• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nathan Tella: Matashin Da Ke Fatan Buga Wa Nijeriya Wasa

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
Nathan Tella: Matashin Da Ke Fatan Buga Wa Nijeriya Wasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matashin dan wasa Nathan Tella ya ce burinsa zai cika yayin da yake shirin buga wa Nijeriya wasa a gasar neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta FIFA ta 2026 a wannan makon.

An sanya sunan dan wasan, mai shekara 24 da haihuwa, wanda ke wasa a kungiyar Bayer Leberkusen, cikin tawagar Super Eagles ta Nijeriya da za ta kara da Lesotho da kuma Zimbabwe.

  • CGTN Ya Gabatar Da Shiri Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • Ganawar San Francisco: Tsaraba Daga Jawabin Shugaba Xi Kan Bukatar Sin Da Amurka Su Nuna Su Manya Ne A Aikace

An haife shi a Lambeth, da ke kasar Ingila, amma ya cancanci buga wa Nijeriya ta dalilin iyayensa, makomarsa ta kasa da kasa ta kasance batu mai mahimmanci tun lokacin da ya fara yin tasiri a bangaren matasa a Arsenal.

Tella ya shaida wa manema labarai cewa, a kullum batunsa wakiltar Nijeriya ne saboda iyalinsa za su kasance cikin matukar farin ciki domin ganin ya cika wannan burin.

“Ina alfahari da asalina na dan Birtaniya da Nijeriya kuma na yi sa’a da samun al’adu biyu, tabbas mun hada al’adun bangarorin biyu, amma gidanmu cikkaken gidan ‘yan Nijeriya ne ta fannin abinci, da al’adu” in ji dan wasan.

Labarai Masu Nasaba

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Tella ya kasance daya daga cikin fitattun ‘yan wasan kungiyar Burnley a kakar wasan da ta gabata yayin da kungiyar ta samu gurbin komawa matakin gasar Firimiya, amma ya koma asalin kungiyarsa ta Southampton a karshen kakar wasan.

Dan wasan gaban, wanda zai iya buga wasa a gefe ko kuma ta tsakiya, ya bayar da gudunmawar kwallaye 22 a kakar wasan da ta gabata kuma ya koma Leberkusen a kan farashin fam miliyan 20 a watan Agusta.

Sabuwar kungiyarsa ba ta yi rashin nasara ba a gasar Bundesliga na Jamus bayan wasanni 10 kuma ana tunanin bajintarsa za ta kara wa tawagar Super Eagles karfi a bangaren ‘yan wasan gaba.

Bayan rashin halartar gasar cin kofin duniya da za a yi a Katar a shekarar 2022, ‘yan Afirkan ta Yamman sun fara yakin neman gurbin shiga gasar ta 2026 inda za su fafata da Lesotho da Zimbabwe a ranakun 16 da 19 ga watan Nuwamba.

Ana sa ran Nijeriya za ta tsallake daga rukunin C a saman takwarorinta na Afirka ta Kudu da Benin, inda kasashen da suka yi nasara a rukunin za su tabbatar da samun gurbi a gasar da za a yi a kasashen Canada da Medico da kuma Amurka bayan da aka kara yawan kasashe daga 32 zuwa 48.
Tawagar Nijeriya a wasannin watan Nuwamba da aka gayyata.

Masu tsaron raga: Francis Uzoho (Omonia Nicosia, Cyprus), Olorunleke Ojo
(Enyimba), Maduka Okoye (Udinese, Italy).

‘Yan wasan baya: Ola Aina (Nottingham Forest, England), Chidozie Awaziem
(Boabista, Portugal), Bright Osayi-Samuel (Fenerbahce, Turkey), Bruno Onyemaechi (Boabista, Portugal), Kenneth Omeruo (Kasimpasa, Turkey), Semi Ajayi (West Bromwich Albion, England), Calbin Bassey (Fulham, England), Jamilu Collins (Cardiff, Wales).

‘Yan wasan tsakiya: Raphael Onyedika (Club Bruges, Belgium), Joe Aribo
(Southampton, England), Frank Onyeka (Brentford, England), Aled Iwobi (Fulham, England).

‘Yan wsan gaba: Kelechi Iheanacho (Leicester City, England), Sadik Umar (Real Sociedad, Spain), Moses Simon (Nantes, France), Ademola Lookman (Atalanta, Italy), Nathan Tella (Bayer Leberkusen, Germany), Taiwo Awoniyi (Nottingham Forest, England), Terem Moffi (Nice, France), Bictor Boniface (Bayer Leberkusen, Germany).


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArsenalEvertonSuper Eagles
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilan Da Suka Sa Turawa Samun Nasarar Mulkin Mallaka A Arewa

Next Post

Halin Maza Muke Rubutawa, Ba Wai Sharri Muke Musu Ba – Amina Ma’aji

Related

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica
Wasanni

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

1 day ago
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff
Wasanni

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

4 days ago
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana
Wasanni

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

5 days ago
Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa
Wasanni

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

5 days ago
Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?
Wasanni

Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

5 days ago
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack
Wasanni

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

1 week ago
Next Post
Halin Maza Muke Rubutawa, Ba Wai Sharri Muke Musu Ba – Amina Ma’aji

Halin Maza Muke Rubutawa, Ba Wai Sharri Muke Musu Ba - Amina Ma'aji

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Nathan Tella

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

September 19, 2025
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

September 19, 2025
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

September 19, 2025
Nathan Tella

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.