• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nazari Kan Noman Citta A Zamanance

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Nazari Kan Noman Citta A Zamanance
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gabatarwa:

Ana sarrafa Citta zuwa wasu nau’ikan kayan lemon kwalba ko ganyen shayi da sauran makamantansu.

Kazalika, a daukacin fadin duniya; ana sarrafa Citta zuwa nau’ikan magungunan gargajiya, ana kuma sarrafa ta zuwa nau’ikan wasu magunguna na Bature, wanda mutane ke amfani da su don neman lafiya.

Har ila yau, ana sarrafa Citta  zuwa nau’ikan magungunan da ake bai wa dabbobi kamar Dokuna, Shanu, Rakuma da sauransu.

Tarihi ya nuna cewa, an fara yin noman Citta a Nijeriya tun a shekarar 1927, bayan gudanar da wani bincike; domin gano amfanin gonar da zai bai wa mazauna Kudauncin Kaduna damar yin kasuwancin cikin gida, musamman yankin na da albarkatun Citta.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Daga 1967 zuwa 1998 harkar noman Citta, ya ragu kwarai da gaske sakamakon wasu tsare-tsare da kuma yin watsi da fannin da gwamnati ta yi da kuma rashin samun kudaden shiga daga fannin, musamman biyo bayan samun danyen mai a kasar nan.

Bisa nazarin da wani masani mai suna Hokiet ya yi a 1992 da kuma nazarin da wani masanin Yohanna ya yi a 2007, sun nuna cewa; za a iya samun cin nasara a fannin aikin noma ta hanyar amfani da fasahar zamani na yin noman wannan Citta, wanda hakan zai taimaka wajen kara bunkasa fannin da kuma habaka tattalin arzikin kasa.

Matsayin Noman Citta A Nijeriya:

Nijeriya na da wadatacciyar kasar noman Citta, musamman kamar yadda hukumar abinci ta duniya (FAO) ta sanar.

Hukumar ta ce a 2009, kimanin kasahi 45.4 a cikin dari; kadada daya tak ta Cittar aka noma.

Kazalika, hukumar ta bayyana cewa, Cittar da aka girbe a Nijeriya a 2009 ta kai kimanin tan 3.4, wanda hakan ya nuna cewa, an samu raguwar a girbinta kwarai da gaske, idan aka kwatanta da yadda wasu sassan duniya suke a halin yanzu.

A kimiyyance, ana iya noman Cittat a kowane sashe na kasar nan, amma akasari an fi nomanta a Jihohin Kaduna, Nasarawa, Benuwe, Neja da kuma Gombe.

A halin yanzu, yankin Kudancin Kaduna ne ke samar da Citta sama da kashi 95  cikin dari.

Noman Citta A Zamanance:

Kayan aikin noma da suka hada da ingantacciyar kasar noma, gudanar da bincike, ilimin zamani, sadarwa, samar da bayanai, fasahar zamani da kuma taraktocin noma, na matukar bayar da gudunmawa wajen habaka noman Citta.

Rashin samar da wadannan kayan aiki kuwa, na karya wa manoma kwarin guiwa tare da gaza samar da wadataccen amfanin gona; kari a kan hakan kuma shi ne, zai iya haifar da talauci, musamman a tsakanin kananan manoma.

Sai dai, fannin noman Citta a Nijeriya, bai samu kulawar da ta dace ba, wanda hakan ya sanya akasari ana yin nomanta ba tare da yin amfani da kayan noma na zamani ba.

Har ila yau, manyan manoman Cittar su ne ke yin amfani da taraktar noma wajen gyaran gona da yin haro da sauran makamantansu.

Hatta kananan manoman da ke noma ta, wadanda su ne suka fi yawa, har yanzu suna yin nomanta ne a gargajiyance.

Kalubalen Da Ke Tattare Da Noman Citta:

Abubuwa da dama ne suka taru suka haifar wa da noman Citta kalubale, wadanda suka hada da rashin samar da kyakkyawan tsari daga wurin gwamnati, rashin kwarewa, nuna halin ko in kula; wanda hakan ke durkusar da masu son zuba jari wajen nomanta a zamanance.

Haka zalika, tsare-tsare da dama a gwamnati, sun janyo kalulabe a fannin wannan noma, wadanda suka hada da Rogo, Kwakwar Manja, Auduga da sauransu.

Sai dai, domin a kara habaka noman a zamanance, gwamnatin tarayya ta kirkiro da cibiya ta kasa mai kula da harkar noman nata a zamanance da ke a garin Ilorin, wato (NCAM) a 1975 zuwa 1980.

Duk da cewa, wannan cibiyar ta yi iya kokarinta, amma kananan manoman Citta ba sa iya samun kayan aiki na zamani.

Alfanun Da Ke Tattare Da Noman Citta:

Allah ya albarkaci Nijeriya da wadatacciyar kasar noma, wadda kuma za a iya yin noman Citta mai tarin yawa.

Kazalika, ta na da wadatattun albarkatu; wadanda da an yi amfani da su, za su samar da damar yin fasahar yin kasuwanci wajen yin noman wannan Citta.

Manoman Citta a Nijeriya, kansu a hade yake; sannan kuma suna kara samun fadakarwa, wanda idan aka ci gaba da fadakar da su tare da samar musu da tallafi da kudade, musamman wajen rungumar  yin nomanta a kamiyyance, ko shakka babu za su samu dimbin alfanu daga wannan fanni.

Sai dai, ta hanyar kirkiro da tsare-tsare masu kyau wanda gwamnati ta yi, hakan ya sa manomanta samun dauki na kudade ta hanyar bankin CBN.

Bugu da kari, a kwanakin baya; an sanya Citta a jerin amfanin gonar da za ta samu kulawa ta musamman daga shirin habaka fannin aikin noma na (ATA), wanda gwamnati mai ci ta kirkiro da shi.

Maiyiwuwa wannan yunkuri na gwamnati, ya taimaka wajen kara noman wannan Citta a kimiyance tare da nomanta, domin samun riba a wannan kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga: Gwamna Dauda Ya Kai Ziyarar Jaje A Zurmi Da Birnin Magaji

Next Post

Matakan Fara Kiwon Beran Masar

Related

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

4 hours ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

5 hours ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

1 week ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

1 week ago
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

2 weeks ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

2 weeks ago
Next Post
Matakan Fara Kiwon Beran Masar

Matakan Fara Kiwon Beran Masar

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.