ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar ‘Yanci: Jihar Kano Ta Zama Madubin Dubawa A Kan Kyakkyawan Shugabanci – Gwamna Abba

by Idris Aliyu Daudawa and Sulaiman
2 years ago
Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta shirya taron kara wa juna sani a wani bangare na bukukuwan cikar Nijeriya shekara 64 da samun ‘yancin kai.

 

Taron wanda ya mayar da hankali kan irin ci gaban da aka samu da kalubalen da ke addabar kasar nan, ya gudana ne a dakin taro na fadar Gwamnatin Kano.

ADVERTISEMENT
  • Kirkirar Kimiyya Da Fasaha Ta Kasar Sin Na Sa Kaimi Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya
  • Muhimman Abubuwa 10 Da Jawabin Tinubu Na Ranar ‘Yancin Kai Ya Kunsa 

Da yake jawabi a wurin taron, Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf ya tabo batutuwa masu motsa zuciya, inda ya bayyana cewa bisa sake fasalin shugabanci da tabbatar da rikon amana, Jihar Kano ta zama madubi ga jihohi da kuma fagen ci gaban siyasar kasar nan.

 

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Gwamna Abba bayan jinjina wa kokarin kwamitin da ya tsara wannan taro, wanda ya ce ya yi kyakkyanwan hange da tunanin zakulo masu gabatar da jawabai wadanda suka kasance mutane masu kima da daraja, ya yi karin haske kan kyakkyawan salon shugabancin gwamnatinsa.

 

Ya ce gwamnatin ta mayar da hankali sosai kan wasu muhimman ayyuka da suke da alaka da kyautata rayuwar al’ummar Jihar Kano kai-tsaye.

 

“Zan yi amfani da wannan dama domin bayyana wasu daga cikin manyan nasarorin da gwamnatin Kano ta samu a bangarori daban-daban, wannan kuma wani kokari ne na magance kalubalen da ya jima yana addabar rayuwar mazauna Kano.

 

“A bangaren ilimi, mun samu gagarumar nasarar sake farfado da sashin, hakan ya hada da ginawa tare da gyaran makarantu, daukar kwararrun malamai, samar da kayan koyo da koyarwa, haka kuma mun bujiro da tsarin ilmantarwa ta hanyar fasahar zamani da koyar da sana’o’i ga matasa.

 

“Sashin lafiya na cikin bangarorin da wannan gwamnati ke bai wa kulawa ta musamman, ta yadda aka daga darajar cibiyoyin kiwon lafiya, da kyautata tsarin kula da lafiyar mata masu ciki da kananan yara, kana an kuma yi duk mai yiwuwa wajen ganin ba a bar jama’ar karkara a baya ba. Sai kuma yadda muka tunkari kalubalen cututtuka kamar maleriya, karancin abinci mai gina jiki da sauran cututtukaka masu yaduwa.”

 

Har ila yau, Gwamna Abba ya nunar da cewa, sauran bangarorin da ke samun kyakkyawar kulawa a gwamnatinsa sun hada da sashin noma, tsaro, tallafa wa matasa da jari iri daban-daban, inganta tsarin aikin gwamnati da bayar da fifiko wajen biyan basussukan kudaden fansho da aka danne wa masu na tsawon lokaci.

 

Gwamnan ya kuma bayyana irin gagarumar nasarar da suka samu ta fuskar manyan ayyuka kamar kyautata muhalli, inganta harkar wasanni wadanda suka samar wa Jihar Kano gagarumin ci gaba.

 

Ya jaddada bukatar hadin kai a tsakanin al’ummar Jihar Kano domin kara samun nasarar da ake fata, yana mai cewar, “wannan kuma bai zai samu ba sai ta hanyar jajircewa, sadaukar da kai domin kare kimar al’ummarmu.” In ji shi.

Kano
Idris Aliyu Daudawa
+ posts Bio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)
Kano
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
  • Sulaiman
    An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • Sulaiman
    Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin
  • Sulaiman
    Shugaban Mongoliya Ya Zanta Da Ministan Wajen Kasar Sin

MASU ALAKA

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina
Labarai

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta
Tsaro

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai
Manyan Labarai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Next Post
Kaso 40 Na ‘Yan Nijeriya Na Samun Wutar Lantarki Fiye Da Awa 20 A Kowace Rana — Minista

Kaso 40 Na 'Yan Nijeriya Na Samun Wutar Lantarki Fiye Da Awa 20 A Kowace Rana — Minista

LABARAI MASU NASABA

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

June 15, 2026
An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.