ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nazari Kan Noman Citta A Zamanance

by Abubakar Abba
2 years ago
Citta

Gabatarwa:

Ana sarrafa Citta zuwa wasu nau’ikan kayan lemon kwalba ko ganyen shayi da sauran makamantansu.

Kazalika, a daukacin fadin duniya; ana sarrafa Citta zuwa nau’ikan magungunan gargajiya, ana kuma sarrafa ta zuwa nau’ikan wasu magunguna na Bature, wanda mutane ke amfani da su don neman lafiya.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, ana sarrafa Citta  zuwa nau’ikan magungunan da ake bai wa dabbobi kamar Dokuna, Shanu, Rakuma da sauransu.

Tarihi ya nuna cewa, an fara yin noman Citta a Nijeriya tun a shekarar 1927, bayan gudanar da wani bincike; domin gano amfanin gonar da zai bai wa mazauna Kudauncin Kaduna damar yin kasuwancin cikin gida, musamman yankin na da albarkatun Citta.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Daga 1967 zuwa 1998 harkar noman Citta, ya ragu kwarai da gaske sakamakon wasu tsare-tsare da kuma yin watsi da fannin da gwamnati ta yi da kuma rashin samun kudaden shiga daga fannin, musamman biyo bayan samun danyen mai a kasar nan.

Bisa nazarin da wani masani mai suna Hokiet ya yi a 1992 da kuma nazarin da wani masanin Yohanna ya yi a 2007, sun nuna cewa; za a iya samun cin nasara a fannin aikin noma ta hanyar amfani da fasahar zamani na yin noman wannan Citta, wanda hakan zai taimaka wajen kara bunkasa fannin da kuma habaka tattalin arzikin kasa.

Matsayin Noman Citta A Nijeriya:

Nijeriya na da wadatacciyar kasar noman Citta, musamman kamar yadda hukumar abinci ta duniya (FAO) ta sanar.

Hukumar ta ce a 2009, kimanin kasahi 45.4 a cikin dari; kadada daya tak ta Cittar aka noma.

Kazalika, hukumar ta bayyana cewa, Cittar da aka girbe a Nijeriya a 2009 ta kai kimanin tan 3.4, wanda hakan ya nuna cewa, an samu raguwar a girbinta kwarai da gaske, idan aka kwatanta da yadda wasu sassan duniya suke a halin yanzu.

A kimiyyance, ana iya noman Cittat a kowane sashe na kasar nan, amma akasari an fi nomanta a Jihohin Kaduna, Nasarawa, Benuwe, Neja da kuma Gombe.

A halin yanzu, yankin Kudancin Kaduna ne ke samar da Citta sama da kashi 95  cikin dari.

Noman Citta A Zamanance:

Kayan aikin noma da suka hada da ingantacciyar kasar noma, gudanar da bincike, ilimin zamani, sadarwa, samar da bayanai, fasahar zamani da kuma taraktocin noma, na matukar bayar da gudunmawa wajen habaka noman Citta.

Rashin samar da wadannan kayan aiki kuwa, na karya wa manoma kwarin guiwa tare da gaza samar da wadataccen amfanin gona; kari a kan hakan kuma shi ne, zai iya haifar da talauci, musamman a tsakanin kananan manoma.

Sai dai, fannin noman Citta a Nijeriya, bai samu kulawar da ta dace ba, wanda hakan ya sanya akasari ana yin nomanta ba tare da yin amfani da kayan noma na zamani ba.

Har ila yau, manyan manoman Cittar su ne ke yin amfani da taraktar noma wajen gyaran gona da yin haro da sauran makamantansu.

Hatta kananan manoman da ke noma ta, wadanda su ne suka fi yawa, har yanzu suna yin nomanta ne a gargajiyance.

Kalubalen Da Ke Tattare Da Noman Citta:

Abubuwa da dama ne suka taru suka haifar wa da noman Citta kalubale, wadanda suka hada da rashin samar da kyakkyawan tsari daga wurin gwamnati, rashin kwarewa, nuna halin ko in kula; wanda hakan ke durkusar da masu son zuba jari wajen nomanta a zamanance.

Haka zalika, tsare-tsare da dama a gwamnati, sun janyo kalulabe a fannin wannan noma, wadanda suka hada da Rogo, Kwakwar Manja, Auduga da sauransu.

Sai dai, domin a kara habaka noman a zamanance, gwamnatin tarayya ta kirkiro da cibiya ta kasa mai kula da harkar noman nata a zamanance da ke a garin Ilorin, wato (NCAM) a 1975 zuwa 1980.

Duk da cewa, wannan cibiyar ta yi iya kokarinta, amma kananan manoman Citta ba sa iya samun kayan aiki na zamani.

Alfanun Da Ke Tattare Da Noman Citta:

Allah ya albarkaci Nijeriya da wadatacciyar kasar noma, wadda kuma za a iya yin noman Citta mai tarin yawa.

Kazalika, ta na da wadatattun albarkatu; wadanda da an yi amfani da su, za su samar da damar yin fasahar yin kasuwanci wajen yin noman wannan Citta.

Manoman Citta a Nijeriya, kansu a hade yake; sannan kuma suna kara samun fadakarwa, wanda idan aka ci gaba da fadakar da su tare da samar musu da tallafi da kudade, musamman wajen rungumar  yin nomanta a kamiyyance, ko shakka babu za su samu dimbin alfanu daga wannan fanni.

Sai dai, ta hanyar kirkiro da tsare-tsare masu kyau wanda gwamnati ta yi, hakan ya sa manomanta samun dauki na kudade ta hanyar bankin CBN.

Bugu da kari, a kwanakin baya; an sanya Citta a jerin amfanin gonar da za ta samu kulawa ta musamman daga shirin habaka fannin aikin noma na (ATA), wanda gwamnati mai ci ta kirkiro da shi.

Maiyiwuwa wannan yunkuri na gwamnati, ya taimaka wajen kara noman wannan Citta a kimiyance tare da nomanta, domin samun riba a wannan kasa.

Citta
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Matakan Fara Kiwon Beran Masar

Matakan Fara Kiwon Beran Masar

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.