• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nathan Tella: Matashin Da Ke Fatan Buga Wa Nijeriya Wasa

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Wasanni
0
Nathan Tella: Matashin Da Ke Fatan Buga Wa Nijeriya Wasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matashin dan wasa Nathan Tella ya ce burinsa zai cika yayin da yake shirin buga wa Nijeriya wasa a gasar neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta FIFA ta 2026 a wannan makon.

An sanya sunan dan wasan, mai shekara 24 da haihuwa, wanda ke wasa a kungiyar Bayer Leberkusen, cikin tawagar Super Eagles ta Nijeriya da za ta kara da Lesotho da kuma Zimbabwe.

  • CGTN Ya Gabatar Da Shiri Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • Ganawar San Francisco: Tsaraba Daga Jawabin Shugaba Xi Kan Bukatar Sin Da Amurka Su Nuna Su Manya Ne A Aikace

An haife shi a Lambeth, da ke kasar Ingila, amma ya cancanci buga wa Nijeriya ta dalilin iyayensa, makomarsa ta kasa da kasa ta kasance batu mai mahimmanci tun lokacin da ya fara yin tasiri a bangaren matasa a Arsenal.

Tella ya shaida wa manema labarai cewa, a kullum batunsa wakiltar Nijeriya ne saboda iyalinsa za su kasance cikin matukar farin ciki domin ganin ya cika wannan burin.

“Ina alfahari da asalina na dan Birtaniya da Nijeriya kuma na yi sa’a da samun al’adu biyu, tabbas mun hada al’adun bangarorin biyu, amma gidanmu cikkaken gidan ‘yan Nijeriya ne ta fannin abinci, da al’adu” in ji dan wasan.

Labarai Masu Nasaba

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Tella ya kasance daya daga cikin fitattun ‘yan wasan kungiyar Burnley a kakar wasan da ta gabata yayin da kungiyar ta samu gurbin komawa matakin gasar Firimiya, amma ya koma asalin kungiyarsa ta Southampton a karshen kakar wasan.

Dan wasan gaban, wanda zai iya buga wasa a gefe ko kuma ta tsakiya, ya bayar da gudunmawar kwallaye 22 a kakar wasan da ta gabata kuma ya koma Leberkusen a kan farashin fam miliyan 20 a watan Agusta.

Sabuwar kungiyarsa ba ta yi rashin nasara ba a gasar Bundesliga na Jamus bayan wasanni 10 kuma ana tunanin bajintarsa za ta kara wa tawagar Super Eagles karfi a bangaren ‘yan wasan gaba.

Bayan rashin halartar gasar cin kofin duniya da za a yi a Katar a shekarar 2022, ‘yan Afirkan ta Yamman sun fara yakin neman gurbin shiga gasar ta 2026 inda za su fafata da Lesotho da Zimbabwe a ranakun 16 da 19 ga watan Nuwamba.

Ana sa ran Nijeriya za ta tsallake daga rukunin C a saman takwarorinta na Afirka ta Kudu da Benin, inda kasashen da suka yi nasara a rukunin za su tabbatar da samun gurbi a gasar da za a yi a kasashen Canada da Medico da kuma Amurka bayan da aka kara yawan kasashe daga 32 zuwa 48.
Tawagar Nijeriya a wasannin watan Nuwamba da aka gayyata.

Masu tsaron raga: Francis Uzoho (Omonia Nicosia, Cyprus), Olorunleke Ojo
(Enyimba), Maduka Okoye (Udinese, Italy).

‘Yan wasan baya: Ola Aina (Nottingham Forest, England), Chidozie Awaziem
(Boabista, Portugal), Bright Osayi-Samuel (Fenerbahce, Turkey), Bruno Onyemaechi (Boabista, Portugal), Kenneth Omeruo (Kasimpasa, Turkey), Semi Ajayi (West Bromwich Albion, England), Calbin Bassey (Fulham, England), Jamilu Collins (Cardiff, Wales).

‘Yan wasan tsakiya: Raphael Onyedika (Club Bruges, Belgium), Joe Aribo
(Southampton, England), Frank Onyeka (Brentford, England), Aled Iwobi (Fulham, England).

‘Yan wsan gaba: Kelechi Iheanacho (Leicester City, England), Sadik Umar (Real Sociedad, Spain), Moses Simon (Nantes, France), Ademola Lookman (Atalanta, Italy), Nathan Tella (Bayer Leberkusen, Germany), Taiwo Awoniyi (Nottingham Forest, England), Terem Moffi (Nice, France), Bictor Boniface (Bayer Leberkusen, Germany).


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArsenalEvertonSuper Eagles
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilan Da Suka Sa Turawa Samun Nasarar Mulkin Mallaka A Arewa

Next Post

Halin Maza Muke Rubutawa, Ba Wai Sharri Muke Musu Ba – Amina Ma’aji

Related

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau
Wasanni

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

4 days ago
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 
Wasanni

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

4 days ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

6 days ago
Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro
Wasanni

Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

7 days ago
PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 
Wasanni

PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 

1 week ago
UEFA: Inter Milan Ta Yi Wa Barcelona Kancal
Wasanni

UEFA: An Kai Ruwa Rana Yayin Da Inter Ta Koro Barcelona Gida

1 week ago
Next Post
Halin Maza Muke Rubutawa, Ba Wai Sharri Muke Musu Ba – Amina Ma’aji

Halin Maza Muke Rubutawa, Ba Wai Sharri Muke Musu Ba - Amina Ma'aji

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.