• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nathan Tella: Matashin Da Ke Fatan Buga Wa Nijeriya Wasa

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Nathan Tella

Matashin dan wasa Nathan Tella ya ce burinsa zai cika yayin da yake shirin buga wa Nijeriya wasa a gasar neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta FIFA ta 2026 a wannan makon.

An sanya sunan dan wasan, mai shekara 24 da haihuwa, wanda ke wasa a kungiyar Bayer Leberkusen, cikin tawagar Super Eagles ta Nijeriya da za ta kara da Lesotho da kuma Zimbabwe.

  • CGTN Ya Gabatar Da Shiri Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • Ganawar San Francisco: Tsaraba Daga Jawabin Shugaba Xi Kan Bukatar Sin Da Amurka Su Nuna Su Manya Ne A Aikace

An haife shi a Lambeth, da ke kasar Ingila, amma ya cancanci buga wa Nijeriya ta dalilin iyayensa, makomarsa ta kasa da kasa ta kasance batu mai mahimmanci tun lokacin da ya fara yin tasiri a bangaren matasa a Arsenal.

Tella ya shaida wa manema labarai cewa, a kullum batunsa wakiltar Nijeriya ne saboda iyalinsa za su kasance cikin matukar farin ciki domin ganin ya cika wannan burin.

“Ina alfahari da asalina na dan Birtaniya da Nijeriya kuma na yi sa’a da samun al’adu biyu, tabbas mun hada al’adun bangarorin biyu, amma gidanmu cikkaken gidan ‘yan Nijeriya ne ta fannin abinci, da al’adu” in ji dan wasan.

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

Tella ya kasance daya daga cikin fitattun ‘yan wasan kungiyar Burnley a kakar wasan da ta gabata yayin da kungiyar ta samu gurbin komawa matakin gasar Firimiya, amma ya koma asalin kungiyarsa ta Southampton a karshen kakar wasan.

Dan wasan gaban, wanda zai iya buga wasa a gefe ko kuma ta tsakiya, ya bayar da gudunmawar kwallaye 22 a kakar wasan da ta gabata kuma ya koma Leberkusen a kan farashin fam miliyan 20 a watan Agusta.

Sabuwar kungiyarsa ba ta yi rashin nasara ba a gasar Bundesliga na Jamus bayan wasanni 10 kuma ana tunanin bajintarsa za ta kara wa tawagar Super Eagles karfi a bangaren ‘yan wasan gaba.

Bayan rashin halartar gasar cin kofin duniya da za a yi a Katar a shekarar 2022, ‘yan Afirkan ta Yamman sun fara yakin neman gurbin shiga gasar ta 2026 inda za su fafata da Lesotho da Zimbabwe a ranakun 16 da 19 ga watan Nuwamba.

Ana sa ran Nijeriya za ta tsallake daga rukunin C a saman takwarorinta na Afirka ta Kudu da Benin, inda kasashen da suka yi nasara a rukunin za su tabbatar da samun gurbi a gasar da za a yi a kasashen Canada da Medico da kuma Amurka bayan da aka kara yawan kasashe daga 32 zuwa 48.
Tawagar Nijeriya a wasannin watan Nuwamba da aka gayyata.

Masu tsaron raga: Francis Uzoho (Omonia Nicosia, Cyprus), Olorunleke Ojo
(Enyimba), Maduka Okoye (Udinese, Italy).

‘Yan wasan baya: Ola Aina (Nottingham Forest, England), Chidozie Awaziem
(Boabista, Portugal), Bright Osayi-Samuel (Fenerbahce, Turkey), Bruno Onyemaechi (Boabista, Portugal), Kenneth Omeruo (Kasimpasa, Turkey), Semi Ajayi (West Bromwich Albion, England), Calbin Bassey (Fulham, England), Jamilu Collins (Cardiff, Wales).

‘Yan wasan tsakiya: Raphael Onyedika (Club Bruges, Belgium), Joe Aribo
(Southampton, England), Frank Onyeka (Brentford, England), Aled Iwobi (Fulham, England).

‘Yan wsan gaba: Kelechi Iheanacho (Leicester City, England), Sadik Umar (Real Sociedad, Spain), Moses Simon (Nantes, France), Ademola Lookman (Atalanta, Italy), Nathan Tella (Bayer Leberkusen, Germany), Taiwo Awoniyi (Nottingham Forest, England), Terem Moffi (Nice, France), Bictor Boniface (Bayer Leberkusen, Germany).

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 
Wasanni

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

October 15, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo
Wasanni

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025
NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3
Wasanni

NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

October 13, 2025
Next Post
Halin Maza Muke Rubutawa, Ba Wai Sharri Muke Musu Ba – Amina Ma’aji

Halin Maza Muke Rubutawa, Ba Wai Sharri Muke Musu Ba - Amina Ma'aji

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

October 16, 2025
Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025
Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025
Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

October 16, 2025
Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

October 16, 2025
An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.