• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nazari Kan Gazawar Tsofaffin Ministocin Noma 52 Da Suka Shude A Nijeriya

by Abubakar Abba and Sulaiman
8 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Nazari Kan Gazawar Tsofaffin Ministocin Noma 52 Da Suka Shude A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daga shekarar 1966 zuwa 2020, Nijeriya ta yi Ministocin Aikin Gona daidai har guda 52.

 

Sai dai, abin takaicin shi ne; bayan tsawon shekara 54, ba a samu wata gagarumar nasara ta a zo a gani ko wani sauyi ga wannan fanni na aikin noman a fadin wannan kasa ba.

  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Rage Kudin Sufuri Da Kashi 40 Ta Hanyar Amfani Da Motoci Masu Iskar Gas
  • Ranar ‘Yanci: Jihar Kano Ta Zama Madubin Dubawa A Kan Kyakkyawan Shugabanci – Gwamna Abba

Har zuwa yanzu, wasu manoma a kasar nan; na ci gaba da amfani da Fatanya da sauran kayan noma na gargajiya.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

Haka zalika, har zuwa yau; wasu manoma a wannan kasa na amfani da Galmar Shanu wajen yin noma, musamman a Arewacin Nijeriya; inda kuma wasu gonaki ‘yan kalilan na masu zuba hannun jari, na masu noma daga ketare; ke amfani da kayan aikin noma na zamani.

 

Wasu daga cikin fitattun tsoffin Ministocin Ma’aikatar Gona na wannan kasar, wadanda suka hada da Cif C.O. Komolafe, Otunba Bamidele Dada, Adamu waziri, Dakta Joe Okezie, Malam Adamu Ciroma, Cif Ola Awotesu, Farfesa Jerry Gana, Madam Ada Adogu, Marigayi Alhaji Abubakar H. Hashidu, Cif Chris Agbobu, Dakta Shettima Mustafa, Dakta Grace Ogwuche da kuma Dakta Malami Buwai.

 

Sauran su ne, Dakta Garba J.A Abdulkadir, Dakta Hassan Adamu. Alhaji Sani Zangon Daura, Dakta Sayyadi Abba Ruwa, Alhaji Dakta Fidellia Njeze, Isa Muhammed, Alhaji Bala Sakkwato, Alhaji Adamu Bello, Dakta Akinwumi Adesina, Cif Audu Ogbeh, Alhaji Sabo Nanono da kuma Mohammad Mahmood Abubakar Tanko.

 

Sai dai, wasu daga cikin wadannan tsoffin ministocin; kamar Jerry Gana da wasu daga cikinsu, ba su shekara guda a kan mukamin ba.

 

Tsohon Ministan Ma’aikatar, Alhaji Adamu Bello; shi ne wanda ya jima yana rike da mukamanin ministan ma’aikatar, inda ya shafe shekaru shida; a lokacin mulkin tsohon shugaban kasa, Cif Olusegun Obasanjo.

 

Duk da irin wadannan jiga-jigan manyan mutane da suka shugabancin ma’aikatar ta noma, fannin ya samu koma-baya.

 

Har ila yau, fannin ya samu koma bayan ne; sakamakon irin rikon sakainar kashin da mafi akasarin shugabannin da suka rike madafun iko na kasar, suka yi watsi da kyawawan shiriye-shirye da tsare-tsaren da tsaffin ministocin su ma suka samar a lokacin da suka shugabanci ma’aikatar, inda suke kawo nasu tsare-tsaren da kuma shiye-shiyen da suke bukata.

 

Misali, shirin inganta noman Rogo; wanda Adamu Bello ya kirkiro a lokacin da ya shugabanci ma’aiktar, wanda kuma bayan nada Dakta Adesina a matsayin ministan ma’aikatar, ya kara karfafa shirin.

 

Sai dai abin takaic, shirin bai kai labari ba; wanda kuma Naira biliyan 10 da aka zuba domin renon gonakin noman na Rogon, ba a iya warware takaddamar kudin da aka ware wa aikin ba.

 

Haka zalika, Adesina ya kirkiro da wani tsari na tura wa manoma kudin tallafin aikin noma kai tsaye zuwa asusun ajiyarsu na bankuna, musamman domin kawar da ayyukan ‘yan-na-kama.

 

Sai dai abin takaici, a lokacin da Cif Audu Ogbeh ya karbi ragamar ma’aikatar, ya yi watsi da wannan tsari na Adesina, musamman saboda dimbin bashin kimanin Naira biliyan 76 da aka gada daga wurin tsohuwar gwamnatin tsohon shugaban kasa, Gooluck Jonathan.

 

Kwararru da dama a fannin aikin noma na kasar nan, sun yi amanna da cewa, daukacin wadannan tsoffin ministoci 54, babu wani kokari da suka yi na kara ciyar da fannin gaba; duba da yadda kasashe kamar Indiya, Pakistan da Brazil suka yi wa Nijeriya fintinkau a fannin farfado da aikin noma.

 

Wasu daga cikin kwararru kamar Dakta Aliyu Sumaila, ya bayyana dalilan da suka sanya aka gaza samar da sauyi a wannan fanni na noma, wadanda suka hada da yin noma da kayan aiki na gargajiya; wanda hakan yasa ba a samun girbin amfani mai yawa da rashin yin amfani da kayan noma na zamani, wanda hakan ke jawo wa manoma yin asara a girbin farko na amfanin gonakinsu.

 

Shi kuwa, Farfesa Banji Oyelaran-Oyeyinka, mai bai wa Shugaban Bankin Raya Nahiyar Afirka (AfDB) shawara ya bayyana cewa, kasar ta gaza samar da sauyi a fannin aikin noman ne sakamakon yadda ‘yan siyasa suka yi watsi da shiye-shiyen da aka kirkiro na habaka fannin, saboda son zuciyarsu.

 

A cewar tasa, kasashe kamar Indiya Fakistan, Birazil da kuma Bietnam; wadanda suka kasance cikin sahu na gaba a kan Nijeriya a fannin noma, sun samu ci gaba wajen samar da sauyi a fannin nasu.

 

Banji ya ci gaba da cewa, akwai babbar tazara tsakanin Nijeriya da Kasar Birazil wajen girbe amfanin gona, inda ya bayyana cewa; idan har Nijeriya na son cike wannan gibi, ya zama wajbi ta rungumi noma da kayan aiki na zamani tare kuma da samar da ingantaccen Irin noma da kuma kara bunkasa noman rani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ma'aikatar NomaTsadar kayan abinci
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Na Binciken Sufeto Bisa Zargin Daba Wa Wani Mutum Wuka A Kan Naira 200

Next Post

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

Related

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

5 days ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

5 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

5 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

2 weeks ago
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

3 weeks ago
Next Post
Nijeriya

Ra'ayoyin 'Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun 'Yancin Kai

LABARAI MASU NASABA

Hukumar kashe gobara

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

June 5, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

June 5, 2025
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

June 5, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

June 5, 2025
Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

June 5, 2025
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

June 5, 2025
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

June 5, 2025
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

June 5, 2025
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

June 5, 2025
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.