joe Aribo
(Southampton, England), Frank Onyeka (Brentford, England), Aled Iwobi (Fulham, England).

‘Yan wsan gaba: Kelechi Iheanacho (Leicester City, England), Sadik Umar (Real Sociedad, Spain), Moses Simon (Nantes, France), Ademola Lookman (Atalanta, Italy), Nathan Tella (Bayer Leberkusen, Germany), Taiwo Awoniyi (Nottingham Forest, England), Terem Moffi (Nice, France), Bictor Boniface (Bayer Leberkusen, Germany).


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArsenalEvertonSuper Eagles
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilan Da Suka Sa Turawa Samun Nasarar Mulkin Mallaka A Arewa

Next Post

Halin Maza Muke Rubutawa, Ba Wai Sharri Muke Musu Ba – Amina Ma’aji

Related

Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba
Wasanni

Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

3 hours ago
Dan Nijeriya Lookman Na Kan Gaba Wajen Lashe Kyautar Gwarzon Kwallon Kafa Na Afrika Ta Bana
Wasanni

Atalanta Na Neman Yuro Miliyan 50 Daga Duk Kungiyar Da Ke Son Daukar Lookman

2 days ago
UEFA
Wasanni

‘Yan Wasa Biyar Da Suka Taka Rawar Gani A Kofin Zakarun Turai

4 days ago
Muhammad Salah: Gwarzon Afirka A Firimiyar Ingila
Wasanni

Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila

4 days ago
Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
Wasanni

Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

5 days ago
De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City
Wasanni

De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City

6 days ago
Next Post
Halin Maza Muke Rubutawa, Ba Wai Sharri Muke Musu Ba – Amina Ma’aji

Halin Maza Muke Rubutawa, Ba Wai Sharri Muke Musu Ba - Amina Ma'aji

LABARAI MASU NASABA

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

June 18, 2025
Kawayen amarya

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

June 18, 2025
Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

June 18, 2025
WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

June 18, 2025
Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

June 18, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

June 18, 2025
Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

June 18, 2025
Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

June 18, 2025
“Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki

“Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki

June 18, 2025
EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana

EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana

June 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.